< Luka 12 >

1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
Aša mulc ominj su sakupilit dă mar kălka una pă alt kic as re pă lănga Isus. Ali Isus elši u zăs alu učenici aluj: “Loc sama dă kvascu alu farizej! Ala kvas ăj licemjerje.
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
Njimika nuj akupirit šje no fi dăskupirit, njiš una tajnă kari no fi šćută.
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
Aša dakă ac zăs šjeva ăm tunjerik su šći ăm lumină, šă dakă ac šupunjit šjeva ăm soba avostră aje isto u fi mužjit pă krovur dă kăš.”
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
Isus u zăs: “Urtašji amej lasăcămă să vă zăk, nu vă fijă frikă dă eje kari numa vă poći amură tela šă nu poći njimika să vă fakă.
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
Ju vuj zăšji dă šjinji trăbă să vă fijă frikă. Fijă vă frikă dă Dimizov kari poči să amori, atunšje vă poči vărlji ăm pakao. Da anume, dă jăl vă trăbă să vă fijă frikă. (Geenna g1067)
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Nus šinšj (5) vrăbuj văndući dă doj banj? Dimizov nu mujtă pă njime.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
A avovă čak šă păru pă kap vi umărat. Nu vă fijă frikă! Voj ščec maj vredni dă gărmadă dă vrăbuj.”
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
Isus u zăs: “Šjinji gođ pă pămănt mu priznali pă minji ăm nenće alu ominj, Ju Fišjoru Omuluj isto uj priznali pă jăl ăm nenće lu anđelji alu Dimizov.
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
Ala kari pă minji nu mu priznali pă pămănt ju muj odreknuli dă jăl la anđeljilje alu Dimizov.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Dakă bilo šjinji svitešći vorba protiv dă minji Fišjoru Omuluj aluje poći fi jirtat; ali dakă šjinjiva svitešči mišjunj dă Duhu Svănt, grehula no fi jirtat.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
Dakă vu adušji la sud ăm sinagogur šă la poglavicur šă vladarur, nu vă brigalec kum šă ku šje muj branali, ili šje să zăk.
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
Kănd u vinji vreme, Duhu Svănt ću ănvăca šje trăbă să zăšj.”
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
Unu dăm ominj ăm gărmadă u zăs alu Isus: “Učitelju ză alu fračilje amnjov să să ămperci ku minji šje anj kăpătat.”
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
Isus u odbilit šă zăšje: “Omulji, šinji mu pus pă minji dă sudac, să ămpărc ăntri voj doj?”
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
Atunšje kănd u svătit alu toc kutotu, Isus u zăs: “Băgăc sama šă păzăcăvă dă pulkučală! Dakă šjinjiva ari mult, tod daje kustu aluj nuj siguran bez obzira kă ari kutotu.”
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
Isus u spus maj una usporedbă: “Are akulo om găzdak făr dă firi kari ave tălek šă tălekula u adus mult plod.
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
Šă jăl šu zăs săngur aluj: ‘Šje să fak kă nam dăstul lok să puj ăndărăt šje mu kriskut?’
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
Atunšje, jăl u zăs: ‘Aša uj fašji: Ju uj răstuna skladišturlje amelji šă uj gradali maj mari, dăstul dă mari să spremălesk kutotu šje mu kriskut.’
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
Šă ju muj zăšji alu duša ame: ‘Aj mulći bunji stvarur aku, šă dă mulc ej šje ur vinji. Odmoruleščići, mănănkă šă be, šă ănfulušeščići!’
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
Ali Dimizov ju zăs aluj: ‘Tu omulje făr dă firi! Mar ăm asta nopći uj šjire duša ata. Atunšje šjinji u ave korist dăm stvarurlje šje caj pus ăndărăt?’
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
Aša păce omu kari ăš akulježi găzdăšijilje păntru jăl săngur, a nu su găzdašjit ăm oči alu Dimizov.”
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
Kapu u zăs Isus alu učenici: “Daje vă zăk: voj nu trăbă să vă brigalec, dă kustu avostru, šă să fijec ăm brigur šje vic mănka, ili să vă brinulec ăm šje vic ămbrăka.
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
Daje kă kustu ăj maj vrednă dă kit mănkare, šă tela maj mult dă kit colu.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Numa ujtăcăvă la găgărašć. Jej njišj nu samănă, njišj nu akulježi. Jelji nari skladište ili šupă, šă tod daje Dimizov lji rănješći. Nu ščec voj maj vredni dă vrabujrljelje?
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
Poči šjinjiva dăm voj ku brigurlje produžuli kustu?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
Dakă, nu pučec să făšjec niti maj măkăčelji, adăšje ščec ăm brigur dă kutotu ostalo?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Numa ujtăcăvă la flor ăm telek! Jelji niti să trudulešći niti fašji colji ali ju vă zăk, kă njiš Car Salomon ăm găzdăšije alor nu are ămbrăkat aša măndru ka florurlje ăm telek.
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
Ali dakă Dimizov dă dastafel măndremi alu jarbă kari kustă astăs, šă să bagă ăm fok, kit atunšje maj mult u da jăl avovă. O voj avec mikă ănkriđală!
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
Dăm ala rănd nu vă gănđec šje vic mănka šă šje vic be. Nu vă uznemirilec!
