< Luka 16 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
He seide also to hise disciplis, Ther was a riche man, that hadde a baili; and this was defamed to him, as he hadde wastid his goodis.
2 Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
And he clepide hym, and seide to hym, What here Y this thing of thee? yelde reckynyng of thi baili, for thou miyte not now be baili.
3 “Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
And the baili seide with ynne him silf, What schal Y do, for my lord takith awei fro me the baili? delfe mai Y not, I schame to begge.
4 Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
Y woot what Y schal do, that whanne Y am remeued fro the baili, thei resseyue me in to her hous.
5 “Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
Therfor whanne alle the dettours of his lord weren clepid togider, he seide to the firste, Hou myche owist thou to my lord?
6 “Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
And he seide, An hundrid barelis of oyle. And he seide to hym, Take thi caucioun, and sitte soone, and write fifti.
7 “Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
Aftirward he seide to another, And hou myche owist thou? Which answerde, An hundrid coris of whete. And he seide to hym, Take thi lettris, and write foure scoore.
8 “Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
And the lord preiside the baili of wickydnesse, for he hadde do prudentli; for the sones of this world ben more prudent in her generacioun than the sones of liyt. (aiōn g165)
9 Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
And Y seie to you, make ye to you freendis of the ritchesse of wickidnesse, that whanne ye schulen fayle, thei resseyue you in to euerlastynge tabernaclis. (aiōnios g166)
10 “Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
He that is trewe in the leeste thing, is trewe also in the more; and he that is wickid in a litil thing, is wickid also in the more.
11 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
Therfor if ye weren not trewe in the wickid thing of ritchesse, who schal bitake to you that that is verry?
12 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
And if ye weren not trewe in othere mennus thing, who schal yyue to you that that is youre?
13 “Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
No seruaunt may serue to twei lordis; for ether he schal hate `the toon, and loue the tothir; ethir he schal drawe to `the toon, and schal dispise the tothir. Ye moun not serue to God and to ritchesse.
14 Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
But the Farisees, that weren coueytous, herden alle these thingis, and thei scorneden hym.
15 Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
And he seide to hem, Ye it ben, that iustifien you bifor men; but God hath knowun youre hertis, for that that is hiy to men, is abhomynacioun bifor God.
16 “An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
The lawe and prophetis til to Joon; fro that tyme the rewme of God is euangelisid, and ech man doith violence in to it.
17 Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
Forsothe it is liyter heuene and erthe to passe, than that o titil falle fro the lawe.
18 “Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
Euery man that forsakith his wijf, and weddith an other, doith letcherie; and he that weddith the wijf forsakun of the hosebonde, doith auowtrie.
19 “An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
There was a riche man, and was clothid in purpur, and whit silk, and eete euery dai schynyngli.
20 A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
And there was a begger, Lazarus bi name, that lai at his yate ful of bilis,
21 Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
and coueitide to be fulfillid of the crummes, that fellen doun fro the riche mannus boord, and no man yaf to hym; but houndis camen, and lickiden hise bilis.
22 “Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
And it was don, that the begger diede, and was borun of aungels in to Abrahams bosum. And the riche man was deed also,
23 A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
and was biried in helle. And he reiside hise iyen, whanne he was in turmentis, and say Abraham afer, and Lazarus in his bosum. (Hadēs g86)
24 Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
And he criede, and seide, Fadir Abraham, haue merci on me, and sende Lazarus, that he dippe the ende of his fyngur in watir, to kele my tunge; for Y am turmentid in this flawme.
25 “Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
And Abraham seide to hym, Sone, haue mynde, for thou hast resseyued good thingis in thi lijf, and Lazarus also yuel thingis; but he is now coumfortid, and thou art turmentid.
26 Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
And in alle these thingis a greet derk place is stablischid betwixe vs and you; that thei that wolen fro hennus passe to you, moun not, nethir fro thennus passe ouer hidur.
27 “Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
And he seide, Thanne Y preie thee, fadir, that thou sende hym in to the hous of my fadir.
28 gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
For Y haue fyue britheren, that he witnesse to hem, lest also thei come in to this place of turmentis.
29 “Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
And Abraham seide to him, Thei han Moyses and the prophetis; here thei hem.
30 “Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
And he seide, Nay, fadir Abraham, but if ony of deed men go to hem, thei schulen do penaunce.
31 “Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”
And he seide to hym, If thei heren not Moises and prophetis, nethir if ony of deed men rise ayen, thei schulen bileue to hym.

< Luka 16 >