< Luka 2 >
1 A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
NOW it came to pass in those days, that there went out a decree from Caesar Augustus, that the whole land should be registered.
2 (Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
(And this first enrolment was made by Cyrenius, afterwards governor of Syria)
3 Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
And all went to be registered, every one to his own city.
4 Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
Then Joseph also went up from Galilee, from the city of Nazareth, to Judea, to the city of David, which is called Bethlehem; because he was of the house and family of David;
5 Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
to be enregistered with Mary, the wife espoused to him, who was big with child.
6 Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
And it came to pass, while they were there, that her time was up, that she should be delivered.
7 ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
And she brought forth a son, her first-born, and wrapped him in swaddling-clothes, and laid him in a manger, because there was no room for them in the inn.
8 Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
And there were shepherds in that country abiding in the open air, and keeping guard over their flock by night.
9 Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
And, behold, the angel of the Lord came upon them, and the glory of the Lord shone around them; and they were exceedingly affrighted.
10 Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
And the angel said unto them, Be not affrighted: for, behold, I bring you tidings of great joy, which shall be for all the people.
11 Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
Because this day there is born for you a Saviour, which is Messiah, the Lord, in the city of David.
12 Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
And this shall be a sign for you; Ye shall find the babe in swaddling-clothes, lying in a manger.
13 Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
And suddenly there appeared with the angel a multitude of the heavenly host, praising God, and saying,
14 “Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
Glory in the highest heavens to God! and upon earth, peace! towards men complacence.
15 Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
And it came to pass, as the angels went from them into heaven, the men, the shepherds, said also to each other, Let us now go to Bethlehem, and see this thing which hath happened, which the Lord hath made known to us.
16 Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
And they came with haste, and found Mary, and Joseph, and the babe, lying in the manger:
17 Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
and when they saw it, they made a public report of the declaration delivered to them respecting this child.
18 duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
And all who heard it, marvelled at the things told them by the shepherds.
19 Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
But Mary carefully preserved all these declarations, laying them together in her heart, in order to apprehend their meaning.
20 Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
And the shepherds returned, glorifying and praising God for all the things which they had heard and seen, exactly as had been told them.
21 A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
And when eight days were fulfilled for circumcising the child, his name also was called JESUS, the name imposed by the angel before he was conceived in the womb.
22 Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
And when the days of her purification were accomplished according to the law of Moses, they brought him to Jerusalem, to present him to the Lord;
23 (yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
as it is written in the law of the Lord, Every male child, that openeth the womb, shall be called holy to the Lord;
24 don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
and to offer a sacrifice, according to what is prescribed in the law of the Lord, A pair of turtle doves, or two young pigeons.
25 To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
And, behold, there was a man at Jerusalem, whose name was Simeon; and this man was righteous and devout, waiting for the consolation of Israel: and the Holy Ghost was upon him.
26 An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
And it had been divinely communicated to him by the Holy Spirit, that he should not see death, till he had seen the Lord’s Messiah.
27 Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
And he came by the spirit into the temple; just as the parents were bringing in the child Jesus, that they might do according to what was the custom of the law concerning him;
28 sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
and he took him into his arms, and blessed God, and said,
29 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
Now dismiss thy servant, Lord, according to thy word, in peace;
30 Gama idanuna sun ga cetonka,
for my eyes have seen thy salvation,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
which thou hast prepared before the face of all people.
32 haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
A light to give revelation to the Gentiles, and glory to thy people Israel.
33 Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
And Joseph and his mother were amazed at the things spoken concerning him.
34 Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
And Simeon blessed them, and said to Mary his mother, Behold, this child is appointed for the fall, and rising again of many in Israel; and for a marked object to be spoken against;
35 ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
(so shall a dart pierce through thy own soul) that the reasonings of many hearts may be laid open,
36 Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
And there was Anna, a prophetess, the daughter of Phanuel, of the tribe of Asser: she was far advanced in old age, having lived but seven years with a husband, from her virgin state:
37 ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
though she was now a widow, of about eighty-four years, who departed not from the temple, attending the divine service, with fastings and prayers night and day:
38 Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
and at the very same moment coming up, she also in turn confessed the Lord, and spake of him to all who were expecting redemption in Jerusalem.
39 Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
And when they had finished all things according to the law of the Lord, they returned into Galilee, into their own city Nazareth.
40 Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
And the child grew, and became endued with great powers of spirit, filled with wisdom; and the grace of God was upon him.
41 Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
And his parents went annually to Jerusalem at the feast of the passover.
42 Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
And when he was twelve years old, they went up to Jerusalem, according to the custom of the feast.
43 Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
And when they had concluded the days, as they were returning, the child Jesus remained at Jerusalem, and Joseph and his mother knew it not:
44 Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
but supposing him to be in the company, they went a day’s journey; and they sought him among their relations and acquaintances;
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
and not finding him, they returned to Jerusalem in search of him.
46 Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
And it came to pass after three days, they found him in the temple, sitting in the midst of the doctors, both hearing them and asking them questions.
47 Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
And all who heard him, were in a transport of admiration, at his understanding and answers.
48 Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
And when they saw him, they were struck with surprise; and his mother said to him, Son, why hast thou behaved to us in this manner? lo! thy father and I have been seeking thee in anguish of heart.
49 Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
And he said unto them, Wherefore did ye seek me? did you not know, that I must be occupied with my Father’s affairs?
50 Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
And they understood not the meaning of what he spake to them.
51 Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
And he went down with them, and came to Nazareth, and was in subjection to them: though his mother preserved all these sayings in her heart.
52 Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.
And Jesus advanced in wisdom and stature, and in favour with God and men.