< Luka 17 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
Or il dit à ses disciples: Il est impossible qu’il n’arrive pas des scandales; mais malheur à celui par qui ils arrivent!
2 Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
Mieux lui vaudrait qu’on lui mette au cou une meule d’âne, et qu’il soit jeté dans la mer, que de scandaliser un de ces petits.
3 Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
Prenez garde à vous-mêmes. Si ton frère pèche, reprends-le, et s’il se repent, pardonne-lui;
4 In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
et si sept fois le jour il pèche contre toi, et que sept fois il retourne à toi, disant: Je me repens, tu lui pardonneras.
5 Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
Et les apôtres dirent au Seigneur: Augmente-nous la foi.
6 Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
Et le Seigneur dit: Si vous avez de la foi comme un grain de moutarde, vous diriez à ce mûrier: Déracine-toi, et plante-toi dans la mer; et il vous obéirait.
7 “In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
Mais qui est celui d’entre vous, qui, ayant un esclave labourant ou paissant [le bétail], quand il revient des champs, dise: Avance-toi de suite et mets-toi à table?
8 Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
Ne lui dira-t-il pas au contraire: Apprête-moi à souper et ceins-toi, et me sers jusqu’à ce que j’aie mangé et bu; et après cela, tu mangeras et tu boiras, toi?
9 Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
Est-il obligé à l’esclave de ce qu’il a fait ce qui avait été commandé? Je ne le pense pas.
10 Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
Ainsi, vous aussi, quand vous aurez fait toutes les choses qui vous ont été commandées, dites: Nous sommes des esclaves inutiles; ce que nous étions obligés de faire, nous l’avons fait.
11 Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
Et il arriva qu’en allant à Jérusalem, il traversait la Samarie et la Galilée.
12 Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
Et comme il entrait dans un village, dix hommes lépreux le rencontrèrent; et ils s’arrêtèrent de loin;
13 suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
et ils élevèrent la voix, disant: Jésus, maître, aie pitié de nous!
14 Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
Et les voyant, il leur dit: Allez, montrez-vous aux sacrificateurs. Et il arriva qu’en s’en allant ils furent rendus nets.
15 Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
Or l’un d’entre eux, voyant qu’il était guéri, revint sur ses pas, glorifiant Dieu à haute voix;
16 Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
et il se jeta sur sa face aux pieds de Jésus, lui rendant grâces. Et c’était un Samaritain.
17 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
Et Jésus, répondant, dit: Les dix n’ont-ils pas été rendus nets? Et les neuf, où sont-ils?
18 Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
Il ne s’en est point trouvé qui soient revenus pour donner gloire à Dieu, si ce n’est cet étranger.
19 Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Et il lui dit: Lève-toi, et t’en va; ta foi t’a guéri.
20 Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
Or, étant interrogé par les pharisiens quand viendrait le royaume de Dieu, il leur répondit et dit: Le royaume de Dieu ne vient pas de manière à attirer l’attention;
21 Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
et on ne dira pas: Voici, il est ici; ou, voilà, il est là. Car voici, le royaume de Dieu est au milieu de vous.
22 Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
Et il dit aux disciples: Les jours viendront où vous désirerez de voir l’un des jours du fils de l’homme, et vous ne le verrez pas.
23 Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
Et on vous dira: Voici, il est ici; ou, voilà, il est là. N’y allez pas, et ne les suivez pas.
24 Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
Car comme l’éclair qui brille, luit de l’un des côtés de dessous le ciel jusqu’à l’autre côté de dessous le ciel, ainsi sera le fils de l’homme en son jour.
25 Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
Mais auparavant il faut qu’il souffre beaucoup, et qu’il soit rejeté par cette génération.
26 “Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
Et comme il arriva aux jours de Noé, ainsi en sera-t-il aux jours du fils de l’homme aussi:
27 Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
on mangeait, on buvait, on se mariait, on donnait en mariage, jusqu’au jour où Noé entra dans l’arche; et le déluge vint, et les fit tous périr.
28 “Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
De même aussi, comme il arriva aux jours de Lot: on mangeait, on buvait, on achetait, on vendait, on plantait, on bâtissait;
29 Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
mais, au jour où Lot sortit de Sodome, il plut du feu et du soufre du ciel, qui les fit tous périr;
30 “Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
il en sera de même au jour où le fils de l’homme sera manifesté.
31 A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
En ce jour-là, que celui qui sera sur le toit et qui aura ses effets dans la maison, ne descende pas pour les emporter; et pareillement que celui qui sera aux champs ne retourne pas en arrière.
32 Ku tuna fa da matar Lot!
Souvenez-vous de la femme de Lot.
33 Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
Quiconque cherchera à sauver sa vie, la perdra; et quiconque la perdra, la gagnera.
34 Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
Je vous dis qu’en cette nuit-là deux seront sur un même lit, l’un sera pris et l’autre laissé;
35 Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
deux femmes moudront ensemble, l’une sera prise et l’autre laissée;
[deux seront aux champs, l’un sera pris et l’autre laissé].
37 Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”
Et répondant, ils lui disent: Où, Seigneur? Et il leur dit: Là où est le corps, là aussi s’assembleront les aigles.

< Luka 17 >