< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Isusu ăn Hram avizut p bogataši kum ubacăt banji ăn blagajnă alu hramuluj.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Atunča avizut š p njeka udovică kum arunkă samo duavă maj mič kovanic.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
Isusu azăs alu učenikulor: “Punjec urjajke, k istina je, asta sărakă udovică apus maj mult njego jej toc zajedno!
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
K toc jej adat ča vut viška, a ja, aša d sărakă, adat tot če arje.”
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Kănd njeki učenikurlje alu Isusuluj arubit kum je Hramu sagradit d maj măndru buluvan š ukrasăt ku maj măndri darurj karje lumja adat alu Dimizov, Isusu zăče:
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
“Osă vije vrijamja kănd nusă rămije nič unu buluvan p buluvan d Hramusta če vu ujtac. Tot s fije duburăt.”
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
Š daja jej la antribat: “Učiteljulje, kănd tot aja osă dogodjaštje? D karje znak osă najavljaskă d tot aja če vinje?”
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
Ja zăs Isusu: “Păzăcăvă s nu vu ănšalje! Mulc osă vije š osă zăkă: ‘Jo sănt Mesija’ š osă zăkă avinjit kraju! Nu lji kridjec.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Kănd audjec d raturj š d pobună, na vjec frikă. Tot aja mora s dogodjaskă, ali kraju alu pămăntuluj nusă vije još.”
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Zăče još: “Narodu osă zaratjaskă păntruv narod š cara păntruv cară.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
Osă fije marj potresurj. Osă fije fuamja š kuga p altje lokurj. Osă fije događajurj d karje lumja osă fije frikă š znakurj p čerj k vinje nješto rov.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
Ali majdată d aja če s fije, osă vu apukă š osă vu maltetirjaskă. Osă vu dja ăn sinagogă la sud š p voj osă trimjată ăn kisuarje. Osă vu dukă la intja alu carurj š la upraviteljurj daja če sljidic p minje.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
Osă vu zadisaskă p voj s putjec s rubic svjedočala avuastră d minje.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Nu vu brinic akuma če s zăčec d minje ăn obrană
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
k jo osă vu dav vorbilje š mudrost karje ničunu alu voštri protivnikurj nusă puată s odoljaskă nič s ăntuarkă vorba.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
Čak š roditelji, fracă, familija, š ortači osă vu predajaskă. Osă vu umuară p njeko d voj.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
Toc osă vu zamrzaskă daja če sljidic p minje.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Ali ničuna d ăštja stvarurj vuavă stvarno nu puatje s vu naštitjaskă.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
Osă dobidic život akă mije răminjec vjerni.”
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
“Kănd vidjec k vuastja opkoljaštje Jeruzalemu, osă štijic k avinjit vrijamja d uništijala alu Jeruzalem.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Ălja karje sa trefit ăn Judeja atunča s fugă ăn djal. Činje je ăn trg atunča s fugă dăn jel, a ălja karje s găsaštje ăn okolică atunča s nu untră ăn trg.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
K aja osă fije zăljilje alu Dimizovuluj d kaznjală ku karje osă ispunjaskă tot če skrije ăn Svăntă pismă d asta vrijamje.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Grjev alu trudnicilor š alu mujerj karje dă s sugă ăn vrijamjaja daja če osă vije marje rovu ăn pămăntusta š marje gnjev osă kadă p narodusta.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
Vuastja osă umuarje p njeka lumja š p alci osă lja dukă kašă p ratne zarobljenikurlje ăn tot pămăntu. Nežidovi osă gazaskă p Jeruzalemu pănă god nu triča vrijamja alor.”
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
“Osă pojavjaskă čudne znakurj p suarje, p lună š p stjalje. A p pămănt osă fije marje zbunjală, ka valurlje alu apăj ăntră marje oluje. Păntruv aja tot narodu osă fije mult zabrinic š ispunic ku frikă.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
Čak š stjaljilje p čerj osă skutirje. Lumja osă muarje d frikă š d marje užas karje osă vije p pămănt.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
Atunča tuată lumja osă vjadă p minje, Bijatu alu Omuluj, kum viuv p oblak ăn marje moć š ăn slavă.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Kănd aja tot ănčapje s dogodjaskă, avjec inimă š fic pljinj d nadă k Dimizov osă vu oslobodjaskă ăndată.”
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Atunča Isusu lja rubit asta vorbă: “Ujtacăvă la smokvă ili bilo d karje ljemn.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
Kănd vidjec pupu alu smokvăj atunča š săngurj štijec k je vara apruapje.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Isto aša kănd vidjec k vinje aja d čaja amrubit, atunča putjec s fic sigurni k je cara alu Dimizovuluj apruapje.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Istina je zăk vuavă, asta generacija nusă trjakă pănd tot asta nu s dogudja.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Čerju š pămăntu osă trjakă, ali vorba amja s rămăje zauvjek!”
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Isusu azăs: “Păzăcăvă š nu fic kašă lumja karje je tupavj d mamurluk š d bjarje ili briga alu životusta. Inače, aja zuvă ruavă p voj osă iznenadjaskă
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
kašă zamka. K osă vije p tuată lumje karje stanujaštje p pămănt.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Ăn tuată vrijamja păzăcăvă š rugacăvă s putjec s avjec snagă s izdržic aštja stvarurj če vinje š fic spremic s stăc la intja amja, la intja alu Bijatu alu Omuluj.”
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Isusu tuată zuvă ănvăca ăn Hram, š sara pljika š provodja nuaptja p djal Masline.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
A tot narodu s skula dănzorja š pljika ăn Hram s puje urjajke la Isusu.

< Luka 21 >