< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
And he was speaking a parable unto them, as to its being needful for them always to pray, and not be faint-hearted;
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
saying—A certain judge, there was in a certain city, —having, for God, no reverence, and, for man, no respect.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
And, a widow, there was, in that city; and she kept coming unto him, saying—Vindicate me from mine adversary!
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
And he was unwilling for a time; but, after these things, he said within himself—Although, neither God, I reverence, nor man, I respect,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
Yet, if only because this widow annoyeth me, I will vindicate her, —lest, persistently coming, she wholly wear me out.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
And the Lord said—Hear ye what, the unrighteous judge saith; —
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
And shall, God, in any wise not execute the vindication of his chosen ones, who are crying out to him day and night, although he beareth long with regard to them?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
I tell you—He will execute their vindication, quickly! nevertheless, though, the Son of Man, do come, will he, after all, find the faith on the earth?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
And he spake, even unto certain who were confident in themselves that they were righteous, and were despising the rest, this parable: —
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Two men, went up into the temple to pray, one, a Pharisee, and, the other, a tax-collector.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
The Pharisee, taking his stand, these things unto himself was praying: O God! I thank thee, that I am not like the rest of men, —extortioners, unjust, adulterers, or, even as this tax-collector;
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
I fast twice in the week, I give a tenth of whatsoever things I gain!
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
But, the tax-collector, afar off, standing, —would not so much as lift up, his eyes, unto heaven, but kept smiting his own breast saying—O God! be propitiated unto me, the sinner!
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
I tell you—This one went down justified, unto his house, rather than that one; because, every one who exalteth himself, shall be abased, but, he that abaseth himself, shall be exalted?
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
And they were bringing unto him, even the babes, that he might touch, them; but the disciples, seeing it, began to rebuke them.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
But, Jesus, called them near, saying—Suffer, the children, to be coming unto me, and do not hinder them; for, of such, is the kingdom of God.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Verily I say unto you—Whosoever shall not welcome the kingdom of God, as a child, in nowise shall enter thereinto.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
And a certain, ruler, questioned him, saying—Good Teacher! by doing what, shall I inherit life age-abiding? (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
But Jesus said to him—Why, callest thou me, good? None, is good, save one—God.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
The commandments, thou knowest: —Do not commit adultery, Do not commit murder, Do not steal, Do not bear false witness, —Honour thy father and mother,
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
And, he, said—All these things, have I kept from my youth.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
And Jesus, hearing, said unto him—Yet one thing, unto thee, is lacking: Whatsoever thou hast, sell, and distribute unto the destitute, —and thou shalt have treasure in [the] heavens; and come! be following me.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
But, he, hearing these things, became, encompassed with grief; for he was rich exceedingly.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
And Jesus, beholding him, said—With what difficulty, shall, they who have money, enter, into the kingdom of God.
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
For it is, easier, for a camel, to enter, through the eye of a needle, than for, a rich man, to enter, into the kingdom of God.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
And they who heard said—Who, then, can be saved?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
And, he, said—The things impossible with men, are, possible with God.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
And Peter said—Lo! we, have left our own possessions, and followed thee!
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
And, he, said unto them—Verily, I say unto you—No one, is there, who hath left—house, or wife, or brethren, or parents, or children, —for the sake of the kingdom of God;
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
who shall in anywise not receive manifold in this season, and, in the age that is coming, life age-abiding. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
And, taking aside the twelve, he said unto them—Lo! we are going up unto Jerusalem, and all the things will be finished, which have been written through means of the prophets, respecting the Son of Man;
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
For he will be delivered up unto the nations, and be mocked, and insulted, and spit upon, —
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
and, having scourged him, they will slay him, and, on the third day, will, he, arise.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
And, they, not one of these things, understood, and this saying was hidden from them, and the could not comprehend the things spoken.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
And it came to pass, as he was drawing near unto Jericho, a certain blind man, was sitting beside the road, begging.
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
And. hearkening unto a multitude moving along, he enquired, what this, might be.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
And they told him—Jesus of Nazareth, is passing by!
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And he cried aloud, saying—Jesus, son of David! have mercy upon me!
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And, they that were going before, began to rebuke him, that he might hold his peace. But, he, by so much the more, was crying out—O Son of David! have mercy upon me!
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
And, standing still, Jesus commanded him to be led unto him; and, when he had drawn near, he questioned him—
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
What desirest thou, I should do unto thee? And, he, said—Lord! …that I may recover sight!
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And, Jesus, said unto him—Recover sight! Thy faith, hath saved thee.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
And, instantly, he recovered sight, and began to follow him, glorifying God. And, all the people, beholding, gave praise unto God.

< Luka 18 >