< Luka 2 >

1 A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
And it came to pass in those days, that there went out a decree from Caesar Augustus that all the world should be taxed.
2 (Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
(And this taxing was first made when Cyrenius was governor of Syria.)
3 Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
And all went to be taxed, every one into his own city.
4 Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
And Joseph also went up from Galilee, out of the city of Nazareth, into Judaea, to the city of David, which is called Bethlehem; (because he was of the house and lineage of David: )
5 Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
To be taxed with Mary his espoused wife, being great with child.
6 Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
And so it was, that, while they were there, the days were accomplished that she should be delivered.
7 ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
And she brought forth her firstborn son, and wrapped him in swaddling clothes, and laid him in a manger; because there was no room for them in the inn.
8 Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
And there were in the same country shepherds abiding in the field, keeping watch over their flock by night.
9 Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
And, see, the angel of the Lord came on them, and the glory of the Lord shone round about them: and they were sore afraid.
10 Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
And the angel said to them, Fear not: for, behold, I bring you good tidings of great joy, which shall be to all people.
11 Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
For to you is born this day in the city of David a Savior, which is Christ the Lord.
12 Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
And this shall be a sign to you; You shall find the babe wrapped in swaddling clothes, lying in a manger.
13 Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
And suddenly there was with the angel a multitude of the heavenly host praising God, and saying,
14 “Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
Glory to God in the highest, and on earth peace, good will toward men.
15 Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
And it came to pass, as the angels were gone away from them into heaven, the shepherds said one to another, Let us now go even to Bethlehem, and see this thing which is come to pass, which the Lord has made known to us.
16 Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
And they came with haste, and found Mary, and Joseph, and the babe lying in a manger.
17 Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
And when they had seen it, they made known abroad the saying which was told them concerning this child.
18 duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
And all they that heard it wondered at those things which were told them by the shepherds.
19 Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
But Mary kept all these things, and pondered them in her heart.
20 Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
And the shepherds returned, glorifying and praising God for all the things that they had heard and seen, as it was told to them.
21 A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
And when eight days were accomplished for the circumcising of the child, his name was called JESUS, which was so named of the angel before he was conceived in the womb.
22 Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
And when the days of her purification according to the law of Moses were accomplished, they brought him to Jerusalem, to present him to the Lord;
23 (yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
(As it is written in the law of the LORD, Every male that opens the womb shall be called holy to the Lord; )
24 don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
And to offer a sacrifice according to that which is said in the law of the Lord, A pair of turtledoves, or two young pigeons.
25 To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
And, behold, there was a man in Jerusalem, whose name was Simeon; and the same man was just and devout, waiting for the consolation of Israel: and the Holy Ghost was on him.
26 An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
And it was revealed to him by the Holy Ghost, that he should not see death, before he had seen the Lord’s Christ.
27 Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
And he came by the Spirit into the temple: and when the parents brought in the child Jesus, to do for him after the custom of the law,
28 sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
Then took he him up in his arms, and blessed God, and said,
29 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
Lord, now let you your servant depart in peace, according to your word:
30 Gama idanuna sun ga cetonka,
For my eyes have seen your salvation,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
Which you have prepared before the face of all people;
32 haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
A light to lighten the Gentiles, and the glory of your people Israel.
33 Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
And Joseph and his mother marveled at those things which were spoken of him.
34 Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
And Simeon blessed them, and said to Mary his mother, Behold, this child is set for the fall and rising again of many in Israel; and for a sign which shall be spoken against;
35 ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
(Yes, a sword shall pierce through your own soul also, ) that the thoughts of many hearts may be revealed.
36 Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
And there was one Anna, a prophetess, the daughter of Phanuel, of the tribe of Aser: she was of a great age, and had lived with an husband seven years from her virginity;
37 ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
And she was a widow of about fourscore and four years, which departed not from the temple, but served God with fastings and prayers night and day.
38 Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
And she coming in that instant gave thanks likewise to the Lord, and spoke of him to all them that looked for redemption in Jerusalem.
39 Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
And when they had performed all things according to the law of the Lord, they returned into Galilee, to their own city Nazareth.
40 Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
And the child grew, and waxed strong in spirit, filled with wisdom: and the grace of God was on him.
41 Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
Now his parents went to Jerusalem every year at the feast of the passover.
42 Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
And when he was twelve years old, they went up to Jerusalem after the custom of the feast.
43 Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
And when they had fulfilled the days, as they returned, the child Jesus tarried behind in Jerusalem; and Joseph and his mother knew not of it.
44 Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
But they, supposing him to have been in the company, went a day’s journey; and they sought him among their kinsfolk and acquaintance.
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
And when they found him not, they turned back again to Jerusalem, seeking him.
46 Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
And it came to pass, that after three days they found him in the temple, sitting in the middle of the doctors, both hearing them, and asking them questions.
47 Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
And all that heard him were astonished at his understanding and answers.
48 Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
And when they saw him, they were amazed: and his mother said to him, Son, why have you thus dealt with us? behold, your father and I have sought you sorrowing.
49 Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
And he said to them, How is it that you sought me? knew you not that I must be about my Father’s business?
50 Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
And they understood not the saying which he spoke to them.
51 Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
And he went down with them, and came to Nazareth, and was subject to them: but his mother kept all these sayings in her heart.
52 Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.
And Jesus increased in wisdom and stature, and in favor with God and man.

< Luka 2 >