< Luka 2 >

1 A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
ᎾᎯᏳᏃ ᎯᎠ ᏄᎵᏍᏔᏁᎢ, ᎾᏍᎩ ᏏᏌ ᎣᎦᏍᏓ ᎤᏁᏨᎯ ᎤᎾᏄᎪᏤ ᏂᎬᎾᏛ ᎡᎶᎯ ᎨᎦᏎᏍᏗᏱ.
2 (Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
ᎾᏍᎩ ᎯᎠ ᎤᎾᏎᎵᏙᎴ ᎠᏏ ᏌᎵᏂ ᏏᎵᏱ ᎤᎬᏫᏳᎯ ᏂᎨᏒᎾ ᏂᎨᏎᎢ.
3 Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
ᎠᎴ ᏂᎦᏛ ᎤᏁᏅᏎ ᎨᎦᏎᏍᏗᏱ ᎠᏂᏏᏴᏫᎭ ᎨᏒ ᏙᏓᏂᏚᎲᎢ.
4 Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
ᎠᎴ ᏦᏩ ᎾᏍᏉ ᎨᎵᎵ ᎤᏂᎩᏎᎢ ᎤᏄᎪᏤ ᎾᏎᎵᏗ ᎦᏚᎲᎢ, ᏭᎷᏤ ᏧᏗᏱ, ᏕᏫ ᏧᏪᏚᎲᎢ, ᎦᏚᏱ ᏧᏙᎢᏛ, ᏕᏫᏰᏃ ᎤᏁᏢᏔᏅᏛ ᎨᏒ ᏅᏓᏳᏓᎴᏅᎯ ᎨᏎᎢ ᎤᎦᏴᎵᎨ ᎨᏎᎢ ᎠᎴ ᏕᏫ,
5 Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
ᎨᎦᏎᏍᏗᏱ ᎤᏰᎸᏎ ᎤᏩᏒ ᎠᎴ ᎺᎵ ᎤᏓᏴᏍᏗ, ᎾᏍᎩ ᎦᏁᎵᏛ ᎨᏎᎢ.
6 Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
ᎯᎠᏃ ᏄᎵᏍᏔᏁᎢ, ᎾᏍᎩ ᎠᏏ ᎾᎿᎭᎠᏁᏙᎮᎢ, ᎤᏍᏆᎸᎮ ᎠᏲᎵ ᎤᎾᏄᎪᏫᏍᏗᏱ.
7 ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
ᎤᎾᏄᎪᏫᏎᏃ ᎢᎬᏱ ᎡᎯ ᎤᏪᏥ ᎠᏧᏣ, ᎠᎴ ᎤᏪᏣᏄᎳᏁᎢ, ᎠᎴ ᏐᏈᎵ ᎤᎾᎵᏍᏓᏴᏗᏱ ᎤᎸᏁᎢ; ᎥᏝᏰᏃ ᏳᏜᏓᏅᏕ ᏧᏂᏒᏍᏗᏱ ᎠᏓᏁᎸᎢ.
8 Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
ᎾᎿᎭᏃ ᎾᎥᎢ ᎠᏫ-ᏗᏂᎦᏘᏯ ᎠᏁᏙᎮ ᎤᏜᏓᏅᏛᎢ, ᎠᏫ ᏓᏂᎦᏘᏰ ᏒᏃᏱ.
9 Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
ᎬᏂᏳᏉᏃ ᏗᎧᎿᎭᏩᏗᏙᎯ ᏱᎰᏩ ᎤᏤᎵᎦ ᎤᏂᎷᏤᎴᎢ, ᎠᎴ ᎦᎸᏉᏗᏳ ᏚᎸᏌᏛ ᎤᎬᏫᏳᎯ ᎤᏤᎵᎦ ᏚᎾᏚᏫᏍᏔᏁᎢ ᎠᎴ ᎤᏣᏔᏅᎯ ᎤᏂᏍᎦᎴᎢ.
