< Luka 17 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
And he said to his disciples, It is impossible for the stumbling-blocks not to come, but woe to him through whom they come!
2 Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
It is better for him if a donkey-powered millstone were hanged about his neck, and he were thrown into the sea, than that he should cause one of these little ones to stumble.
3 Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
Take heed to yourselves. And if thy brother should sin against thee, rebuke him, and if he repents, forgive him.
4 In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
And if he should sin against thee seven times in the day, and seven times in the day turn back, saying, I repent, thou will forgive him.
5 Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
And the apostles said to the Lord, Increase faith for us.
6 Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
And the Lord said, If ye have faith as a grain of mustard plant, ye would say to this sycamine tree, Be thou uprooted and be planted in the sea, and it would have obeyed you.
7 “In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
But which of you having a bondman plowing or feeding livestock, who, when he comes in from the field, will straightaway say, After coming near, sit down?
8 Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
Will he not rather say to him, Prepare what I may dine, and having gird thyself, serve me until I eat and drink, and after these things thou will eat and drink?
9 Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
Does he have a favor for that bondman because he did the things that were commanded? I think not.
10 Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
Thus ye also, when ye did all the things that were commanded you, say, We are unprofitable bondmen, because we have done what we are obligated to do.
11 Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
And it came to pass as he went to Jerusalem, that he was passing through the middle of Samaria and Galilee.
12 Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
And as he entered into a certain village, ten leprous men who stood from afar met him.
13 suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
And they raised a voice, saying, Jesus, Master, be merciful to us.
14 Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
And when he saw them, he said to them, After departing, display yourselves to the priests. And it came to pass, during their going they were cleansed.
15 Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
And one of them, when he saw that he was healed, turned back with a great voice glorifying God.
16 Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
And he fell upon his face beside his feet giving him thanks. And he was a Samaritan.
17 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
And having answered, Jesus said, Were not the ten cleansed? But where are the nine?
18 Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
Were there none found who returned to give glory to God, except this foreigner?
19 Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And he said to him, After rising, go. Thy faith has healed thee.
20 Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
And questioned by the Pharisees when the kingdom of God comes, he answered them and said, The kingdom of God does not come with observation,
21 Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
nor will they say, Lo, here! or, Lo, there! For behold, the kingdom of God is inside of you.
22 Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
And he said to the disciples, The days will come when ye will long to see one of the days of the Son of man, and ye will not see it.
23 Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
And they will say to you, Lo, here! Lo, there! Do not depart, nor pursue.
24 Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
For just as the lightning, its flashing from under the sky to under the sky, illuminates, so will the Son of man be in his day.
25 Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
But first it is necessary for him to suffer many things and be rejected from this generation.
26 “Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
And just as it happened in the days of Noah, so also it will be in the days of the Son of man.
27 Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
They ate, they drank, they married, they were given in marriage, until the day that Noah entered into the ark, and the flood came and destroyed them all.
28 “Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
And likewise as it happened in the days of Lot. They ate, they drank, they bought, they sold, they planted, they built.
29 Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
But in that day Lot went out from Sodom he rained fire and brimstone from the sky, and destroyed them all.
30 “Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
It will be according to these things in that day the Son of man is revealed.
31 A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
In that day, he who will be on the housetop, and his vessels in the house, let him not go down to take them up. And let him who is in the field likewise not return for the things behind.
32 Ku tuna fa da matar Lot!
Remember Lot's wife.
33 Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
Whoever will seek to save his life will lose it, and whoever will lose it will keep it alive.
34 Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
I say to you, in that night there will be two in one bed. The one man will be taken, and the other man will be left.
35 Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
Two will be grinding together. The one woman will be taken, and the other woman will be left.
This verse is not in the majority of the Greek manuscripts.
37 Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”
And having answered, they say to him, Where, Lord? And he said to them, Where the body is, there the vultures will be gathered together.

< Luka 17 >