< Luka 14 >
1 Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
Ühel hingamispäeval läks Jeesus einestama ühe variseride ülema koju, kus nad teda hoolikalt jälgisid.
2 A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
Seal oli üks mees, kelle käed ja jalad olid tursunud.
3 Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
Niisiis küsis Jeesus vaimuliku seaduse tundjatelt ja variseridelt: „Kas seadus lubab hingamispäeval terveks teha või mitte?“
4 Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
Aga nad vaikisid. Jeesus puudutas meest, tegi ta terveks ja saatis oma teed.
5 Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
Siis ütles Jeesus neile: „Kui teie poeg või härg kukuks juhtumisi hingamispäeval kaevu, kas te ei tõmbaks teda siis kohe välja?“
Nad ei suutnud vastust anda.
7 Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
Nii rääkis ta loo külalistele, sest ta märkas, kuidas nad olid valinud istumiseks aukohti.
8 “In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
„Kui sind on kutsutud pulmapeole, siis ära istu aukohale, sest võib-olla on kutsutud keegi, kes on sinust tähtsam, “alustas ta.
9 In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
„Sinu võõrustaja, kes on teid mõlemat kutsunud, tuleb ja ütleb sulle: „Anna oma koht sellele inimesele.“Siis pead sa piinlikkust tundes minema kohale, mis on järele jäänud.
10 Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
Kui sind on kutsutud, siis vali hoopis kõige tagasihoidlikum koht, nii et kui su võõrustaja tuleb sisse, ütleb ta sulle: „Mu sõber, palun mine paremale kohale.“Siis oleksid sa austatud kõigi külaliste ees, kes koos sinuga istuvad.
11 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Sest neid, kes end ise ülendavad, alandatakse, ja neid, kes end ise alandavad, ülendatakse.“
12 Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
Seejärel ütles ta mehele, kes oli teda kutsunud: „Kui sa korraldad lõuna- või õhtusöögi, siis ära kutsu oma sõpru, vendi, sugulasi või rikkaid naabreid, et nad võiksid omakorda sind kutsuda ja nii saaksid sa tasu.
13 Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
Kui sa korraldad pidusöögi, kutsu hoopis vaeseid, vigaseid, sante ja pimedaid,
14 Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
ning sa saad õnnistatud, sest neil ei ole sulle millegagi tasuda, ja sa saad tasu heade ülestõusmisel.“
15 Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
Kui üks neist, kes koos Jeesusega lauas sõi, kuulis seda, ütles ta Jeesusele: „Kui imetore on neil, kes söövad peolauas Jumala riigis!“
16 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
„Elas kord üks mees, kes valmistas suure pidusöögi ja kutsus palju külalisi, “vastas Jeesus.
17 Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
„Kui saabus söögiaeg, saatis ta oma sulased kõigile kutsutuile ütlema: „Tulge, sest pidusöök on valmis!“
18 “Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
Aga nad kõik hakkasid vabandusi esitama. Esimene ütles: „Ostsin just põllu ja pean minema seda vaatama. Palun vabanda mind.“
19 “Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
Teine ütles: „Ostsin just viis paari härgi ja ma pean minema neid katsetama. Palun vabanda mind.“Kolmas ütles:
20 “Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
„Võtsin just naise, nii et ma ei saa tulla.“
21 “Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
Sulane läks tagasi ja rääkis oma isandale, mida nad olid öelnud. Majaisand sai pahaseks ja ütles oma sulasele: „Mine ruttu välja linna tänavatele ja kõrvaltänavatele ning too sisse vaesed, vigased, pimedad ja sandid.“
22 “Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
Siis ütles sulane: „Isand, ma tegin nii, nagu sa käskisid, aga ikka on veel tühje kohti.“
23 “Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
Nii käskis isand sulast: „Mine välja maanteedele ja külatänavatele ning sunni inimesi tulema. Ma tahan, et koda saaks täis.
24 Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
Ma ütlen sulle, ükski neist kutsututest ei saa mu pidusööki maitsta.““
25 Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
Jeesusega käis kaasas suur rahvahulk. Ta pöördus ja ütles neile:
26 “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
„Kui te tahate mind järgida, kuid ei vihka oma isa ja ema, naist ja lapsi, vendi ja õdesid − koguni oma elu −, ei saa te mu jüngrid olla.
27 Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
Kui te ei võta oma risti ega järgne mulle, ei saa te mu jüngrid olla.
28 “In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
Kui kavatsete torni ehitada, kas ei arvuta te kõigepealt, kui palju see maksma läheb, ega vaata, kas teil on piisavalt raha selle lõpetamiseks?
29 Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
Kui te pärast vundamendi rajamist ei suuda seda valmis teha, siis naeraksid kõik, kes teid näevad, ja ütleksid:
30 yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
„Vaadake teda: ta alustas ehitamist, kuid ei suutnud lõpetada.“
31 “Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
Missugune kuningas läheb teise kuningaga sõtta, ilma et istuks enne koos nõuandjatega maha ega arvutaks, kas tema ja ta kümme tuhat meest suudavad võita tema vastu marssivad kakskümmend tuhat?
32 In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
Kui ta ei suuda, saadab ta esindajad rahu paluma siis, kui teine kuningas on veel väga kaugel.
33 Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
Samamoodi on igaühega teist: kes ei loobu kõigest, ei saa minu jünger olla.
34 “Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
Sool on hea, aga kui see kaotab oma maitse, kuidas saab selle taas soolaseks muuta?
35 Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Sellest pole kasu mulla ega väetisena – te viskate selle lihtsalt välja. Kellel kõrvad on, see kuulaku!“