10 Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
ᏗᎧᎿᎭᏩᏗᏙᎯᏃ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ; ᏞᏍᏗ ᏱᏥᏍᎦᎢᎮᏍᏗ, ᎬᏂᏳᏉᏰᏃ ᎢᏨᏲᎯᏏ ᎣᏍᏛ ᎧᏃᎮᏛ ᎤᏣᏘ ᎠᎵᎮᎵᏍᏗ, ᎾᏂᎥ ᏴᏫ ᎤᎾᏛᎪᏗ.
11 Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
ᎪᎯᏰᏃ ᎢᎦ ᎢᏣᏕᏁᎸ ᏕᏫ ᎤᏪᏚᎲᎢ, ᎢᏥᏍᏕᎵᏍᎩ ᎾᏍᎩ ᎦᎶᏁᏛ ᎤᎬᏫᏳᎯ.
12 Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
ᎯᎠᏃ ᎾᏍᎩ ᎢᏣᏙᎯᎰᎯᏍᏙᏗ ᎨᏎᏍᏗ; ᏓᏰᏥᏩᏛᎯ ᎠᏲᎵ ᎠᏥᏣᏄᎴᏍᏗ, ᏐᏈᎵ ᎤᎾᎵᏍᏓᏴᏗᏱ ᎦᏅᎨᏍᏗ.
13 Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
ᎩᎳᏉᏃ ᎢᏴᏛ ᎤᏂᏣᏘ ᎦᎸᎳᏗ ᎠᏁᎯ ᎬᏩᎵᎪᏁᎴ ᏗᎧᎿᎭᏩᏗᏙᎯ, ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎠᏂᎸᏉᏗᏍᎨᎢ, ᎯᎠ ᎾᏂᏪᏍᎨᎢ;
14 “Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
ᎦᎸᏉᏗᏳ ᎨᏎᏍᏗ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᏩᏍᏛ ᎦᎸᎳᏗᏳ, ᎡᎶᎯᏃ ᏙᎯᎣ ᎨᏎᏍᏗ, ᎣᏍᏛ ᎨᎦᏓᏅᏖᏍᎨᏍᏗ ᏴᏫ.
15 Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
ᎿᎭᏉᏃ ᎯᎠ ᏄᎵᏍᏔᏁᎢ, ᎾᏍᎩ ᏗᏂᎧᎿᎭᏩᏗᏙᎯ ᎬᏩᎾᏓᏅᎡᎸ, ᎦᎸᎳᏗ ᏫᎤᏂᎶᏒ, ᎯᎠ ᏂᏚᎾᏓᏪᏎᎴ ᎠᏫ-ᏗᏂᎦᏘᏯ; Ꭷ, ᎿᎭᏉ ᎦᏚᏱ ᎢᏕᎾ, ᎠᎴ ᏫᏓᏙᎴᎰᎯ ᎾᏍᎩ ᎯᎠ ᏄᎵᏍᏔᏅᎢ, ᎾᏍᎩ ᏱᎰᏩ ᎬᏂᎨᏒ ᏥᏂᎬᏂᏏ.
16 Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
ᎤᎵᏍᏗᏳᏃ ᏭᏂᎷᏤᎢ, ᎠᎴ ᏚᏂᏩᏛᎮ ᎺᎵ ᎠᎴ ᏦᏩ, ᎠᎴ ᎠᏲᎵ ᏐᏈᎵ ᎤᎾᎵᏍᏓᏴᏗᏱ ᎦᏅᎨᎢ.
17 Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
ᎤᏂᎪᎲᏃ ᎤᏂᏃᎮᎵᏙᎴ ᏄᏍᏛ ᎨᏥᏃᎮᎮᎸ ᎾᏍᎩ ᎠᏲᎵ ᎠᏥᏁᎢᏍᏗᏍᎬᎢ.
18 duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
ᏂᎦᏛᏃ ᎤᎾᏛᎦᏅᎯ ᎤᏂᏍᏆᏂᎪᏎ ᏄᏍᏛ ᎬᏩᏂᏃᎮᎮᎸ ᎠᏫ-ᏗᏂᎦᏘᏯ.
