< Luka 17 >
1 Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
Jesus said to his disciples, ‘It is inevitable that there should be temptations but sorrow awaits the person who does the tempting!
2 Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
It would be better for them if they had been flung into the sea with a millstone round their neck, rather than that they should cause even one of these little ones to stumble.
3 Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
Be on your guard! If your brother or sister does wrong, rebuke them; but if they repent, forgive them.
4 In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
Even if they wrong you seven times a day, but turns to you every time and says “I am sorry,” you must forgive them.’
5 Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
‘Give us more faith,’ said the apostles to the Master;
6 Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
but the Master said, ‘If your faith were only like a mustard seed, you could say to this mulberry tree “Be uprooted and planted in the sea,” and it would obey you.
7 “In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
Which of you, if he had a servant ploughing, or tending the sheep, would say to him, when he came in from the fields, “Come at once and take your place at the table,”
8 Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
Instead of saying “Prepare my dinner, and then make yourself ready and serve me while I am eating and drinking, and after that you will eat and drink yourself”?
9 Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
Does he feel grateful to his servant for doing what he is told?
10 Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
And so with you – when you have done all that you have been told, still say “We are but useless servants; we have done no more than we ought to have done.”’
11 Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
On the way to Jerusalem Jesus passed between Samaria and Galilee.
12 Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
As he was entering a village, ten lepers met him.
13 suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
Standing still, some distance off, they called out loudly, ‘Jesus! Sir! Pity us!’
14 Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
When Jesus saw them, he said, ‘Go and show yourselves to the priest.’ And, as they were on their way, they were made clean.
15 Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
One of them, finding he was cured, came back, praising God loudly,
16 Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
and threw himself on his face at Jesus’ feet, thanking him for what he had done; and this man was a Samaritan.
17 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
‘Were not all the ten made clean? exclaimed Jesus. But the nine – where are they?
18 Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
Were there none to come back and praise God except this foreigner?
19 Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Get up,’ he said to him, ‘and go on your way. Your faith has delivered you.’
20 Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
Being once asked by the Pharisees when the kingdom of God was to come, Jesus answered, ‘The kingdom of God does not come in a way that can be seen,
21 Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
nor will people say “Look, here it is!” or “There it is!”; for the kingdom of God is within you!
22 Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
The day will come,’ he said to his disciples, ‘when you will long to see but one of the days of the Son of Man, and will not see it.
23 Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
People will say to you “There he is!” Or “Here he is!” Do not go and follow them.
24 Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
For, just as lightning will lighten and flare from one side of the heavens to the other, so will it be with the Son of Man.
25 Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
But first he must undergo much suffering, and he must be rejected by the present generation.
26 “Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
As it was in the days of Noah, so will it be again in the days of the Son of Man.
27 Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
They were eating and drinking and marrying and being married, up to the very day on which Noah entered the ark, and then the flood came and destroyed them all.
28 “Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
So, too, in the days of Lot. People were eating, drinking, buying, selling, planting, building;
29 Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
but, on the very day on which Lot came out of Sodom, it rained fire and sulphur from the skies and destroyed them all.
30 “Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
It will be the same on the day on which the Son of Man reveals himself.
31 A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
On that day, if a person is on their house-top and their goods in the house, they must not go down to get them; nor again must one who is on the farm turn back.
32 Ku tuna fa da matar Lot!
Remember Lot’s wife.
33 Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
Whoever is eager to get the most out of their life will lose it; but whoever will lose it will preserve it.
34 Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
On that night, I tell you, of two people on the same bed, one will be taken and the other left;
35 Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
of two women grinding grain together, one will be taken and the other left.’
37 Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”
‘Where will it be, Master?’ asked the disciples. ‘Where there is a body,’ said Jesus, ‘there will the vultures flock.’