< Luka 12 >
1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
tadānīṁ lokāḥ sahasraṁ sahasram āgatya samupasthitāstata ekaiko 'nyeṣāmupari patitum upacakrame; tadā yīśuḥ śiṣyān babhāṣe, yūyaṁ phirūśināṁ kiṇvarūpakāpaṭye viśeṣeṇa sāvadhānāstiṣṭhata|
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
yato yanna prakāśayiṣyate tadācchannaṁ vastu kimapi nāsti; tathā yanna jñāsyate tad guptaṁ vastu kimapi nāsti|
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
andhakāre tiṣṭhanato yāḥ kathā akathayata tāḥ sarvvāḥ kathā dīptau śroṣyante nirjane karṇe ca yadakathayata gṛhapṛṣṭhāt tat pracārayiṣyate|
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
he bandhavo yuṣmānahaṁ vadāmi, ye śarīrasya nāśaṁ vinā kimapyaparaṁ karttuṁ na śakruvanti tebhyo mā bhaiṣṭa|
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna )
tarhi kasmād bhetavyam ityahaṁ vadāmi, yaḥ śarīraṁ nāśayitvā narakaṁ nikṣeptuṁ śaknoti tasmādeva bhayaṁ kuruta, punarapi vadāmi tasmādeva bhayaṁ kuruta| (Geenna )
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
pañca caṭakapakṣiṇaḥ kiṁ dvābhyāṁ tāmrakhaṇḍābhyāṁ na vikrīyante? tathāpīśvarasteṣām ekamapi na vismarati|
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
yuṣmākaṁ śiraḥkeśā api gaṇitāḥ santi tasmāt mā vibhīta bahucaṭakapakṣibhyopi yūyaṁ bahumūlyāḥ|
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
aparaṁ yuṣmabhyaṁ kathayāmi yaḥ kaścin mānuṣāṇāṁ sākṣān māṁ svīkaroti manuṣyaputra īśvaradūtānāṁ sākṣāt taṁ svīkariṣyati|
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
kintu yaḥ kaścinmānuṣāṇāṁ sākṣānmām asvīkaroti tam īśvarasya dūtānāṁ sākṣād aham asvīkariṣyāmi|
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
anyacca yaḥ kaścin manujasutasya nindābhāvena kāñcit kathāṁ kathayati tasya tatpāpasya mocanaṁ bhaviṣyati kintu yadi kaścit pavitram ātmānaṁ nindati tarhi tasya tatpāpasya mocanaṁ na bhaviṣyati|
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
yadā lokā yuṣmān bhajanagehaṁ vicārakartṛrājyakartṛṇāṁ sammukhañca neṣyanti tadā kena prakāreṇa kimuttaraṁ vadiṣyatha kiṁ kathayiṣyatha cetyatra mā cintayata;
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
yato yuṣmābhiryad yad vaktavyaṁ tat tasmin samayaeva pavitra ātmā yuṣmān śikṣayiṣyati|
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
tataḥ paraṁ janatāmadhyasthaḥ kaścijjanastaṁ jagāda he guro mayā saha paitṛkaṁ dhanaṁ vibhaktuṁ mama bhrātaramājñāpayatu bhavān|
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
kintu sa tamavadat he manuṣya yuvayo rvicāraṁ vibhāgañca karttuṁ māṁ ko niyuktavān?
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
anantaraṁ sa lokānavadat lobhe sāvadhānāḥ satarkāśca tiṣṭhata, yato bahusampattiprāptyā manuṣyasyāyu rna bhavati|
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
paścād dṛṣṭāntakathāmutthāpya kathayāmāsa, ekasya dhanino bhūmau bahūni śasyāni jātāni|
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
tataḥ sa manasā cintayitvā kathayāmbabhūva mamaitāni samutpannāni dravyāṇi sthāpayituṁ sthānaṁ nāsti kiṁ kariṣyāmi?
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
tatovadad itthaṁ kariṣyāmi, mama sarvvabhāṇḍāgārāṇi bhaṅktvā bṛhadbhāṇḍāgārāṇi nirmmāya tanmadhye sarvvaphalāni dravyāṇi ca sthāpayiṣyāmi|
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
aparaṁ nijamano vadiṣyāmi, he mano bahuvatsarārthaṁ nānādravyāṇi sañcitāni santi viśrāmaṁ kuru bhuktvā pītvā kautukañca kuru| kintvīśvarastam avadat,
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
re nirbodha adya rātrau tava prāṇāstvatto neṣyante tata etāni yāni dravyāṇi tvayāsāditāni tāni kasya bhaviṣyanti?