19 Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
ᎺᎵᏍᎩᏂ ᎾᏍᎩ ᎯᎠ ᏂᎦᏛ ᎤᏍᏆᏂᎪᏔᏁᎢ, ᎠᎴ ᎾᏍᎩ ᎤᏓᏅᏖᎯᎶᎡ ᏧᏓᏅᏛᎢ.
20 Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
ᎠᏫᏃ-ᏗᏂᎦᏘᏯ ᎢᎤᎾᏨᏎᎢ, ᎠᏂᎸᏉᏗᏍᎨ ᎠᎴ ᎠᎾᎵᎮᎵᏤᎮ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᏅᏗᎦᎵᏍᏙᏗᏍᎨ ᏂᎦᎥ ᎤᎾᏛᎦᏅ ᎠᎴ ᎤᏂᎪᎲᎢ, ᎾᏍᎩ ᏄᏍᏛ ᎨᏥᏃᏁᎸᎢ.
21 A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
ᏧᏁᎵᏁᏃ ᎢᎦ ᎤᏍᏆᎸᎲ ᎾᏍᎩ ᎠᎱᏍᏕᏎᏗ ᎨᏒ ᎠᏲᎵ, ᏥᏌ ᏚᏃᎡᎢ, ᎾᏍᎩ ᏗᎧᎿᎭᏩᏗᏙᎯ ᏂᏚᏬᎡ ᎠᏏᏉ ᎾᏥᏁᎵᎬᎾ ᎨᏎᎢ.
22 Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
ᎿᎭᏉᏃ ᎤᏍᏆᎸᎲ ᎤᎾᏓᏅᎦᎸᏗᏱ ᎾᏍᎩᏯ ᏂᎬᏅ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᎼᏏ ᎤᏬᏪᎳᏅᎯ, ᏥᎷᏏᎵᎻ ᎤᏂᏃᎴ ᏱᎰᏩ ᎤᏂᎧᏁᏗᏱ;
23 (yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
ᎾᏍᎩᏯ ᏂᎬᏅ ᎪᏪᎸ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗᏱ ᎼᎰᏩ ᏣᏥᎵᎦ; ᎾᏂᎥ ᎢᎬᏱ ᎤᎾᏕᏅᎯ ᎠᏂᏍᎦᏯ ᏱᎰᏩ ᏣᏥᏲᎯᏎᎸᎯ ᎨᎪᏎᎮᏍᏗ;
24 don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
ᎠᎴ ᎠᏥᎸ-ᎨᎳᏍᏗ ᎤᎾᎵᏍᎪᎸᏙᏗᏱ ᎾᏍᎩᏯ ᎯᎠ ᏂᎦᏪᏍᎬ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᏱᎰᏩ ᎤᏤᎵᎦ; ᎠᏂᏔᎵ ᏧᎴᏗᏂᏍᎪᏂᎯ, ᎠᎴ ᎠᏂᏔᎵ ᎠᏂᏛ ᏬᏱ.
25 To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
ᎠᎴ ᎬᏂᏳᏉ ᎩᎶ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᏍᎦᏯ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᎡᎮ ᏏᎻᏯᏂ ᏧᏙᎢᏛ; ᎠᎴ ᎾᏍᎩ ᏚᏳᎪᏛ ᎢᏯᏛᏁᎯ ᎠᎴ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᏗᎧᎿᎭᏩᏕᎩ ᎨᏎᎢ, ᎠᎦᏘᏰ ᎢᏏᎵ ᎨᏥᏄᏬᎯᏍᏙᏗᏱ; ᎦᎸᏉᏗᏳᏃ ᎠᏓᏅᏙ ᏔᎵ ᎤᏛᏗᏕᎨᎢ.
