< Luka 20 >

1 Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
И бысть во един от дний онех, учащу Ему люди в церкви и благовествующу, приидоша священницы и книжницы со старцы
2 Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
и реша к Нему, глаголюще: рцы нам, коею областию сия твориши, или кто есть давый Тебе власть сию?
3 Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
Отвещав же рече к ним: вопрошу вы и Аз единаго словесе, и рцыте Ми:
4 baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
крещение Иоанново с небесе ли бе, или от человек?
5 Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
Они же помышляху в себе, глаголюще, яко аще речем: с небесе, речет: почто убо не веровасте ему?
6 Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
Аще ли же речем: от человек, вси людие камением побиют ны: известно бо бе о Иоанне, яко пророк бе.
7 Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
И отвещаша: не вемы откуду.
8 Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
Иисус же рече им: ни Аз глаголю вам, коею областию сия творю.
9 Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
Начат же к людем глаголати притчу сию: человек некий насади виноград, и вдаде его делателем, и отиде на лета многа:
10 A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
и во время посла к делателем раба, да от плода винограда дадут ему: делатели же бивше его, послаша тща.
11 Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
И приложи послати другаго раба: они же и того бивше и досадивше (ему), послаша тща.
12 Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
И приложи послати третияго: они же и того уязвльше изгнаша.
13 “Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
Рече же господин винограда: что сотворю? Послю сына моего возлюбленнаго, еда како, его видевше, усрамятся.
14 “Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
Видевше же его делателе, мышляху в себе, глаголюще: сей есть наследник: приидите, убием его, да наше будет достояние.
15 Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
И изведше его вон из винограда, убиша. Что убо сотворит им господин винограда?
16 Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
Приидет и погубит делатели сия и вдаст виноград инем. Слышавше же рекоша: да не будет.
17 Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
Он же воззрев на них, рече: что убо писаное сие: камень, егоже небрегоша зиждущии, сей бысть во главу угла?
18 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
Всяк падый на камени том, сокрушится: а на немже падет, стрыет его.
19 Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
И взыскаша архиерее и книжницы возложити Нань руце в той час и убояшася народа: разумеша бо, яко к ним притчу сию рече.
20 Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
И наблюдше послаша лаятели, притворяющих себе праведники быти: да имут Его в словеси, во еже предати Его началству и области игемонове.
21 Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
И вопросиша Его, глаголюще: Учителю, вемы, яко право глаголеши и учиши, и не на лица зриши, но воистинну пути Божию учиши:
22 Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
достоит ли нам кесареви дань даяти, или ни?
23 Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
Разумев же их лукавство, рече к ним: что Мя искушаете?
24 “Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
Покажите Ми цату: чий имать образ и надписание? Отвещавше же рекоша: кесарев.
25 Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
Он же рече им: воздадите убо, яже кесарева, кесареви, и яже Божия, Богови.
26 Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
И не могоша зазрети глаголгола Его пред людьми: и дивишася о ответе Его и умолчаша.
27 Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
Приступиша же нецыи от саддукей, глаголющии воскресению не быти, вопрошаху Его,
28 “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
глаголюще: Учителю, Моисей написа нам: аще кому брат умрет имый жену, и той безчаден умрет, да брат его поймет жену и возставит семя брату своему:
29 To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
седмь убо братий бе: и первый поят жену, умре безчаден:
30 Na biyun,
и поят вторый жену, и той умре безчаден:
31 da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
и третий поят ю: такожде же и вси седмь: и не оставиша чад и умроша:
32 A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
послежде же всех умре и жена:
33 Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
в воскресение убо, котораго их будет жена? Седмь бо имеша ю жену.
34 Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
И отвещав рече им Иисус: сынове века сего женятся и посягают: (aiōn g165)
35 amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
а сподобльшиися век он улучити и воскресение, еже от мертвых, ни женятся, ни посягают: (aiōn g165)
36 Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
ни умрети бо ктому могут: равни бо суть Ангелом и сынове суть Божии, воскресения сынове суще:
37 Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
а яко востают мертвии, и Моисей сказа при купине, якоже глаголет Господа Бога Авраамля и Бога Исаакова и Бога Иаковля:
38 Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Бог же несть мертвых, но живых: вси бо Тому живи суть.
39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
Отвещавше же нецыи от книжник рекоша: Учителю, добре рекл еси.
40 Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
Ктому же не смеяху Его вопросити ничесоже. Рече же к ним:
41 Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
како глаголют Христа Сына Давидова быти?
42 Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
Сам бо Давид глаголет в книзе псаломстей: рече Господь Господеви моему: седи о десную Мене,
43 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
дондеже положу враги Твоя подножие ногама Твоима.
44 Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
Давид убо Господа Его нарицает, и како Сын ему есть?
45 Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
Слышащым же всем людем, рече учеником Своим:
46 “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
внемлите себе от книжник хотящих ходити во одеждах и любящих целования на торжищих и председания на сонмищих и преждевозлежания на вечерях:
47 Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”
иже снедают домы вдовиц и виною далече молятся: сии приимут лишше осуждение.

< Luka 20 >