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
ataeva yaḥ kaścid īśvarasya samīpe dhanasañcayamakṛtvā kevalaṁ svanikaṭe sañcayaṁ karoti sopi tādṛśaḥ|
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
atha sa śiṣyebhyaḥ kathayāmāsa, yuṣmānahaṁ vadāmi, kiṁ khādiṣyāmaḥ? kiṁ paridhāsyāmaḥ? ityuktvā jīvanasya śarīrasya cārthaṁ cintāṁ mā kārṣṭa|
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
bhakṣyājjīvanaṁ bhūṣaṇāccharīrañca śreṣṭhaṁ bhavati|
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
kākapakṣiṇāṁ kāryyaṁ vicārayata, te na vapanti śasyāni ca na chindanti, teṣāṁ bhāṇḍāgārāṇi na santi koṣāśca na santi, tathāpīśvarastebhyo bhakṣyāṇi dadāti, yūyaṁ pakṣibhyaḥ śreṣṭhatarā na kiṁ?
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
aparañca bhāvayitvā nijāyuṣaḥ kṣaṇamātraṁ varddhayituṁ śaknoti, etādṛśo lāko yuṣmākaṁ madhye kosti?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
ataeva kṣudraṁ kāryyaṁ sādhayitum asamarthā yūyam anyasmin kāryye kuto bhāvayatha?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
anyacca kāmpilapuṣpaṁ kathaṁ varddhate tadāpi vicārayata, tat kañcana śramaṁ na karoti tantūṁśca na janayati kintu yuṣmabhyaṁ yathārthaṁ kathayāmi sulemān bahvaiśvaryyānvitopi puṣpasyāsya sadṛśo vibhūṣito nāsīt|
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
adya kṣetre varttamānaṁ śvaścūllyāṁ kṣepsyamānaṁ yat tṛṇaṁ, tasmai yadīśvara itthaṁ bhūṣayati tarhi he alpapratyayino yuṣmāna kiṁ na paridhāpayiṣyati?
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
ataeva kiṁ khādiṣyāmaḥ? kiṁ paridhāsyāmaḥ? etadarthaṁ mā ceṣṭadhvaṁ mā saṁdigdhvañca|
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
jagato devārccakā etāni sarvvāṇi ceṣṭanate; eṣu vastuṣu yuṣmākaṁ prayojanamāste iti yuṣmākaṁ pitā jānāti|
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
ataeveśvarasya rājyārthaṁ saceṣṭā bhavata tathā kṛte sarvvāṇyetāni dravyāṇi yuṣmabhyaṁ pradāyiṣyante|
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
he kṣudrameṣavraja yūyaṁ mā bhaiṣṭa yuṣmabhyaṁ rājyaṁ dātuṁ yuṣmākaṁ pituḥ sammatirasti|
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
ataeva yuṣmākaṁ yā yā sampattirasti tāṁ tāṁ vikrīya vitarata, yat sthānaṁ caurā nāgacchanti, kīṭāśca na kṣāyayanti tādṛśe svarge nijārtham ajare sampuṭake 'kṣayaṁ dhanaṁ sañcinuta ca;
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
yato yatra yuṣmākaṁ dhanaṁ varttate tatreva yuṣmākaṁ manaḥ|
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
aparañca yūyaṁ pradīpaṁ jvālayitvā baddhakaṭayastiṣṭhata;
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
prabhu rvivāhādāgatya yadaiva dvāramāhanti tadaiva dvāraṁ mocayituṁ yathā bhṛtyā apekṣya tiṣṭhanti tathā yūyamapi tiṣṭhata|
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
yataḥ prabhurāgatya yān dāsān sacetanān tiṣṭhato drakṣyati taeva dhanyāḥ; ahaṁ yuṣmān yathārthaṁ vadāmi prabhustān bhojanārtham upaveśya svayaṁ baddhakaṭiḥ samīpametya pariveṣayiṣyati|
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
yadi dvitīye tṛtīye vā prahare samāgatya tathaiva paśyati, tarhi taeva dāsā dhanyāḥ|
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
aparañca kasmin kṣaṇe caurā āgamiṣyanti iti yadi gṛhapati rjñātuṁ śaknoti tadāvaśyaṁ jāgran nijagṛhe sandhiṁ karttayituṁ vārayati yūyametad vitta|
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
ataeva yūyamapi sajjamānāstiṣṭhata yato yasmin kṣaṇe taṁ nāprekṣadhve tasminneva kṣaṇe manuṣyaputra āgamiṣyati|
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
tadā pitaraḥ papraccha, he prabho bhavān kimasmān uddiśya kiṁ sarvvān uddiśya dṛṣṭāntakathāmimāṁ vadati?