26 An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
ᎠᎴ ᎬᏂᎨᏒ ᎢᏳᏩᏁᎸᎯ ᎨᏎ ᎦᎸᏉᏗᏳ ᎠᏓᏅᏙ, ᎾᏍᎩ ᎠᏲᎱᎯᏍᏗ ᎨᏒ ᎤᎪᏩᏛᏗ ᏂᎨᏒᎾ ᎨᏒ ᎬᏂ ᏱᎰᏩ ᎤᏤᎵ ᎦᎶᏁᏛ ᎤᎪᎲᎯ ᏱᎩ
27 Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
ᎠᎴ ᎠᏓᏅᏙ ᎤᏓᏅᏖᎮᎸᎯ ᏭᎷᏤ ᎤᏛᎾ-ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ; ᏧᎦᏴᎵᎨᏃ ᎤᏂᏴᏔᏂᎸ ᎠᏲᎵ ᏥᏌ ᎾᏍᎩ ᏂᎬᏅ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᎢᏳᎾᏛᏁᏗᏱ,
28 sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
ᎿᎭᏉ ᎾᏍᎩ ᎤᏁᏎᎢ, ᎠᎴ ᎤᎸᏉᏔᏁ ᎤᏁᎳᏅᎯ, ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎢ;
29 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
ᏣᎬᏫᏳᎯ, ᎿᎭᏉ ᎯᏅᏏᏓᏍᏗ ᏅᏩᏙᎯᏯᏛ ᏕᎯᏲᏍᎦ, ᎾᏍᎩᏯ ᏂᏣᏪᏒ ᏣᏁᏨᎢ;
30 Gama idanuna sun ga cetonka,
ᏗᏥᎦᎵᏰᏃ ᎬᏗ ᏥᎪᏩᏛ ᏣᏤᎵ ᎠᎵᏍᏕᎸᏙᏗ.
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
ᎾᏍᎩ ᏣᏓᏁᎳᏅᎯ ᏥᎩ ᎾᏂᎥ ᏴᏫ ᎠᏂᎦᏔᎲᎢ,
32 haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
ᎢᎦ-ᎦᏘ ᏧᏂᎸᏌᏓᏕᏗ ᏧᎾᏓᎴᏅᏛ ᏴᏫ, ᎠᎴ ᎦᎸᏉᏗᏳ ᎨᏒ ᏗᏣᏤᎵ ᏴᏫ ᎢᏏᎵ ᎤᎾᏤᎵᎦ.
33 Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
ᏦᏩᏃ ᎠᎴ ᎠᏲᎵ ᎤᏥ ᎠᏂᏍᏆᏂᎪᏍᎨ ᏄᏍᏛ ᎠᏥᏁᎢᏍᏗᏍᎬ ᎾᏍᎩ.
34 Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
ᎻᎻᏯᏂᏃ ᎣᏍᏛ ᏚᏁᏤᎴᎢ, ᎠᎴ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴ ᎺᎵ ᎠᏲᎵ ᎤᏥ, ᎬᏂᏳᏉ ᎯᎠ ᎾᏍᎩ ᎠᏲᎵ ᎠᏥᎧᏅ ᎾᏍᎩ ᎢᏏᎵ ᎠᏁᎯ ᎤᏂᏣᏘ ᏧᏂᏅᎢᏍᏗᏱ ᎠᎴ ᏧᎾᎴᎯᏐᏙᏗᏱ; ᎠᎴ ᎤᏰᎸᏛ ᎤᎾᏡᏙᏗ ᎠᏂᏬᏂᏍᎬᎢ.
35 ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
ᎾᏍᎩ ᎤᏂᏣᏘ ᏄᏍᏛ ᏓᎾᏓᏅᏖᏍᎬ ᏧᏂᎾᏫᏱ ᎬᏂᎨᏒ ᎢᏳᎵᏍᏙᏗᏱ: ᎥᎥ, ᎠᏰᎳᏍᏗ-ᎦᏅᎯᏛ ᎾᏍᏉ ᏨᏒ ᏣᏓᏅᏙ ᏓᏣᏘᎵ.
