< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Jesu ha lola aba boni bafumi niba bika impo zabo mwi citanda.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
A ba boni mwanakazi yo fwililwe yo nyandite habika tuhafu twe pene.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
Chawamba, Zeniti nami bona, Uzu mwanakazi yo fwililwe wa zwisa kumihita.
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
Mubonse mwa zwisa impo zenu, Kono uzu mwanakazi ya sena chakwe wa mihita ka kuli waleta zonse zakakwete mubu njebwe bwakwe.
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Bamwi ba bali ku wamba Inkeleke mwiba kabisezwe ka bukwala ni mavwe ni mpo, cawamba.
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
Kwezo zintu zimubwene, inako mwikeze kakwina ivwe lyete nilishale kulimwi nilisawi”.
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
Chiba mubuza kuti muluti, Izo kazi tendahale lili? Hape chisupo chete chitondeze kuti kazi tendahale?
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
ce taba; mumamele, kanzi muchengwa. Bangi kabeze che zina lyangu, Nokucho kuti; Njime kreste, inako chiya chuta, kono kanji mubechilili.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Ha muzuwa inkondo ni kuli sandukila, Kanji mutiyi, Izo zintu kazi pangahali pili, kono kanji ma mani mani.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Chawamba kubali; Masika kalwise masika amwi; Mushobo ni mushobo kabalwe.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
Izikinyebo ikando mwi kanda iboneke, Nilufu lungi muzibaka zingi, Ni zala, Nizitiza, Ni zikomosa zikando zizwa kwe lreeza kwi wulu.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
Izi, ni ziseni kwiza, Bantu kaba milwise kamayaza, Bami sukulule niku mikwitila mu masinagoge, ni mwi tolongo, bami twale kuba simwine, niku ba atuli bezintu kebaka lyezina lyangu.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
Izo kazi mizile kuti muwambe buniti.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Aho muli lemuhele mwi inkulo zenu, kuti kanji mulitukisezi pili zete muli tabilile kazo.
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
Mukuti ime kanimihe mamzwi ni butali, kuti bami lwisa bakangwe kumi taba ni kumi kananisa.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
Kamu betekwa niku bazazi benu, niba kwaluzubo benu, niba likani benu, kabe haye bamwi kwenu.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
Imi kamu toiwe bantu bonse ibaka lyezina lyangu.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Imi ka kwina nanta lusuki lu mwina lwete nilu shale kumitwi yenu.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
Kamu haze ihuho zenu kaku kola kwenu.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
Chimwa bona Jerusalema izimbukitwe masole mwizibe kuti kuza kunuka kwayo chiku chunine.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
linu, bena kwa Judea batilile ku malundu; Bena mu munzi bazwe mo'imi bena mwi kanda kanji bazwimo, ku bolela ku munzi.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
Mukuti inako yaku bozekeza bantu bubi bwabo, kuti ziñoletwe zi boneke zose.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Bukabo kabwizile banakazi ba lihindite niba nyosa mwao mazuba; ka kuti bukabo bukando ka bube kwa nteni mwi kanda; imi bukali kabu sukile abo bantu.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
Mubawe kabu kali bwe sumo, kaba hapwe batwalwe kubantu bonse, imi jelusalema ka lyatolwe kube kanda mane ba maninine.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
Zisupo kazi boneke hezuba ni mwezi ni nkani; imi mwi kanda mahasi kahwilwe niku njanja kebaka lya mawate ni masunda.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
Bantu kaba zumininine kebaka lyo kutiya niku lindila zete zize mwi kanda; ka kuti zina ziho zo kwi wulu muzi nyanganye.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
Imi kaba bone Mwana wo Muntu heti chokeza mu makope ke ziho ni kanya ikando.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Izo chizatanga kwiza; mu loleze menso kwi wulu, Imi muinuke; ka kuli kulukululwa kwenu chi kwina hafwihi.
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Cha ba wambila inguli, Chati' mubone i samu lye feiga ni zisamu zimwi.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
Hali tumpa makoba, Imi mwi ziba ni kulemuha kuti imbumbi chiina hafuhi.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Ka mukwa wina bulyo, ne nwe, hamu bona izo chizi keza, mwina no kwi ziba kuti mubuso we Ireeza chi wina hafuhi.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Kabuniti ni wamba kwenu, ulu luzubo kete lumane, zonse zi seni ku tendahala.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Iwulu kali mane ni kanda bulyo; mi manzwi angu kete ni a mane.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Imi mu mamele inkulo zenu kanji zi lyanganiswa kulya kwenu, niku kolwa mutoho, niku bilela zo buhalo.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
mane ilyo izuba kali miwane kamu litukise; MU kuti kachiwile bonse bazakite mwi kanda yonse.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Mi he, mutonde mulapele inako yonse, ili kuti mukole ni kubanduka kwezo zonse zete nizi boneke, ni kwa kwe habusu bwa Mwana Muntu.
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Jesu abali kulutanga musihali mwi nkeleke imi masiku aba kuzwanga niku ka lindila hachi wulu chisumpwa ze samu lya olive.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
Imi chichaba chonse chibali kwiza kakusasani mwi nkeleke kuku mutekeleza.

< Luka 21 >