< Luka 13 >
1 A yanzun fa, akwai waɗansu da suka kasance a lokacin can, suka ba Yesu labarin Galiliyawa da Bilatus ya gauraye jininsu tare da jinin hadayunsu.
Just at that time people came to tell Him about the Galilaeans whose blood Pilate had mingled with their sacrifices.
2 Yesu ya amsa ya ce, “Kuna tsammani waɗannan Galiliyawan sun fi dukan sauran Galiliyawa zunubi ne, shi ya sa suka sha irin wannan wahala?
"Do you suppose," He asked in reply, "that those Galilaeans were worse sinners than the mass of the Galilaeans, because this happened to them?
3 Ina gaya muku, a’a! Amma in ba ku tuba ba, ku ma duka za ku hallaka.
I tell you, certainly not. On the contrary, if you are not penitent you will all perish as they did.
4 Ko kuwa kuna tsammani, sha takwas ɗin nan da suka mutu lokacin da hasumiya a Silowam ya fāɗi a kansu, sun fi dukan sauran mutanen Urushalima laifi ne?
Or those eighteen on whom the tower at Siloam fell, do you suppose they had failed in their duty more than all the rest of the people who live in Jerusalem?
5 Ina gaya muku, a’a! Amma in ba ku tuba ba, ku ma duka za ku hallaka.”
I tell you, certainly not. On the contrary, if you do not repent you will all perish just as they did."
6 Sai ya ba su wannan misali ya ce, “Wani mutum yana da itacen ɓaure, da aka shuka a gonar inabinsa. Da ya je cire’ya’yan itacen, sai ya tarar ba tă yi’ya’ya ba.
And He gave them the following parable. "A man," He said, "who had a fig-tree growing in his garden came to look for fruit on it and could find none.
7 Sai ya ce wa mai lura da gonar inabin, ‘Yau shekara uku ke nan ina zuwa neman’ya’yan ɓaure daga itacen nan, amma ba na samun kome. Sare shi! Don me za a bar shi ya tare wuri.’
So he said to the gardener, "'See, this is the third year I have come to look for fruit on this fig-tree and cannot find any. Cut it down. Why should so much ground be actually wasted?'
8 “Mutumin ya amsa ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ka bar shi, in yi masa banƙasa, in kuma zuba masa taki har na shekara ɗaya.
"But the gardener pleaded, "'Leave it, Sir, this year also, till I have dug round it and manured it.
9 In kuwa ya ba da’ya’ya shekara mai zuwa, yana da kyau! In kuwa ba haka ba, sai ka sare shi.’”
If after that it bears fruit, well and good; if it does not, then you shall cut it down.'"
10 Wata ranar Asabbaci, Yesu yana koyarwa a wata majami’a,
Once He was teaching on the Sabbath in one of the synagogues
11 a wurin kuwa, akwai wata mace wadda aljani ya gurgunta, har na shekaru goma sha takwas. Duk ta tanƙware, ba ta ma iya miƙewa ko kaɗan.
where a woman was present who for eighteen years had been a confirmed invalid: she was bent double, and was unable to lift herself to her full height.
12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kirata gaba, ya ce mata, “Mace, an’yantar da ke daga rashin lafiyarki.”
But Jesus saw her, and calling to her, He said to her, "Woman, you are free from your weakness."
13 Sai ya ɗibiya hannuwansa a kanta, nan da nan sai ta miƙe, ta yabi Allah.
And He put His hands on her, and she immediately stood upright and began to give glory to God.
14 Amma mai mulkin majami’ar ya ji haushi da Yesu ya yi warkarwa a ranar Asabbaci. Sai ya ce wa mutanen, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Saboda haka, ku zo a ranakun nan a warkar da ku, ba ranar Asabbaci ba.”
Then the Warden of the Synagogue, indignant that Jesus had cured her on a Sabbath, said to the crowd, "There are six days in the week on which people ought to work. On those days therefore come and get yourselves cured, and not on the Sabbath day."
15 Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ku munafukai! Ashe, kowannenku ba yakan kunce bijiminsa ko jakinsa, yă kai shi waje yă ba shi ruwa, a ranar Asabbaci ba?
But the Lord's reply to him was, "Hypocrites, does not each of you on the Sabbath untie his bullock or his ass from the stall and lead him to water?
16 Ashe, bai kamata a’yantar da macen nan, diyar zuriyar Ibrahim, wadda Shaiɗan ya daure, har shekara goma sha takwas, a ranar Asabbaci, daga abin da ya daure ta ba?”
And this woman, daughter of Abraham as she is, whom Satan had bound for no less than eighteen years, was she not to be loosed from this chain because it is the Sabbath day?"
17 Sa’ad da ya faɗi wannan, sai duka masu gāba da shi suka kunyata. Amma mutane kuwa suka yi murna saboda dukan abubuwan banmamaki da yake yi.
When He had said this, all His opponents were ashamed, while the whole multitude was delighted at the many glorious things continually done by Him.
18 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Yaya mulkin Allah yake? Da me zan kwatanta shi?
This prompted Him to say, "What is the Kingdom of God like? and to what shall I compare it?
