< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Looking around, Jesus watched rich people putting their gifts into the collection box.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
He also saw a very poor widow put in two small coins.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
“I tell you the truth,” he said, “this poor widow has put in more than all the rest together.
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
All of them gave from their wealth what they had, but she gave from her poverty all she had to live on.”
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Some of those there were talking about the Temple, its fine stonework and the beautiful gifts that had been donated. But Jesus said,
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
“Regarding these things you're looking at… The time is coming when not one stone will be left on another; everything will be destroyed!”
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
“Teacher, when will this happen?” they asked him. “What will be the sign that these things are about to happen?”
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
“Make sure you're not deceived,” Jesus warned them. “Many people will come claiming to be me, saying, ‘Here I am!’ and, ‘The time has come!’ but don't follow them.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
When you hear of wars and revolutions, don't be frightened, because these things have to happen first, but the end won't come immediately.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Nation will fight nation, and kingdom will fight kingdom,” he told them.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
“There will be severe earthquakes, famines, and epidemic diseases in many lands, and extraordinary signs in the sky that are terrifying.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
But before all this, they will seize you and persecute you. They will drag you before synagogues and throw you into prison, and put you on trial before kings and governors on account of me.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
But this will provide you an opportunity to speak on my behalf before them.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
So make up your mind beforehand not to worry about how to defend yourselves,
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
for I will give you words of wisdom that your enemies won't be able to dispute or contradict.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
You will be betrayed even by your parents, brothers, relatives, and friends, and they will kill some of you.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
Everyone will hate you because of me.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
But not a single hair of your head will be lost.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
By standing firm you will gain your lives.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
However, when you see Jerusalem surrounded by armies, then you know that its destruction is near.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Those who are in Judea should run away to the mountains, and those who are in Jerusalem should leave, and those who are the countryside shouldn't enter the city.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
For these are days of punishment, fulfilling all that's written.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
How hard it will be for those who are pregnant or nursing babies at that time! For terrible trouble is coming on the land and punishment against this people.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
They will be killed by the sword and taken away as prisoners to all the nations. Jerusalem will be trodden down by the foreign nations until their time is fulfilled.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
There will be signs in the sun, moon, and stars, and on the earth the nations will be in distress, confused by the sea's rolling and crashing.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
People will be faint from fear, terrified about what is happening to the world, for the powers of heaven will be shaken.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
Then they'll see the Son of man coming in a cloud with power and great glory.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
But when these things happen, stand up and look up, because you will soon be saved.”
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Then he told them this story as an illustration. “Look at the fig tree, or any other kind of tree.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
When you see new leaves appear, you don't need to be told that summer is near.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
In the same way, when you see these things happening, you don't need to be told that God's kingdom is near.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
I tell you the truth, this generation won't come to an end before all this happens.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Heaven and earth will come to an end, but my word will not.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Watch out that you don't become distracted by partying or getting drunk or by the worries of this life, so that this day catches you by surprise.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
For this day will come upon everyone who lives on the face of the earth.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Always keep watch and pray, so that you may be able to escape all that will happen and stand before the Son of man.”
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Every day Jesus taught in the Temple, and every evening he went and stayed on the Mount of Olives.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
All the people came early in the morning to listen to him in the Temple.

< Luka 21 >