< Luka 19 >
1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
And Jesus having entred Jericho passed through the city,
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
and behold, there was a man named Zaccheus, who was the chief publican, and very rich.
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
And he sought to see Jesus who He was; but he could not for the croud; for he was little of stature.
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
And he ran before and got up into a sycamore-tree that he might see Him; for He was to pass by that way.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
And when Jesus came to the place, He looked up and saw him, and said to him, Zaccheus, make haste and come down; for to-day I must abide at thy house.
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
And he made haste and came down, and received Him with joy.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
And when they saw it, they all murmured, saying, He is gone to be guest with a wicked man.
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
But Zaccheus stood up and said unto Jesus, Behold, Lord, the half of my substance I give to the poor; and if I have taken any thing from any one wrongfully, I restore him fourfold.
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
Then said Jesus, This day is salvation come to this house, for as much as he also is a son of Abraham.
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
For the Son of man is come to seek and to save that which was lost.
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
And as they listened to these things, He proceeded and spake a parable; because He was nigh to Jerusalem, and they thought that the kingdom of God would immediately be manifested.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
He said therefore, A certain nobleman went into a distant country to receive the investiture of a kingdom and then to return.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
And he called ten of his servants, and delivered to them ten pounds, and said, Trade with them till I come.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
But his citizens hated him, and sent an embassy after him, saying, We will not have this man to reign over us.
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
And when he was returned, having received the kingdom, he ordered these servants to be called to him, to whom he had delivered the money, that he might know what use each had made of it.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
Then came the first and said, Lord, thy pound hath gained ten pounds.
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
And he said to him, Well done, thou good servant, as thou hast been faithful in a very little, thou shalt be governor over ten cities.
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
And the second came, saying, Lord, thy pound hath produced five pounds:
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
and he said to this likewise, Be thou also over five cities.
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
And another came, and said, Behold, my Lord, thy pound, which I have kept laid up in a napkin:
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
for I was afraid of thee, because thou art an austere man, who takest up what thou didst not lay down, and reapest what thou didst not sow.
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
But he said to him, Out of thy own mouth will I judge thee, thou wicked servant, Thou knewest that I am an austere man, taking up what I laid not down, and reaping what I did not sow;
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
and why then didst thou not put my money into the bank, that when I came I might have received it with interest?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
And he said to them that stood by, Take away the pound from him, and give it to him that hath the ten pounds.
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
(And they said unto him, Lord, he hath ten pounds already: )
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
for I tell you, that to every one that hath shall be given; but from him that hath not, even what he seemingly hath shall be taken away.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
But those mine enemies, who would not have me to reign over them, bring hither, and slay them before me.
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
And when He had said these things, He went forward, going up to Jerusalem.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
And when He was nigh to Bethphage and Bethany, at the mount called the mount of Olives, He sent two of his disciples,
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
saying, Go into the opposite village, in which, at your entring, ye will find a colt tied, on which no man ever yet sat; loose him and bring him hither.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
And if any one ask you, Why do ye loose him? thus shall ye say unto him, The Lord hath need of him.
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
And they that were sent, went away and found it as He had told them.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
But as they were untying the colt, the owners of it said to them, Why do ye untie the colt?
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
and they answered, The Lord hath need of him.
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
And they brought him to Jesus: and throwing their garments upon the colt they set Jesus thereon.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
And as He went along they spread their clothes under Him in the way.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
And when He was now come near to the foot of the mount of Olives, the whole multitude of the disciples rejoicing began to praise God with a loud voice for all the mighty works which they had seen,
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
saying, Blessed be the king that cometh in the name of the Lord: peace in heaven, and glory in the highest!
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
And some of the pharisees from among the multitude said to Him, Master, rebuke thy disciples.
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
And He answered them, I tell you, that if these were silent, the very stones would cry out.
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
And as He drew near, beholding the city, He wept over it,
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
saying, If thou hadst known, even thou, at lest in this thy day, the things relating to thy peace--- but now they are hid from thine eyes.
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
For the days shall come upon thee, that thine enemies shall cast up a trench about thee, and surround thee, and keep thee in on every side,
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
and shall lay thee to the ground, and thy children within thee; and they shall not leave in thee one stone upon another: because thou didst not regard the time of thy visitation.
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
And He went into the temple, and cast out those that were buying and selling in it,
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
saying unto them, It is written, "my house is the house of prayer: but ye have made it a den of thieves."
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
And He was teaching daily in the temple: but the chief priests and the scribes and the rulers of the people sought to destroy Him;
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
and could not find how to effect it: for all the people were attentive to hear Him.