< Luka 14 >
1 Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
And it came to pass, on His going into the house of a certain one of the chiefs of the Pharisees, on a Sabbath, to eat bread, that they were watching Him,
2 A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
and behold, there was a certain dropsical man before Him;
3 Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
and Jesus answering spoke to the lawyers and Pharisees, saying, “Is it lawful to heal on the Sabbath?”
4 Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
And they were silent, and having taken hold of [him], He healed him, and let [him] go;
5 Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
and answering them He said, “Of which of you will a donkey or ox fall into a pit, and he will not immediately draw it up on the Sabbath day?”
And they were not able to answer Him again to these things.
7 Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
And He spoke an allegory to those called, marking how they were choosing out the first couches, saying to them,
8 “In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
“When you may be called by anyone to wedding feasts, you may not recline on the first couch, lest [one] more honorable than you may have been called by him,
9 In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
and he who called you and him having come will say to you, Give to this one [your] place, and then you may begin to occupy the last place with shame.
10 Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
But when you may be called, having gone on, recline in the last place, that when he who called you may come, he may say to you, Friend, come up higher; then you will have glory before those dining with you;
11 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
because everyone who is exalting himself will be humbled, and he who is humbling himself will be exalted.”
12 Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
And He also said to him who called Him, “When you may make an early meal or a dinner, do not be calling your friends, nor your brothers, nor your relatives, nor rich neighbors, lest they may also call you again, and a repayment may come to you;
13 Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
but when you may make a feast, be calling poor, maimed, lame, blind,
14 Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
and you will be blessed, because they have nothing to repay you, for it will be repaid to you in the resurrection of the righteous.”
15 Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
And one of those dining with Him, having heard these things, said to Him, “Blessed [is] he who will eat bread in the Kingdom of God”;
16 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
and He said to him, “A certain man made a great dinner, and called many,
17 Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
and he sent his servant at the hour of the dinner to say to those having been called, Be coming, because now all things are ready.
18 “Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
And all began with one [voice] to excuse themselves. The first said to him, I bought a field, and I have need to go forth and see it; I beg of you, have me excused.
19 “Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
And another said, I bought five yoke of oxen, and I go on to prove them; I beg of you, have me excused.
20 “Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
And another said, I married a wife, and because of this I am not able to come.
21 “Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
And that servant having come, told these things to his lord, then the master of the house, having been angry, said to his servant, Go forth quickly into the broad places and lanes of the city, and the poor, and maimed, and lame, and blind, bring in here.
22 “Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
And the servant said, Lord, it has been done as you commanded, and still there is room.
23 “Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
And the lord said to the servant, Go forth into the ways and hedges, and constrain to come in, that my house may be filled;
24 Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
for I say to you that none of those men who have been called will taste of my dinner.”
25 Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
And there were going on with Him great multitudes, and having turned, He said to them,
26 “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
“If anyone comes to Me, and does not hate his own father, and mother, and wife, and children, and brothers, and sisters, and yet even his own life, he is not able to be My disciple;
27 Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
and whoever does not carry his cross, and come after Me, is not able to be My disciple.
28 “In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
For who of you, willing to build a tower, does not first, having sat down, count the expense, whether he has the things for completing?
29 Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
Lest that he having laid a foundation, and not being able to finish, all who are beholding may begin to mock him,
30 yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
saying, This man began to build, and was not able to finish.
31 “Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
Or what king going on to engage with another king in war, does not, having sat down, first consult if he with ten thousand is able to meet him who is coming against him with twenty thousand?
32 In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
And if not so—he being yet a long way off—having sent a delegation, he asks the things for peace.
33 Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
So, then, everyone of you who does not take leave of all that he himself has, is not able to be My disciple.
34 “Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
The salt [is] good, but if the salt becomes tasteless, with what will it be seasoned?
35 Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
It is neither fit for land nor for manure—they cast it outside. He who is having ears to hear—let him hear.”