< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
Et il entra dans Jéricho, et traversa [la ville].
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
Et voici, un homme, appelé du nom de Zachée: et il était chef de publicains, et il était riche;
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
et il cherchait à voir Jésus, quel il était; et il ne pouvait, à cause de la foule, car il était petit de taille.
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
Et, courant en avant, il monta sur un sycomore pour le voir; car il allait passer là.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
Et quand il fut venu à cet endroit, Jésus, regardant, le vit, et lui dit: Zachée, descends vite; car il faut que je demeure aujourd’hui dans ta maison.
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
Et il descendit à la hâte, et le reçut avec joie.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
Et voyant cela, tous murmuraient, disant qu’il était entré chez un pécheur pour y loger.
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
Et Zachée, se tenant là, dit au Seigneur: Voici, Seigneur, je donne la moitié de mes biens aux pauvres; et si j’ai fait tort à quelqu’un par une fausse accusation, je lui rends le quadruple.
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
Et Jésus lui dit: Aujourd’hui [le] salut est venu à cette maison, vu que lui aussi est fils d’Abraham;
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
car le fils de l’homme est venu chercher et sauver ce qui était perdu.
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
Et comme ils entendaient ces choses, il ajouta et [leur] dit une parabole, parce qu’il était près de Jérusalem, et qu’ils pensaient que le royaume de Dieu allait immédiatement paraître.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
Il dit donc: Un homme noble s’en alla dans un pays éloigné, pour recevoir un royaume et revenir.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
Et ayant appelé dix de ses propres esclaves, il leur donna dix mines, et leur dit: Trafiquez jusqu’à ce que je vienne.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
Or ses concitoyens le haïssaient; et ils envoyèrent après lui une ambassade, disant: Nous ne voulons pas que celui-ci règne sur nous.
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
Et il arriva, à son retour, après qu’il eut reçu le royaume, qu’il commanda d’appeler auprès de lui ces esclaves auxquels il avait donné l’argent, afin de savoir combien chacun aurait gagné par son trafic.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
Et le premier se présenta, disant: Maître, ta mine a produit dix mines.
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
Et il lui dit: Bien, bon esclave, parce que tu as été fidèle en ce qui est très peu de chose, aie autorité sur dix villes.
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
Et le second vint, disant: Maître, ta mine a produit cinq mines.
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
Et il dit aussi à celui-ci: Et toi, sois [établi] sur cinq villes.
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
Et un autre vint, disant: Maître, voici ta mine, que j’ai gardée déposée dans un linge;
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
car je t’ai craint, parce que tu es un homme sévère: tu prends ce que tu n’as pas mis, et tu moissonnes ce que tu n’as pas semé.
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
Il lui dit: Je te jugerai par ta propre parole, méchant esclave: tu savais que moi je suis un homme sévère, prenant ce que je n’ai pas mis et moissonnant ce que je n’ai pas semé;
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
et pourquoi n’as-tu pas mis mon argent à la banque, et quand je serais venu je l’aurais retiré avec l’intérêt?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
Et il dit à ceux qui étaient présents: Ôtez-lui la mine et donnez-la à celui qui a les dix mines.
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
– Et ils lui dirent: Seigneur, il a dix mines.
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
– Car je vous dis qu’à quiconque a, il sera donné; et à celui qui n’a pas, cela même qu’il a lui sera ôté.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
Mais ceux-là, mes ennemis, qui n’ont pas voulu que je règne sur eux, amenez-les ici et tuez-les devant moi.
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
Et ayant dit ces choses, il allait devant eux, montant à Jérusalem.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
Et il arriva, comme il approchait de Bethphagé et de Béthanie, vers la montagne appelée des Oliviers, qu’il envoya deux de ses disciples,
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
disant: Allez au village qui est vis-à-vis; et y étant entrés, vous trouverez un ânon attaché, sur lequel jamais aucun homme ne s’assit; détachez-le, et amenez-le.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
Et si quelqu’un vous demande pourquoi vous le détachez, vous lui direz ainsi: Le Seigneur en a besoin.
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
Et ceux qui étaient envoyés, s’en allant, trouvèrent [tout] comme il le leur avait dit.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
Et comme ils détachaient l’ânon, les maîtres de celui-ci leur dirent: Pourquoi détachez-vous l’ânon?
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
Et ils dirent: Parce que le Seigneur en a besoin.
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
Et ils l’amenèrent à Jésus; et ayant jeté leurs vêtements sur l’ânon, ils mirent Jésus dessus.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
Et comme il allait son chemin, ils étendaient leurs vêtements sur le chemin.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
Et comme il approchait déjà, à la descente de la montagne des Oliviers, toute la multitude des disciples, se réjouissant, se mit à louer Dieu à haute voix pour tous les miracles qu’ils avaient vus,
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
disant: Béni soit le roi qui vient au nom du Seigneur! Paix au ciel, et gloire dans les lieux très hauts!
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
Et quelques-uns des pharisiens lui dirent du milieu de la foule: Maître, reprends tes disciples.
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
Et répondant, il leur dit: Je vous dis que si ceux-ci se taisent, les pierres crieront.
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
Et quand il fut proche, voyant la ville, il pleura sur elle,
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
disant: Si tu avais connu, toi aussi, au moins en cette tienne journée, les choses qui appartiennent à ta paix! mais maintenant elles sont cachées devant tes yeux.
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
Car des jours viendront sur toi, où tes ennemis t’entoureront de tranchées, et t’environneront, et te serreront de tous côtés,
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
et te renverseront par terre, toi et tes enfants au-dedans de toi; et ils ne laisseront pas en toi pierre sur pierre, parce que tu n’as point connu le temps de ta visitation.
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
Et il entra au temple, et se mit à chasser dehors ceux qui y vendaient et qui y achetaient,
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
leur disant: Il est écrit: « Ma maison est une maison de prière »; mais vous, vous en avez fait une caverne de voleurs.
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
Et il enseignait tous les jours dans le temple; et les principaux sacrificateurs et les scribes, et les principaux du peuple, tâchaient de le faire mourir.
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
Et ils ne trouvaient rien qu’ils puissent faire; car tout le peuple se tenait suspendu à ses lèvres pour l’entendre.

< Luka 19 >