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
Dă kutotu aje să brinulešći ominj făr dă Dimizov. Ăngănđecăvă kă Tata avostru dăm nor šćijă šje vă trăbă.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
Šă anume tražalec kraljevstva alu Dimizov elši šă kutotu ostalo vu fi dat.
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
O mikă stadă, nuc fijă frikă, kă Tata avostru să ănfălušešći să vă apušji ăm kraljevstva aluj.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
Vinđec kutotu šje avec šă dăđec alu sărašj. Aša adunăcăvă tăšč kari nu su puće rupi, šă găzdăšijă să vă fijă ăm nor kari nu propadalešči, hunđi lotri nor puće vinji, niti găndašji să mănăšji!
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
Daje kă sufljičilje avoštri u fi hunđi ăj blago avostru.”
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Isus u zăs alu učenici: “Fijec spremni dă lukru, la să fijec opremilică šă ăm mănjilje avoštri lasă fijă luminjilje acăcaći.
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
Aša u fi ka slugurlje kari u ašćiptat pă gospodaru aluj să să ăntorkă dă pă nuntă, spremni să ăj dăsvăkă kum u kukunji pă ušă.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Măndremi alu eje slugur kari u fi skulac, kănd u vinji gospodaru! Anume ju vă zăk: Domnu šu punji săngur kintrinca să lji služulaskă šă lju punji să šadă la masă šă lju dvoruli.
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
Šă kănd u vinji gospodaru ăm miržuku dă nopči ili dăspru zua šă lju afla aša, măndremi u fi alu ala slugur!
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
Slušulecămă dă asta: ka să šćijă gazda ăm kari šas u vinji lotru, jăl ar păză šă nar lăsa să ăj fijă provalalit ăm kasă.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Voj isto trăbă să fijec spremni, kă ju Fišjoru Omuluj uj vinji ăm vremi kănd nu či nadali.”
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
Petar atunšje lu ăntribat pă jăl: “Domnu spuj tu asta usporedbă păntru noj učenici, ili ăj păntru toc?”
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
Isus u zăs: “Šinji ăj ala vjernă šă kufiri upravitelj kari ăl postavalešći dă gospodar pă kasa, šă ăm pravă vremi u da mănkari alu toc ăm kasa?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Măndremi alu ala sluga kari kănd u vinji gospodaru, u fašji aša.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
Dă anume, ju vă spuj kă gospodaru u odredilit alu ala sluga să vodulaskă ku kutotu imanje kari ari.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
Ali dakă sluga šar zăšji ăm sufljituš: ‘Gospodaru, nu su ăntoršji aša păfriš’, šă atunšje să apušji să bată pă slugur šă să be, mănăšji šă să ambeći?
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
Atunšje u vinji gospodaru alu sluga ăm šjas kari nu šćijec. Šă atunšje fărd dă milost lu kaznali, ju da sudbină ku alci una kari nus vjerni.
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
Sluga kari šćijă šje gănđešći gospodaru, šă dakă nu fašji šă nu să pripremilešči dă dolasku aluj, jăl u kăpăta mulći luvalur.
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
Ali dakă sluga nu šćijă voje alu gospodaru, šă fašji šjeva šje zaslužulešći kaznă, atunšje u kăpăta pucănji luvalur. Kă alu toc kari mult u fost dat, mult su ašćipta dă la jej, šă alu eje alu kari u fost mult dat ăm povjerenje, dă la eje šă maj mult u fi šjirut.”
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
Isus u zăs: “Ju am vinjit să vărljesk fok dă sud pă pămănt, šă kum aš gănđi să să apušji să ardă!
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
Trăbă majnti să mă bučez ku mukur. Kum mă mučulesk pă šje aje no trešji!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Gănđec kă am vinjit să vă aduk putuljală pă pămănt ăntri ominj? Nu, ju am adus podjelă!
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
Dă aku maj menkulo ăm kasa dă šinšj ominj ur fi ămpărcăc tri u fi pă parče ame šă doj protiv dă tri.
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
Tatusu u fi protiv dă fišjoruš, šă fišjoru u fi protiv dă tatusu, mumăsa protiv dă fataš, a fata protiv dă mumăsa, šă sokra protiv dă njivastaš, šă njivasta protiv dă sokrăsa.”
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
Kum svite alu gărmadă, Isus u zăs: “Kănd viđec njegri oblakur kă să răđika dă pă more pă zapad, voj odma zăšjec: ‘Astăs u fi plojă’, šă voj ščec u pravu.
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
Šă kănd să apukă să bată văntu dăm pustinja la jug, odma zăšjec: ‘U fi zuva tari kaldă’, šă ăj aša.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
Licemjerilor! Voj šćijec să čitalec znakurlje pă pămănt šă pă nor. Kum dă nu prišjipec šje aku să dogudulešči!
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Voj ac trăbuji dăm haje avostru să šćijec šje ăj benji.
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
Dăkă šjinjiva či optužulešći păntru dugu kari nac plăčit šă vă gănđešči să vă adukă la sud, ănšjarkă inka pă kalji să vij la ligizală majnti dă sud! Ar puće să či adukă la sudac, sudacu să či đe la oficir, šă oficiru či poći băgă ăm čemică.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
Ju vă zăk, kă akulo vi trăbuji să rămăj păn šje no fi plăčit toc banji.”

< Luka 12 >