< Luka 14 >

1 Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
And it came to pass, when he had come into the house of one of the chief men of the Pharisees on the sabbath to eat bread, that they were watching him.
2 A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
And lo! there was a certain man before him, who had the dropsy.
3 Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
And Jesus answering spoke to the lawyers and Pharisees, saying, Is it lawful to cure on the sabbath, or not?
4 Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
But they were silent. And taking hold of him, he cured him, and sent him away.
5 Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
And he answered them and said, Who is there of you, who, if his son or his ox fall into a pit, will not immediately pull him out on the sabbath-day?
6 Suka rasa abin faɗi.
And they could make no answer to this.
7 Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
And he spoke a parable to those who were invited, when he observed how they chose out the highest places at the table, saying to them,
8 “In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
When thou art invited by any one to a wedding, do not take the highest place, lest one more honorable than thou may have been invited by him;
9 In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
and he who invited thee and him come and say to thee, Give place to this man; and then thou wilt begin with shame to take the lowest place.
10 Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
But when thou art invited, go and recline in the lowest place, that when he who invited thee cometh, he may say to thee, Friend, go up higher. Then wilt thou have honor in the presence of all who are at table with thee.
11 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
For every one that exalteth himself will be humbled; and he that humbleth himself will be exalted.
12 Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
And he said also to him who invited him, When thou makest a dinner or a supper, do not invite thy friends, nor thy brothers, nor thy kinsmen, nor rich neighbors; lest they too invite thee in return, and a recompense be made thee.
13 Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
But when thou makest a feast, call the poor, the maimed, the lame, the blind;
14 Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
and thou shalt be blessed, because they cannot recompense thee; but thou shalt be recompensed at the resurrection of the righteous.
15 Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
And one of those who were at table with him, hearing this, said to him, Blessed is he who shall eat bread in the kingdom of God.
16 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
And he said to him, A certain man made a great supper, and invited many.
17 Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
And at the hour of supper he sent his servant to say to those who had been invited, Come, for things are now ready.
18 “Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
And all with one accord began to excuse themselves. The first said to him, I have bought a piece of land, and must needs go out and see it; I pray that I may be excused.
19 “Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
And another said, I have bought five yoke of oxen, and am going out to try them; I pray that I may be excused.
20 “Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
And another said, I have married a wife, and therefore I cannot come.
21 “Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
And the servant came, and reported these things to his lord. Then the master of the house, being angry, said to his servant, Go out quickly into the streets and lanes of the city, and bring in hither the poor, and the maimed, the blind, and the lame.
22 “Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
And the servant said, Lord, what thou didst command hath been done, and yet there is room.
23 “Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
And the lord said to the servant, Go out into the highways and hedges, and constrain them to come in, that my house may be filled.
24 Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
For I say to you, that none of those men who were invited shall taste of my supper.
25 Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
And great multitudes were going with him; and he turned and said to them,
26 “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
If any one cometh to me, and hateth not his father and mother and wife and children and brothers and sisters, yea, and his own life also, he cannot be my disciple.
27 Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
Whoever doth not bear his own cross and follow me, cannot be my disciple.
28 “In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
For which of you, intending to build a tower, doth not sit down first and count the cost, whether he hath the means to finish it?
29 Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
lest haply when he hath laid a foundation, and is not able to finish, all that behold begin to make sport of him,
30 yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
saying, This man began to build, and was not able to finish.
31 “Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
Or what king, setting out to give battle to another king, will not first sit down and consider whether he be able with ten thousand to meet him that cometh against him with twenty thousand?
32 In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
Else, while the other is yet a great way off, he sendeth an embassy, and asketh conditions of peace.
33 Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
So likewise, whoever of you doth not forsake all that he hath, cannot be my disciple.
34 “Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
Salt then is good; but if the salt itself have lost its savor, wherewith shall it be seasoned?
35 Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
It is fit neither for the land, nor for the dunghill; men cast it out. He that hath ears, let him hear.

< Luka 14 >