< Luka 18 >
1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
And he spoke to them a similitude also, that men should pray at all times, and not become weary.
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
There was a judge in a certain city, who feared not God, and regarded not men.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
And there was a certain widow in that city; and she came to him, and said: Vindicate me against my adversary.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
And he would not, for a long time: but afterwards, he said to himself: Though I fear not God, and regard not men,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
yet, because this widow troubleth me, I will vindicate her; that she may not be always coming and troubling me.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
And our Lord said: Hear what the unjust judge saith.
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
And will not God, much more, vindicate his chosen, who call upon him by day and by night; and have patience with them?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
I tell you, He will vindicate them speedily. Yet the Son of man will come; and will he find faith on the earth?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
And he spake this similitude, against certain persons, who had confidence in themselves that they were righteous, and despised every one.
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Two men went up to the temple to pray; the one a Pharisee, and the other a publican.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
And the Pharisee stood by himself, and prayed thus: God, I thank thee that I have not been like the rest of men, rapacious, oppressive, and adulterous; nor like this publican.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
But I fast twice in a week, and tithe all I possess.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
And the publican stood afar off, and would not even lift his eyes to heaven, but smote upon his breast, and said: God, be merciful to me, a sinner.
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
I say to you, that this man went down to his house justified, rather than the Pharisee. For every one that exalteth himself, will be humbled; and every one that humbleth himself, will be exalted.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
And they brought to him infants, that he might touch them: and his disciples saw them, and rebuked them.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
But Jesus called them, and said to them: Suffer little children to come to me, and forbid them not; for of those that are like them, of such is the kingdom of heaven.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Verily I say to you, That he who shall not receive the kingdom of God, as a little child, will not enter it.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
And one of the chiefs asked him, and said to him: Good Teacher, what shall I do, that I may inherit eternal life? (aiōnios )
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Jesus said to him: Why callest thou me, good? For, there is none good, except one; God.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Thou knowest the commandments: Thou shalt not kill; and thou shalt not commit adultery; and thou shalt not steal; and thou shalt not testify a false testimony; honor thy father and thy mother.
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
He said to him: All these have I kept, from my childhood.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
And when Jesus heard these words, he said to him: One thing is lacking to thee: go, sell all that thou hast, and give to the poor; and thou wilt have a treasure in heaven; and come after me.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
And he, when he heard these words, was dejected; for he was very rich.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
And when Jesus saw that he was dejected, he said: How difficult it is, for those that have wealth to enter into the kingdom of God!
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
It is easier for a camel to enter the eye of a needle, than a rich man the kingdom of God.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
They who heard it, said to him: Who then can have life?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
And Jesus said: Those things which, with men, cannot be, with God, can be.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
Simon Cephas said to him: Lo, we have left every thing, and come after thee.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
Jesus said to him: Verily I say to you: There is no man, who hath left houses, or parents, or brothers, or wife, or children, for the sake of the kingdom of God,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn , aiōnios )
that shall not receive manifold in the present time, and, in the coming world, eternal life. (aiōn , aiōnios )
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
And Jesus took his twelve, and said to them: Behold, we are going up to Jerusalem; and all the things written in the prophets, concerning the Son of man, will be fulfilled.
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
For he will be delivered over to the Gentiles; and they will mock him, and spit in his face;
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
and will scourge him, and will treat him with ignominy, and will kill him; and, the third day, he will arise.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
But not one of these things, did they understand; but this subject was hidden from them, and they knew not the things told to them.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
And as they came near to Jericho, a blind man was sitting by the side of the way, begging.
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
And he heard the noise of the multitude that passed, and inquired what it was.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
They say to him: Jesus the Nazarean is passing by.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And he called out, and said: Jesus, Son of David, have mercy on me.
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And they that went before Jesus rebuked him, that he might be silent. But he cried out the more, Son of David, have mercy on me.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
And Jesus stood, and commanded him to be called to him. And when he came to him, he asked him,
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
and said to him: What wilt thou, that I do for thee? And he said: My Lord, that I may see.
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said to him: See thou; thy faith hath vivified thee.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
And immediately he saw. And he followed after him, and glorified God. And all the people who beheld, gave glory to God.