< Luka 18 >
1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
And he spoke a parable to them to show that they ought to pray always, and not be faint-hearted:
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
saying, There was in a certain city a judge, who feared not God, nor regarded man.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
And there was a widow in that city; and she kept coming to him, saying, Avenge me of my adversary!
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
And he would not for some time. But afterward he said within himself, Though I neither fear God, nor regard man,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
yet, because this widow troubleth me, I will avenge her; lest by coming for ever she weary me out.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
And the Lord said, Hear what the unjust judge saith.
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
And will not God avenge his chosen, who cry to him day and night, though he be slow to punish in their behalf?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
I tell you that he will avenge them speedily. But yet, when the Son of man cometh, will he find faith on the earth?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
And to some who trusted in themselves that they were righteous, and despised all others, he spoke this parable:
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Two men went up into the temple to pray; the one a Pharisee, and the other a publican.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
The Pharisee stood and prayed by himself thus: O God, I thank thee that I am not as the rest of men, extortioners, unjust, adulterers, or even as this publican.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
I fast twice in the week; I give tithes of all that I gain.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
But the publican, standing afar off, would not even lift up his eyes to heaven; but smote his breast, saying, O God, be merciful to me a sinner!
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
I tell you, this man went down to his house justified rather than the other; for every one that exalteth himself will be humbled; but he that humbleth himself will be exalted.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
And they brought to him infants also, that he might touch them; and the disciples, on seeing it, rebuked them.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
But Jesus called them to him, saying, Suffer the little children to come to me, and forbid them not; for to such belongeth the kingdom of God.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Truly do I say to you, Whoever shall not receive the kingdom of God as a little child, will not enter therein.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
And a certain ruler asked him, saying, Good teacher, what shall I do to inherit everlasting life? (aiōnios )
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
And Jesus said to him, Why dost thou call me good? None is good but one, that is, God.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Thou knowest the commandments: “Do not commit adultery; Do not kill; Do not steal; Do not bear false witness; Honor thy father and thy mother.”
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
And he said, All these have I kept from my youth.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
And Jesus hearing this said to him, One thing thou still lackest: sell all that thou hast, and distribute to the poor, and thou shalt have treasure in heaven; and come, follow me.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
But when he heard this, he became very sorrowful; for he was very rich.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
And Jesus seeing him said, How hardly do they that have riches enter the kingdom of God!
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
It is easier for a camel to go through the eye of a needle, than for a rich man to enter the kingdom of God.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
And those who heard this said, Who then can be saved?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
But he said, What is impossible with men is possible with God.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
Then Peter said, Lo! we left what we had, and followed thee.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
And he said to them, Truly do I say to you, There is no one that hath left house, or wife, or brothers, or parents, or children, for the sake of the kingdom of God,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn , aiōnios )
who will not receive many fold more in the present time, and in the world to come everlasting life. (aiōn , aiōnios )
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
And taking the twelve aside, he said to them, Behold, we are going up to Jerusalem, and all that hath been written by the prophets concerning the Son of man will be accomplished.
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
For he will be delivered up to the gentiles, and will be mocked, and insulted, and spit upon;
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
and they will scourge him, and put him to death; and the third day he will rise again.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
And they understood none of these things; and the meaning of these words was hidden from them, and they did not comprehend what was said.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
And it came to pass, as he drew near to Jericho, that a certain blind man was sitting by the wayside begging.
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
And hearing a multitude passing by, he asked what this meant.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
And they told him that Jesus of Nazareth was passing by.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And he cried out, saying, Jesus, Son of David, have pity on me!
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And they who went before sharply bade him hold his peace. But he cried out the more, Son of David, have pity on me!
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
And Jesus stopped, and ordered him to be brought to him. And when he had come near, he asked him,
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
What dost thou wish me to do for thee? And he said, Lord, to restore my sight.
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said to him, Receive thy sight; thy faith hath saved thee.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
And immediately he received his sight, and followed him, giving glory to God; and all the people on seeing it gave praise to God.