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
tataḥ prabhuḥ provāca, prabhuḥ samucitakāle nijaparivārārthaṁ bhojyapariveṣaṇāya yaṁ tatpade niyokṣyati tādṛśo viśvāsyo boddhā karmmādhīśaḥ kosti?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
prabhurāgatya yam etādṛśe karmmaṇi pravṛttaṁ drakṣyati saeva dāso dhanyaḥ|
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
ahaṁ yuṣmān yathārthaṁ vadāmi sa taṁ nijasarvvasvasyādhipatiṁ kariṣyati|
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
kintu prabhurvilambenāgamiṣyati, iti vicintya sa dāso yadi tadanyadāsīdāsān praharttum bhoktuṁ pātuṁ madituñca prārabhate,
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
tarhi yadā prabhuṁ nāpekṣiṣyate yasmin kṣaṇe so'cetanaśca sthāsyati tasminneva kṣaṇe tasya prabhurāgatya taṁ padabhraṣṭaṁ kṛtvā viśvāsahīnaiḥ saha tasya aṁśaṁ nirūpayiṣyati|
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
yo dāsaḥ prabherājñāṁ jñātvāpi sajjito na tiṣṭhati tadājñānusāreṇa ca kāryyaṁ na karoti sonekān prahārān prāpsyati;
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
kintu yo jano'jñātvā prahārārhaṁ karmma karoti solpaprahārān prāpsyati| yato yasmai bāhulyena dattaṁ tasmādeva bāhulyena grahīṣyate, mānuṣā yasya nikaṭe bahu samarpayanti tasmād bahu yācante|
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
ahaṁ pṛthivyām anaikyarūpaṁ vahni nikṣeptum āgatosmi, sa ced idānīmeva prajvalati tatra mama kā cintā?
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
kintu yena majjanenāhaṁ magno bhaviṣyāmi yāvatkālaṁ tasya siddhi rna bhaviṣyati tāvadahaṁ katikaṣṭaṁ prāpsyāmi|
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
melanaṁ karttuṁ jagad āgatosmi yūyaṁ kimitthaṁ bodhadhve? yuṣmān vadāmi na tathā, kintvahaṁ melanābhāvaṁ karttuṁm āgatosmi|
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
yasmādetatkālamārabhya ekatrasthaparijanānāṁ madhye pañcajanāḥ pṛthag bhūtvā trayo janā dvayorjanayoḥ pratikūlā dvau janau ca trayāṇāṁ janānāṁ pratikūlau bhaviṣyanti|
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
pitā putrasya vipakṣaḥ putraśca pitu rvipakṣo bhaviṣyati mātā kanyāyā vipakṣā kanyā ca mātu rvipakṣā bhaviṣyati, tathā śvaśrūrbadhvā vipakṣā badhūśca śvaśrvā vipakṣā bhaviṣyati|
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
sa lokebhyoparamapi kathayāmāsa, paścimadiśi meghodgamaṁ dṛṣṭvā yūyaṁ haṭhād vadatha vṛṣṭi rbhaviṣyati tatastathaiva jāyate|
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
aparaṁ dakṣiṇato vāyau vāti sati vadatha nidāgho bhaviṣyati tataḥ sopi jāyate|
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
re re kapaṭina ākāśasya bhūmyāśca lakṣaṇaṁ boddhuṁ śaknutha,
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
kintu kālasyāsya lakṣaṇaṁ kuto boddhuṁ na śaknutha? yūyañca svayaṁ kuto na nyāṣyaṁ vicārayatha?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
aparañca vivādinā sārddhaṁ vicārayituḥ samīpaṁ gacchan pathi tasmāduddhāraṁ prāptuṁ yatasva nocet sa tvāṁ dhṛtvā vicārayituḥ samīpaṁ nayati| vicārayitā yadi tvāṁ praharttuḥ samīpaṁ samarpayati praharttā tvāṁ kārāyāṁ badhnāti
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
tarhi tvāmahaṁ vadāmi tvayā niḥśeṣaṁ kapardakeṣu na pariśodhiteṣu tvaṁ tato muktiṁ prāptuṁ na śakṣyasi|