< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
So He entered Jericho and was passing through the town.
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
There was a man there called Zacchaeus, who was the local surveyor of taxes, and was wealthy.
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
He was anxious to see what sort of man Jesus was; but he could not because of the crowd, for he was short in stature.
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
So he ran on in front and climbed up a mulberry tree to see Him; for He was about to pass that way.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
As soon as Jesus came to the place, He looked up and said to him, "Zacchaeus, come down quickly, for I must stay at your house to-day."
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
So he came down in haste, and welcomed Him joyfully.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
When they all saw this, they began to complain with indignation. "He has gone in to be the guest of a notorious sinner!" they said.
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
Zacchaeus however stood up, and addressing the Lord said, "Here and now, Master, I give half my property to the poor, and if I have unjustly exacted money from any man, I pledge myself to repay to him four times the amount."
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
Turning towards him, Jesus replied, "To-day salvation has come to this house, seeing that he too is a son of Abraham.
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
For the Son of Man has come to seek and to save that which was lost."
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
As they were listening to His words, He went on to teach them by a parable, because He was near to Jerusalem and they supposed that the Kingdom of God was going to appear immediately.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
So He said to them, "A man of noble family travelled to a distant country to obtain the rank of king, and to return.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
And he called ten of his servants and gave each of them a pound, instructing them to trade with the money during his absence.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
"Now his countrymen hated him, and sent a deputation after him to say, 'We are not willing that he should become our king.'
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
And upon his return, after he had obtained the sovereignty, he ordered those servants to whom he had given the money to be summoned before him, that he might learn their success in trading.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
"So the first came and said, "'Sir, your pound has produced ten pounds more.'
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
"'Well done, good servant,' he replied; 'because you have been faithful in a very small matter, be in authority over ten towns.'
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
"The second came, and said, "'Your pound, Sir, has produced five pounds.'
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
"So he said to this one also, "'And you, be the governor of five towns.'
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
"The next came. "'Sir,' he said, 'here is your pound, which I have kept wrapt up in a cloth.
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
For I was afraid of you, because you are a severe man: you take up what you did not lay down, and you reap what you did not sow.'
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
"'By your own words,' he replied, 'I will judge you, you bad servant. You knew me to be a severe man, taking up what I did not lay down, and reaping what I did not sow:
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
why then did you not put my money into a bank, that when I came I might have received it back with interest?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
"And he said to those who stood by, "'Take the pound from him and give it to him who has the ten pounds.'
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
("They said to him, "'Sir, he already has ten pounds.')
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
"'I tell you that to every one who has anything, more shall be given; and from him who has not anything, even what he has shall be taken away.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
But as for those enemies of mine who were unwilling that I should become their king, bring them here, and cut them to pieces in my presence.'"
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
After thus speaking, He journeyed onward, proceeding up to Jerusalem.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
And when he was come near Bethphage and Bethany, at the Mount called the Oliveyard, He sent two of the disciples on in front,
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
saying to them, "Go into the village facing you. On entering it you will find an ass's foal tied up which no one has ever yet ridden: untie it, and bring it here.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
And if any one asks you, 'Why are you untying the colt?' simply say, 'The Master needs it.'"
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
So those who were sent went and found things as He had told them.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
And while they were untying the colt the owners called out, "Why are you untying the colt?"
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
and they replied, "The Master needs it."
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
Then they brought it to Jesus, and after throwing their outer garments on the colt they placed Jesus on it.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
So He rode on, while they carpeted the road with their garments.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
And when He was now getting near Jerusalem, and descending the Mount of Olives, the whole multitude of the disciples began in their joy to praise God in loud voices for all the mighty deeds they had witnessed.
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
"Blessed is the King," they cried, "who comes in the name of the Lord: in Heaven peace, and glory in the highest realms."
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
Thereupon some of the Pharisees in the crowd appealed to Him, saying, "Rabbi, reprove your disciples."
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
"I tell you," He replied, "that if they became silent, the very stones would cry out."
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
When He came into full view of the city, He wept aloud over it, and exclaimed,
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
"O that at this time thou hadst known--yes even thou--what makes peace possible! But now it is hid from thine eyes.
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
For the time is coming upon thee when thy foes will throw up around thee earthworks and a wall, investing thee and hemming thee in on every side.
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
And they will dash thee to the ground and thy children within thee, and will not leave one stone upon another within thee; because thou hast not recognized the time of thy visitation."
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
Then Jesus entered the Temple and proceeded to drive out the dealers.
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
"It is written," He said, "'And My house shall be the House of Prayer,' but you have made it a robbers' cave."
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
And day after day He taught in the Temple, while the High Priests and the Scribes were devising some means of destroying Him, as were also the leading men of the people.
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
But they could not find any way of doing it, for the people all hung upon His lips.

< Luka 19 >