36 Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
ᎠᎴ ᎩᎶ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᎨᏴ ᎡᏂ ᏧᏙᎢᏛ ᎠᏙᎴᎰᏍᎩ ᎡᎮᎢ, ᎾᏍᎩ ᏆᏄᎡᎵ ᎤᏪᏥ ᎨᏎᎢ, ᎡᏌ ᎠᏂᎳᏍᏓᎸ ᎤᏠᏱ, ᎾᏍᎩ ᎤᏣᏘ ᎠᎦᏴᎵᎨ ᎨᏎᎢ, ᎠᎴ ᎦᎵᏉᎩ ᎢᏧᏕᏘᏴᏛ ᎤᎾᏁᎳᏛᎯ ᎨᏎ ᎠᏍᎦᏯ ᎠᏛᏉ ᎨᏒ ᏧᎾᏨᏛ;
37 ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
ᎠᎴ ᎤᏬᏑᎶᏨᎯ ᎨᏎ ᏁᎳᏍᎪᎯ ᏅᎩᎦᎵ ᎢᏴᏛ ᎢᏳᏕᏘᏴᏛ, ᎾᏍᎩ ᎥᏝ ᏱᏓᏅᏍᎨ ᎤᏛᎾ-ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ, ᎤᏁᎳᏅᎯᏉ ᏓᎧᎿᎭᏩᏗᏎᎢ ᎠᎹᏟ ᎬᏍᎬ ᎠᎴ ᎠᏓᏙᎵᏍᏗᏍᎬ ᏂᏚᎵᏏᏂᏒ ᎠᎴ ᏂᏚᎩᏨᏂᏒᎢ.
38 Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
ᎾᏍᎩᏃ ᎾᏍᏉ ᎾᎯᏳᏉ ᎤᎷᏤ ᎤᎵᎮᎵᏤᎴ ᏱᎰᏩ, ᎠᎴ ᎾᏍᎩ ᏕᎧᏁᎢᏍᏓᏁᎮ ᎾᏂᎥᏉ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᎠᏁᎯ ᎠᏂᎦᏖᏃᎯ ᎠᎫᏴᏙᏗ ᎨᏒ ᎤᎾᏄᎪᎢᏍᏗᏱ.
39 Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
ᎤᏂᏍᏆᏛᏃ ᏂᎦᏛ ᎢᏯᏛᏁᎵᏓᏍᏗ ᎨᏒ ᎾᏍᎩᏯ ᏂᎬᏅ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᏱᎰᏩ ᎤᏤᎵᎦ, ᎢᎤᎾᏨᏎ ᎨᎵᎵ ᏭᏂᎶᏎ, ᎤᏅᏒ ᏧᏂᏚᎲ ᎾᏎᎵᏗ ᏭᏂᎷᏤᎢ.
40 Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
ᎠᏲᎵᏃ ᎠᏛᏍᎨᎢ ᎠᎴ ᎤᏓᏅᏛ ᎠᎵᏂᎪᏍᎨᎢ, ᎤᎧᎵᏨᎯ ᎨᏎ ᎠᎦᏙᎥᎯᏍᏗ ᎨᏒᎢ; ᎠᎴ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏓᏙᎵᏍᏗ ᎨᏒ ᏚᎧᎿᎭᏩᏗᏙᎮᎢ.
41 Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
ᏧᎦᏴᎵᎨᏃ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᎠᏁᎨ ᏂᏓᏕᏘᏴᎯᏒ ᎧᏃᎯᏰᎩ ᏗᎵᏍᏓᏴᏗᏱ ᎠᏍᏆᎵᏍᎬ ᎢᏳᎢ.
42 Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
ᏔᎳᏚᏃ ᎢᏳᏕᏘᏴᏛ ᎨᏎ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᎤᏁᏅᎭ ᎾᏍᎩᏯ ᎢᏳᎾᏛᏁᏗ ᎨᏒ ᏓᎾᎵᏍᏓᏴᎲᏍᎬ ᎢᏳᎢ.
