< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Jesus looked up and saw the rich men who were putting their gifts into the treasury.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
He saw a certain poor widow putting in two mites.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
So he said, “Truly I say to you, this poor widow put in more than all of them.
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
All of these gave gifts out of their abundance. But this widow, out of her poverty, put in all she had to live on.”
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
As some spoke of the temple, how it was decorated with beautiful stones and offerings, he said,
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
“As for these things that you see, the days will come when not one stone will be left on another which will not be torn down.”
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
So they asked him, saying, “Teacher, when will these things happen? What will be the sign when these things are about to happen?”
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
Jesus answered, “Be careful that you are not deceived. For many will come in my name, saying, 'I am he,' and, 'The time is near.' Do not go after them.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
When you hear of wars and riots, do not be terrified, for these things must happen first, but the end will not happen immediately.”
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Then he said to them, “Nation will rise against nation, and kingdom against kingdom.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
There will be great earthquakes, and in various places famines and plagues. There will be terrifying events and great signs from heaven.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
But before all of these things, they will lay their hands on you and will persecute you, delivering you over to the synagogues and prisons, bringing you before kings and governors because of my name.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
It will lead to an opportunity for your testimony.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Therefore resolve in your hearts not to prepare your defense ahead of time,
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
for I will give you words and wisdom that all your adversaries will not be able to resist or contradict.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
But you will be delivered up also by parents, brothers, relatives, and friends, and they will put some of you to death.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
You will be hated by everyone because of my name.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
But not a hair of your head will perish.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
In your endurance you will gain your souls.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
When you see Jerusalem surrounded by armies, then know that its destruction is near.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Then let those in Judea flee to the mountains, let those who are in the city leave it, and those who are out in the country must not enter the city.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
For these are days of vengeance, so that all the things that are written will be fulfilled.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Woe to them who are pregnant and to them who are nursing in those days! For there will be great distress upon the land, and wrath to this people.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
They will fall by the edge of the sword, and they will be led captive into all the nations, and Jerusalem will be trampled by the Gentiles until the times of the Gentiles are fulfilled.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
There will be signs in the sun, in the moon, and in the stars, and on the earth. The nations will be in distress, anxious because of the roar of the sea and waves.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
There will be men fainting from fear and from expectation of the things which are coming upon the world. For the powers of the heavens will be shaken.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
Then they will see the Son of Man coming in a cloud with power and great glory.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
But when these things begin to happen, stand up and lift up your heads, because your deliverance is coming near.”
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Jesus told them a parable, “Look at the fig tree, and all the trees.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
When they sprout buds, you see for yourselves and know that summer is already near.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
So also, when you see these things happening, you know that the kingdom of God is near.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Truly I say to you, this generation will not pass away until all these things take place.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Heaven and earth will pass away, but my words will never pass away.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
But pay attention to yourselves, so that your hearts are not burdened with the effects of drinking and intoxication, and the worries of life, and then that day will close on you suddenly like a trap.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
For it will come upon everyone living on the face of the whole earth.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
But be alert at all times, praying that you may be strong enough to escape all these things that will take place, and to stand before the Son of Man.”
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
So during the days he was teaching in the temple, and at night he went out and stayed on the Mount of Olives.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
All of the people came early in the morning to hear him in the temple.

< Luka 21 >