< Luka 19 >
1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
In vnide, in šel je skozi Jeriho.
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
In glej, mož po imenu Zahej, in ta je bil starešina mitarjem, in bil je bogat,
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
In rad bi bil videl Jezusa, kdo da je; pa ni mogel za voljo ljudstva, ker je bil majhne postave.
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
In poletel je naprej, in zlezel je na murvo, da bi ga videl: ker je imel todi mimo iti.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
In Jezus, ko pride na to mesto, ozrè se gor, in ugleda ga, in reče mu: Zahej, snidi hitro! kajti danes moram v tvojej hiši ostati.
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
Pa snide hitro in ga radosten sprejme.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
In vsi so, ko so to videli, godrnjali, govoreč: Pri grešnem človeku se je navrnil!
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
Pristopivši pa Zahej, reče Gospodu: Glej, polovico premoženja svojega, Gospod, dajem ubogim; in če sem koga ogoljufal, povrnil mu bom čvetero.
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
Jezus mu pa reče: Danes je prišlo zveličanje tej hiši, ker je tudi ta sin Abrahamov.
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
Kajti prišel je sin človečji iskat in zveličat, kar se je izgubilo.
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
Ko so pa to poslušali, pristavi in pové priliko, zato, ker je bil blizu Jeruzalema, in so mislili, da se bo kraljestvo Božje precej razodelo.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
In reče: Neki človek imenitnega rodú je šel v daljno deželo, da si vzeme kraljestvo, in da se vrne.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
In poklicavši deset hlapcev, dá jim deset mošenj, in reče jim: Kupčujte, dokler se ne vrnem.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
Meščani njegovi so ga pa sovražili, ter pošljejo poslance za njim, govoreč: Nečemo, da bi nam ta kraljeval.
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
In zgodí se, ko je bil kraljestvo prejel in se je vrnil, pa reče, naj mu pokličejo te hlapce, kterim je bil dal srebro, da bi zvedel, kaj je kdo prikupčeval.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
Pa pride prvi, govoreč: Gospod, mošnja tvoja je pridobila deset mošenj.
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
In reče mu: Dobro, vrli hlapec! ker si bil v najmanjem zvest, iméj oblast nad desetémi mesti.
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
In pride drugi, govoreč: Gospod, mošnja tvoja je napravila pet mošenj.
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
In tudi temu reče: Tudi ti bodi nad petémi mesti.
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
In drugi pride, govoreč: Gospod, glej, tu je mošnja tvoja, ktero sem imel v prtu spravljeno.
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
Kajti bal sem se te, ker si trd človek: jemlješ, česar nisi položil; žanješ, česar nisi posejal.
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
Pa mu reče: Sodil te bom po tvojih besedah, hudobni hlapec! Vedel si, da sem trd človek, in jemljem, česar nisem položil, in žanjem, česar nisem posejal;
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
In za kaj nisi dal srebra mojega kupcu, da bi ga bil, kedar bi se bil vrnil, prejel z dobičkom?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
Ter reče tém, kteri so stali pred njim: Vzemite mu mošnjo, in dajte tistemu, kteri jih ima deset.
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
(Pa mu rekó: Gospod, deset mošenj ima!)
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
Pravim vam namreč, da vsakemu, kdor ima, dalo se bo; a kdor nima, odvzelo mu se bo tudi to, kar ima.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
A tiste sovražnike moje, kteri niso hoteli, da bi jim kraljeval, pripeljite sêm, in posekajte jih pred menoj.
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
In ko je bil to povedal, šel je dalje, gredoč gor v Jeruzalem.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
In zgodí se, ko se približa Betfagi in Betaniji, pri gori, ktera se imenuje Oljska, pošlje dva izmed učencev svojih,
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
Govoreč: Pojdita v vas, ki je nasproti, v kterej bosta našla, kedar vnideta, žrebe privezano, na ktero se ni nikoli noben človek usedel: odvežita ga, in pripeljita sèm.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
In če vaju kdo vpraša: Po kaj odvezujeta? povejta mu tako: Gospod ga potrebuje.
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
In poslanca odideta in najdeta, kakor jima je bil rekel.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
Ko sta pa žrebe odvezovala, rekó jima gospodarji njegovi: Kaj odvezujeta žrebe?
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
Ona pa rečeta: Gospod ga potrebuje.
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
In pripeljeta k Jezusu; in položivši svoja oblačila na žrebe, posadé Jezusa.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
Ko je pa šel, pogrinjali so oblačila svoja na pot.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
In ko se je uže bližal strmcu Oljske gore, začne vsa množica učencev radostna Boga hvaliti z močnim glasom za vse čudeže, ktere so videli,
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
Govoreč: Blagoslovljen kralj, kteri gre v imenu Gospodovem! Mir na nebu, in slava na višavah!
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
In nekteri Farizeji izmed ljudstva mu rekó: Učenik, popréti učencem svojim!
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
In odgovarjajoč, reče jim: Pravim vam, da če ti umolkneje, vpilo bo kamenje.
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
In ko se približa in ugleda mesto, razjoka se nad njim,
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
Govoreč: Ko bi pač tudi ti vedelo, vsaj ta dan tvoj, kaj je za mir tvoj: ali sedaj je skrito pred očmí tvojimi.
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
Prišli bodo namreč nate dnevi, ko te bodo obdali sovražniki tvoji z nasipi, in te bodo oblegali, in stiskali te od vseh stranî;
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
In razbili bodo tebe in otroke tvoje v tebi, in ne kamena na kamenu ne bodo pustili v tebi: za to, ker nisi poznalo časa, v kterim si bilo obiskano.
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
In ko vnide v tempelj, začne izganjati tiste, kteri so prodajali v njem in kupovali,
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
Govoreč jim: Pisano je: "Dom moj je dom molitve;" a vi ste naredili iz njega "jamo razbojniško".
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
In učil je vsak dan v tempeljnu; a véliki duhovni in pismarji in prvaki ljudski so iskali, da bi ga pogubili;
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
In niso nahajali, kaj bi mu storili: kajti ljustvo se ga je držalo vse, poslušajoč ga.