43 Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
ᎤᏂᏍᏆᏛᏃ ᎢᎪᎯᏛ ᏚᎵᏒᏍᏛᎢ, ᎥᎤᎾᏨᏏᏗᏒ ᎠᏲᎵ ᏥᏌ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᏗᎤᏗᎩᏰᎢ, ᏦᏩᏃ ᎠᎴ ᎤᏥ ᎥᏝ ᏱᏁᎵᏍᎨᎢ.
44 Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
ᎾᏍᎩᏃ ᏑᎾᏓᏡᎩ ᎠᎾᎢᏒ ᎨᎳᏗ ᎠᏁᎵᏍᎬ ᏏᎦ ᎡᏅᏍᏗ ᎢᏴᏛ ᎤᏁᏅᏎᎢ; ᎪᎱᏍᏗᏃ ᏧᏅᏅ ᎠᎴ ᏗᎾᏓᎦᏔᎯ ᎠᏂᏅ ᎤᏂᏲᎴᎢ.
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
ᎬᏩᏠᏨᏃ ᎢᎤᎾᏨᏎᎢ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᏭᏂᎶᏎ ᎬᏩᏲᎮᎢ.
46 Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
ᎯᎠᏃ ᏄᎵᏍᏔᏁᎢ, ᎾᏍᎩ ᏦᎢᏁ ᎢᎦ ᎤᏂᏩᏛᎮ ᎤᏛᏃᎯ ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ, ᎤᏬᎴ ᎠᏰᎵ ᎠᏂᏅ ᏗᎾᏕᏲᎲᏍᎩ ᏓᏛᏓᏍᏓᏁᎮ ᎠᎴ ᏓᏛᏛᎮᎸᎥᏍᎨᎢ.
47 Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
ᏂᎦᏛᏃ ᎬᏩᏛᎦᏁᎸᎯ ᎤᏂᏍᏆᏂᎪᏎ ᏃᏒ ᎪᎵᎬᎢ, ᎠᎴ ᎬᏩᏛᏛᎲᏍᎬ ᏕᎦᏬᎯᎵᏴᏍᏓᏁᎲᎢ.
48 Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
ᏧᎦᏴᎵᎨᏃ ᎬᏩᎪᎲ ᎤᏂᏍᏆᏂᎪᏎᎢ; ᎤᏥᏃ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴᎢ ᎠᏇᏥ, ᎦᏙᏃ ᏅᏍᎩᎾᏛᏂᏏᏉ? ᏣᏙᏓ ᎢᏍᏛᏲᎲᎩ ᎤᏪᎵᎯᏍᏗ ᎣᎩᎾᏓᏅᏔᏩᏕᎬᎩ.
49 Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
ᎯᎠᏃ ᏂᏚᏪᏎᎴᎢ; ᎦᏙᏃ ᎢᏍᎩᏂᏲᎮᎢ? ᏝᏍᎪ ᏱᏍᏗᎦᏔᎮ ᎡᏙᏙᏱ ᎠᏎ ᎠᏇᏓᏍᏗ ᎨᏒᎢ?
50 Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
ᎠᏎᏃ ᎥᏝ ᏳᏃᎵᏤ ᎾᏍᎩ ᏂᏚᏪᏎᎸᎢ.
51 Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
ᏚᏍᏓᏩᏛᏎᏃ, ᎠᎴ ᎾᏎᎵᏗ ᏭᎷᏤᎢ, ᎠᎴ ᏕᎤᏁᎶᏕᎢ. ᎤᏥᏍᎩᏂ ᎯᎠ ᎾᏍᎩ ᏂᎦᏛ ᎤᏍᏆᏂᎪᏔᏁ ᎤᎾᏫᏱ.
52 Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.
ᎠᎴ ᏥᏌ ᎧᏁᏉᏥᏎ ᎠᎦᏔᎿᎭᎢᏳ ᎨᏒ ᎠᎴ ᎠᏛᏍᎬᎢ ᎠᎴ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎠᎴ ᏴᏫ ᎬᏩᎨᏳᎯᏳ ᎨᏒᎢ.

< Luka 2 >