< Luka 21 >
1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Jesuh naw mang hü lü, bawimangki he naw, Temple khawh petnak üng ami khawh pe u se a jah hmuh.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Acunüng, m'yenksekia hmeinu mat pi, tangka ca nghngih pe law hnga se hmu lü,
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
“Akcanga ka ning jah mthehki, hin hea kthaka pi, acuna m'yenkse hmeinu naw a pet däm bawk ve;
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
“Hin he naw ami taka kpawih pe lawki he; cunsepi, hina hmeinu naw a xünnak vaia a tak naküt pe ve,” a ti.
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Acunüng, axüisaw he avang naw, Temple lunga kyäpa mawng, a dawa mawng la Pamhnam ami petmsawta mawng pyen u se,
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
Jesuh naw, “Hin atuh nami jah hmuh, hin üng lung matca pi am ve se, avan a kpyehnaka kcün pha law khai,” a ti.
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
Amimi naw, “Saja aw, acun cun itia kya law khai? Acun a pha law hlü üng msingnak i ve law khai?” tia, ami kthäh.
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
Jesuh naw, “Ä ami ning jah hleihlaknak vaia a na cäiei ua. Khyang khawjah naw, ‘Kei Khritaw ni,’ ‘Akcün pha law hlü ve,’ ti u lü, keia ngming pyen u lü, ngdang law khai he; acun he ä nami jah läk vai.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Acunüng, ngtungahnak la nghnengnaka ngthu nami ngjak üng, ä nami kyüh vai. Acun he akcüka ve law khai he, cunsepi acuna phäha adütnak ng'et lawkia am kya pha naw.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
“Pung la pung ngtu law khai he, khawe la khawe ngtu law khai he;
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
“Mkhyü aknuia ngsün law khai, pung avana khawjaw law khai, mnehmnang da law khai, khankhawa am hmuh khawia msingnak he aktäkpaia ngdang law khai he.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
“Acun he avan am a pha law hlan üng, ka ngminga phäha, ning jah man u lü, ning jah mkhuimkha u lü, Sinakok la thawngima ning jah cehpüi khai he. Sangpuxang he la khawbawi hea veia ning jah cehpüi khai he.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
“Cunsepi, acun cun thangkdaw nami pyenak vaia kcün kdawa kya khai.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
“Akcün am a pha law hlan üng ikba nami pyen be vaia ä cäi ua.
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
“Nami ye he naw, am ami ning jah nängnak vaia, khyaihnaka ngthu la ksingnak kei naw ka ning jah pe khai.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
“Nami nu la nami pa he, nami hnunpüi he, nami püi he naw pi ning jah ceng u lü ning jah man law sak khai he; avang ning jah hnim khai he.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
“Keia ngminga phäha khyang avan naw ning jah hneng law khai he.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
“Cunsepi, nami lusam matca pi am khyük khai ni.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
“Nami khängceknak am nami ngküikyanei kyu khai.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
“Acunüng, yekap he naw Jerusalem nglung law na u se nami hmuh üng, Jerusalem pyeh law hlüki ti nami ksing vai.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
“Judah khawa awmki he mcung hea dawng u se; mlüh k’uma awmki he kpunga dawng u se; mlüh kpunga awmki he mlüh k’uma ä lut be u se.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
“Acuna mhmüp cun, cangcim üng ng’yuki akümnak vaia, Mkhuimkhanaka Mhmüpa kya khai.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
“Acuna mhmüp üng m'yaieiki he la naca kpawmeiki he ta ami jo se ve; hina mdeka khana khuikhanak cang pha law khai, hina khyang hea khana Mhnama mkhuimkhanak pha law khaia kyaki.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
“Avang he Mthikcim am jah hnim khai he, avang he pung kcea jah cehpüi u lü thawngim üng jah khyum khai he; khyangmjükce hea mhmüp am a küm hlana küt üng, Jerusalem cun khyangmjükce hea khaw keha ve khai.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
“Nghngi, khya la aisi hea khana msingnak he ngdang law khai he; mliktui nghmüm law lü phu law se khawmdek khan avan üng khyang he kyükyawk u lü cäicah law khai he.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
“Khan ngsün law khaia kyase, khawmdek khana pha law khaia khuikhanak vai ngaihkyunak la kyühkyawk lawa phäha pi khyang he käikang law khai he.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
“Acunüng, khyanga Capa cun johit la hlüngtainak am khawngmei üng kyum law lü ngdang law khai.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
“Acun hea tünei law üng, ngdüi u lü han teng u, nami hama küikyannak ng'et law ve,” a ti.
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Acunüng, Jesuh naw ami veia msuimcäpnak pyen be lü, “Fik thing la thing avan jah ngai u;
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
“Hlip law se nami hmuh la khawkhye ng’et lawki ti nami ksingki.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
“Acukba bäa nangmi pi acun he awm law u se, nami jah hmu üng, Pamhnama khaw pha law hlüki ni ti ksing ua.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
“Hina khyang he am thi pha u se, acun he avan pha law khai ti ksing u.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
“Khankhaw la mce khyük ni se pi ka ngthu am khyük.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
“Acunakyase, a na cäiei u, am acunüng ta ei ngang, aw ngang u lü khawmdek khawhthema phäha nami mlunga bawngkha k'um üng, acuna mhmüp am nami sima pha law sawxat khai ni.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
“Acuna mhmüp cun ngvaia kba khawmdek avan üng awmkia khyang hea khana pha law khaia kyaki.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
“Acunakyase, kya law khaia khuikhanak üngka naw phyawng u lü khyanga Capaa ma nami ngdüi hlawt khaia anglät se ktaiyü u lü a na k’äih ua,” a ti.
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Acunüng Jesuh cun amhmüp tä se Temple k'uma jah mthei lü amthan tä se Olip mcung ami tia ktaiyü khaia citki.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
Angawi tä se a ngthu ngai khai hea khyang avan Temple üng citki he.