< Luka 20 >

1 Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
On one of these days, when Jesus was teaching the people in the Temple Courts and telling the Good News, the Chief Priests and the Teachers of the Law, joined by the Councillors, confronted him,
2 Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
and addressing him, said: “Tell us what authority you have to do these things. Who is it that has given you this authority?”
3 Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
“I, too,” said Jesus in reply, “will ask you one question. Give me an answer to it.
4 baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
It is about John’s baptism — was it of divine or of human origin?”
5 Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
But they began arguing together: “If we say ‘divine,’ he will say ‘Why did not you believe him?’
6 Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
But, if we say ‘human,’ the people will all stone us, for they are persuaded that John was a Prophet.”
7 Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
So they answered that they did not know its origin.
8 Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
“Then I,” said Jesus, “refuse to tell you what authority I have to do these things.”
9 Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
But Jesus began to tell the people this parable — “A man once planted a vineyard, and then let it out to tenants, and went abroad for a long while.
10 A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
At the proper time he sent a servant to the tenants, that they should give him a share of the produce of the vineyard. The tenants, however, beat him and sent him away empty-handed.
11 Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
The owner afterwards sent another servant; but the tenants beat and insulted this man too, and sent him away empty-handed.
12 Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
He sent a third; but they wounded this man also, and threw him outside.
13 “Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
‘What shall I do?’ said the owner of the vineyard. ‘I will send my son, who is very dear to me. Perhaps they will respect him.’
14 “Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
But, on seeing him, the tenants consulted with one another. ‘Here is the heir!’ they said. ‘Let us kill him, and then the inheritance will become ours.’
15 Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
So they threw him outside the vineyard and killed him. Now what will the owner of the vineyard do to them?
16 Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
He will come and put those tenants to death, and will let the vineyard to others.” “Heaven forbid!” they exclaimed when they heard it.
17 Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
But Jesus looked at them and said: “What then is the meaning of this passage? — ‘The very stone which the builders despised has now itself become the corner-stone.’
18 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
Every one who falls on that stone will be dashed to pieces, while any one on whom it falls — it will scatter him as dust.”
19 Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
After this the Teachers of the Law and the Chief Priest were eager to lay hands on Jesus then and there, but they were afraid of the people; for they saw that it was at them that he had aimed this parable.
20 Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
Having watched their opportunity, they afterwards sent some spies, who pretended to be good men, to catch Jesus in the course of conversation, and so enable them to give him up to the Governor’s jurisdiction and authority.
21 Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
These men asked Jesus a question. They said: “Teacher, we know that you are right in what you say and teach, and that you do not take any account of a man’s position, but teach the Way of God honestly;
22 Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
are we right in paying tribute to the Emperor or not?”
23 Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
Seeing through their deceitfulness, Jesus said to them:
24 “Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
“Show me a florin. Whose head and title are on it?”
25 Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
“The Emperor’s,” they said; and Jesus replied: “Well then, pay to the Emperor what belongs to the Emperor, and to God what belongs to God.”
26 Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
They could not lay hold of this answer before the people; and, in their wonder at his reply, they held their tongues.
27 Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
Presently there came up some Sadducees, who maintain that there is no resurrection. Their question was this —
28 “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
“Teacher, Moses laid down for us in his writings that — ‘Should a man’s married brother die, and should he be childless, the man should take the widow as his wife, and raise up a family for his brother.’
29 To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
Well, there were once seven brothers; of whom the eldest, after taking a wife, died childless.
30 Na biyun,
The second and third brothers both took her as their wife;
31 da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
and so, too, did all seven — dying without children.
32 A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
The woman herself was the last to die.
33 Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
About the woman, then — at the resurrection, whose wife is she to be, all seven brothers having had her as their wife?”
34 Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
“The men and women of this world,” said Jesus, “marry and are given in marriage; (aiōn g165)
35 amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
but, for those who are thought worthy to attain to that other world and the resurrection from the dead, there is no marrying or being married, (aiōn g165)
36 Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
nor indeed can they die again, for they are like angels and, having shared in the resurrection, they are God’s Sons.
37 Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
As to the fact that the dead rise, even Moses indicated that, in the passage about the Bush, when he calls the Lord — ‘The God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob.’
38 Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Now he is not God of dead men, but of living. For in his sight all are alive.”
39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
“Well said, Teacher!” exclaimed some of the Teachers of the Law,
40 Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
for they did not venture to question him any further.
41 Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
But Jesus said to them: “How is it that people say that the Christ is to be David’s son?
42 Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
For David, in the Book of Psalms, says himself — ‘The Lord said to my lord: “Sit at my right hand,
43 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
until I put thy enemies as a stool for thy feet.”’
44 Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
David, then, calls him ‘lord,’ so how is he David’s son?”
45 Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
While all the people were listening, Jesus said to the disciples:
46 “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
“Be on your guard against the Teachers of the Law, who delight to walk about in long robes, and like to be greeted in the streets with respect, and to have the best seats in the Synagogues, and places of honour at dinner.
47 Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”
These are the men who rob widows of their houses, and make a pretence of saying long prayers. Their sentence will be all the heavier.”

< Luka 20 >