< Luka 19 >
1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
And, having entered, he was passing through Jericho;
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
and lo! a man, by name called Zacchaeus, and, he, was a chief tax-collector, and [he] was rich.
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
And he was seeking to see Jesus, what sort of man he was, and could not for the multitude, because, in stature, he was, small.
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
And, running forward unto the front, he got up a sycamore-tree, that he might see him; for, by that way, was he about to pass.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
And, as he came up to the place, looking up, Jesus said unto him—Zacchaeus! make haste, and come down; For, to-day, in thy house, I must needs abide.
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
And he made haste, and came down, and received him joyfully.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
And all, when they beheld, began to murmur, saying—With a sinful man, hath he gone in to lodge!
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
But, taking his stand, Zacchaeus said unto the Lord—Lo! the half of my possessions, Lord, unto the destitute, I give; and, if, from anyone, I have taken aught by false accusation, I give back fourfold.
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
And Jesus said unto him—This day, salvation, unto this house, hath come, —for that, he too, is, a son of Abraham;
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
For the Son of Man came, to seek and to save what was lost.
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
And, because they were hearing these things, he added and spake a parable, because of his being near Jerusalem, and their supposing that, instantly, was the kingdom of God to shine forth.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
He said, therefore—A certain man, of noble birth, went into a country far away, to receive for himself a kingdom, and to return.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
And, calling ten servants of his own, he gave unto them ten minas, and said unto them—Do business, till I come.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
But, his citizens, hated him, and sent off an embassy after him, saying—We desire not, this, man, to be made king over us!
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
And it came to pass, when he returned, having received the kingdom, that he bade be called unto him these servants, to whom he had given the silver, that he might take note, what business they had done.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
And the first came near, saying—Lord! thy mina, hath made, ten minas.
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
And he said to him—Well done! good servant. Because, in a very small thing, thou hast been, faithful, have thou authority over, ten cities.
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
And the second came, saying—Thy mina, lord, hath made five minas.
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
And he said, to him also, And, thou, be over five cities.
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
And, the other, came, saying—Lord, lo! thy mina, which I kept lying by in a napkin;
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
For I was afraid of thee, because, a harsh man, thou art, —Thou takest up, what thou layedst not down, and reapest, what thou sowedst not!
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
He saith to him—Out of thy mouth, do I judge thee, O wicked servant! Thou knewest that, I, a harsh man, am, —taking up, what I laid not down, and reaping, what I did not sow;
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
Wherefore, then, didst thou not place my silver upon a [money-changer’s] table, and, I, when I came, with interest might have exacted it?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
And, unto the by-standers, he said—Take, from him, the mina, and give unto him that hath, the ten minas; —
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
And they said to him, Lord! he hath ten minas; —
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
I tell you—Unto everyone that hath, shall be given, whereas, from him that hath not, even what he hath, shall be taken away.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
But, these mine enemies who desired not that I should be made king over them, bring ye here, and slay them outright before me.
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
And, having said these things, he was moving on in front, going up into Jerusalem.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
And it came to pass, as he drew near unto Bethphage, and Bethany, unto the mount which is called the Mount of Olives, he sent off two of his disciples,
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
saying—Go your way unto the opposite village, in which, as ye are entering, ye shall find a colt, bound, whereon, no man, hath, ever sat, —and, having loosed him, bring him.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
And, if any one question you—Wherefore are ye loosing him? thus, shall ye say—His Lord, hath, need.
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
And they who were sent, departing, found as he had said to them.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
And, as they were loosing the colt, his lords said unto them—Why are ye loosing the colt?
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
And, they, said—His Lord, hath, need.
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
And they brought him unto Jesus; and, throwing their mantles over the colt, they seated Jesus thereon.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
And, as he moved along, they were spreading their own mantles in the way.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
And, when he was drawing near, already, unto the descent of the Mount of Olives, one-and-all the throng of the disciples began joyfully to be praising God with a loud voice, concerning all the mighty works which they had seen;
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
saying—Blessed is he that cometh… The king! In the name of the Lord! In heaven, peace! And glory in the highest!
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
And, certain of the Pharisees from the multitude, said unto him—Teacher! rebuke thy disciples.
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
And he answered and said—I tell you—If, these, shall hold their peace, the stones, will cry out.
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
And, when he drew near, beholding the city, he wept over it, saying—
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
If thou hadst got to know, in this day, even thou, the conditions of peace… But, now, are they hid from thine eyes:
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
Because days will have come upon thee, that thine enemies will throw around a rampart against thee, and enclose thee; and hem thee in from every side, —
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
And will level thee with the ground, and thy children within thee, and will not leave, stone on stone, within thee: because thou didst not get to know the season of thy visitation.
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
And, entering into the temple, he began to be casting out them who were selling;
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
saying unto them—It is written, And, my house, shall be, a house of prayer; but, ye, have made, it, a den of robbers.
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
And he was teaching day by day in the temple; but, the High-priests and the Scribes, also the chiefs of the people, were seeking to destroy him, —
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
and could not find what they might do, for, the people, one and all, were hanging upon him, as they hearkened.