19 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda wani mutum ya ɗauka, kuma ya shuka a gonarsa. Ta yi girma, ta zama itace, kuma tsuntsayen sararin sama suka huta a rassansa.”
It is like a mustard seed which a man drops into the soil in his garden, and it grows and becomes a tree in whose branches the birds roost."
20 Ya sāke tambaya, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
And again He said, "To what shall I compare the Kingdom of God?
21 Yana kama da yisti wadda mace ta ɗauka, ta kwaɓa garin alkama mai yawa da shi, har sai da yistin ya gauraye kullun duka.”
It is like yeast which a woman takes and buries in a bushel of flour, to work there till the whole is leavened."
22 Sa’ad da Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi ta cikin garuruwan da ƙauyukan, yana koyarwa.
He was passing through town after town and village after village, steadily proceeding towards Jerusalem,
23 Sai wani ya tambaye shi ya ce, “Ya Ubangiji, shin, wai mutane kima ne kawai za su sami ceto?” Ya ce musu,
when some one asked Him, "Sir, are there but few who are to be saved?"
24 “Ku yi matuƙar ƙoƙari ku shiga ta matsattsiyar ƙofa, domin ina faɗa muku, mutane da yawa za su yi ƙoƙarin shiga, amma ba za su iya ba.
"Strain every nerve to force your way in through the narrow gate," He answered; "for multitudes, I tell you, will endeavour to find a way in and will not succeed.
25 Da zaran maigidan ya tashi ya rufe ƙofar, za ku tsaya a waje kuna ƙwanƙwasawa, kuna roƙo cewa, ‘Ranka yă daɗe, buɗe mana ƙofa.’ “Amma shi zai amma ya ce, ‘Ni ban san ku, ko inda kuka fito ba.’
As soon as the Master of the house shall have risen and shut the door, and you have begun to stand outside and knock at the door and say, "'Sir, open the door for us' --"'I do not know you,' He answers; 'you are no friends of mine.'
26 “Sa’an nan za ku ce, ‘Haba, mu da muka ci, muka sha tare da kai, har ka yi koyarwa a cikin titi-titi namu.’
"Then you will plead, "'We have eaten and drunk in your company and you have taught in our streets.'
27 “Amma shi zai amma ya ce, ‘Ban san ku, ko inda kuka fito ba. Ku rabu da ni, dukan ku masu aikata mugunta!’
"But He will reply, "'I tell you that you are no friends of mine. Begone from me, all of you, wrongdoers that you are.'
28 “Za a yi kuka a can, da cizon haƙora, sa’ad da kuka ga Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, da dukan annabawa a mulkin Allah, amma ku kuwa, za a jefar da ku a waje.
"There will be the weeping and gnashing of teeth, when you see Abraham and Isaac and Jacob and all the Prophets in the Kingdom of God, and yourselves being driven far away.
29 Mutane za su zo daga gabas, da yamma, da kudu, da arewa, su ɗauki wuraren zamansu a bikin, a cikin mulkin Allah.
They will come from east and west, from north and south, and will sit down at the banquet in the Kingdom of God.
30 Tabbatacce, akwai waɗansu da suke na ƙarshe, da za su zama na farko, na farko kuma, da za su zama na ƙarshe.”
And I tell you that some now last will then be first, and some now first will then be last."
31 A wannan lokaci, waɗansu Farisiyawa suka zo suka ce wa Yesu, “Ka bar nan ka tafi wani wuri dabam. Hiridus yana so ya kashe ka.”
Just at that time there came some Pharisees who warned Him, saying, "Leave this place and continue your journey; Herod means to kill you."
32 Ya amsa ya ce, “Ku je ku gaya wa dilan nan, wato, mai makirci cewa, ‘Da yau da kuma gobe, zan fitar da aljanu, in kuma warkar da mutane, sa’an nan a rana ta uku in cika burin aikina.
"Go," He replied, "and take this message to that fox: "'See, to-day and to-morrow I am driving out demons and effecting cures, and on the third day I finish my course.'
33 Duk da haka, dole in ci gaba da aikin a yau, da kuma gobe, sa’an nan in ci gaba da yin haka kashegari kuma, gama tabbatacce, ba annabi da yakan mutu a bayan birnin Urushalima!’
"Yet I must continue my journey to-day and to-morrow and the day following; for it is not conceivable that a Prophet should perish outside of Jerusalem.
34 “Urushalima, ayya Urushalima, ke da kika kashe annabawa, kuma kika jefa wa waɗanda aka aika gare ki da duwatsu. Sau da yawa na yi kewan in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, kamar yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma ba ki yarda ba!
O Jerusalem, Jerusalem, thou who murderest the Prophets and stonest those who have been sent to thee, how often have I desired to gather thy children just as a hen gathers her brood under her wings, and you would not come!
35 Duba, an bar muku gidanku fanko. Ina kuwa faɗa muku, ba za ku sāke ganina ba, sai kun ce, ‘Mai albarka ne shi wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”
See, your house is left to you. But I tell you that you will never see me again until you say, 'Blessed is He who comes in the name of the Lord!'"