< Luka 12 >
1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
Kwa wakati obhu, maelfu mingi gha bhanu bhakusanyiki pamonga kiasi kya kujhanda kukanyana, akajhanda kujobha ni bhanafunzi bha muene hoti, “Mukihadhariajhi ni chachu jha Mafarisayo ambajho ndo unafiki”
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
Na pibelepi kujha ni siri gha jhifigheme ambajho jhibeta lepi kufunulibhwa, wala lijambo lya lifighibhu ambalyo libelepi kumanyikana.
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
Na lyolyoha lyamwibeta kujobha mu ngisi libetapelekibhwa mu mwanga. Na ghoghoha gha mghajobhili mu mbolokhoto mu fichumba fyenu fya futendibhu ghibeta kutangasibhwa panani pa nyumba.
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
Nikabhajobhela marafiki zangu, musibhatili bhala bhabhikoma mb'ele na kisha bhajhelepi ni khenu khenge kya kukheta,
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna )
Lakini nikabhaonya jhamwibeta kuntila. Muntilayi jhola ambajhe baada jha kuhoma, ajheni mamlaka gha kutagha jehanamu. Ena, nikabhajobhela muenga muntilayi ojho. (Geenna )
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Je shomoro bhahanu bhigolesibhwa lepi kwa sarafu sibhele? hata hivyo ajhelepi hata mmonga bhabhi jhaibeta kujhebhelelibhwa palongolo pa K'yara.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
Lakini mumanyayi kujha, njwili sya mitu ghinu ghibhalangibhu. Msitili muenga mwebha thamani mbaha kuliko shomoro bhingi.
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
Nikabhajobhela, jhejhioha jha akanikiri nene mbele sya bhanu, Mwana ghwa Adamu ibeta kun'kiri mbele sya malaika bha K'yara.
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
Lakini jhejhioha jhaibeta kunibela mbele sya bhanu, ni muene ibetakubelibhwa mbele jha malaika bha K'yara.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Jhejhioha jhaibeta kujobha lilobhi linofu lepi kwa mwana ghwa Adamu, ibetakusamehebhwa, lakini jhejhioha jhaibekun'kufuru Roho mtakatifu, ibetalepi kusamehebhwa.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
Pabhibeta kubhapeleka mbele sya bhabhaha bha masinagogi, bhatawala ni bhenye mamlaka, Musitili juu ni namna jha kulongela katika kwitetela au kiki kyamwibeta kujobha,
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
Kwa kujha Roho mtakatifu ibetakubhafundisya kya mwibeta kujobha kwa wakati obhu.”
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
Munu mmonga pa kusanyiku akan'jobhela, “Mwalimu, n'jobhelayi ndongo bhangu anigabhilayi sehemu jha urithi bhwangu.”
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
Yesu akan'jibu, niani anibhekili kujha mwamuzi ni mpatanishi kati jha muenga?
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
Ndipo akabhajobhela, mkihadhariajhi ni khila namna jha tamaa, kwandabha uzima bhwa munu ujhelepi kwa fenu fya ajhe nafu.”
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
Yes akabhajobhela mfano, akajobha, N'gonda ghwa munu mmonga tajiri ghwahoguili nesu,
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
na akakikota mugati mwa muene, akajobha nibetaketabhuli kwani nijhelepi ni sehemu jha kubheka mazao ghangu?
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
Akajobha, nibetakheta naha. Nibetakubomola ghala sya jhoni sidebe ni kujhenga jhibhaha nikuhifadhi mazao gha nene ghoha ni fenu fenge.
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
Nibetakujobhela nafsi jha nene, “Nafsi, ukibhakili akiba jha fenu fingi kwa miaka ghimehele. P'omosekayi, uliayi, unyuajhi ni kustarehe.”
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
Lakini K'yara akabhajobhela, ebhe munu mpumbafu, kiru kya lelu wilonda Roho kuhoma kwa bhebhe ni fenu fyoha fye ufiandele fibetakujha fya kiki?
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
Ndivyo kyajhibekujha kwa khila munu jhaikibhekela mali na sio kwitayarisya kwandabha jha Bwana.
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
Yesu akabhajobhela bhanafunzi bha muene, kwa hiyo nikabhajobhela musihofu juu jha maisha gha jhomu jha kujha mwibeta kulya kiki au juu jha mibhele ghya jhomu jha kujha mwibeta kufuala kiki
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
Kwa kuwa maisha ndo zaidi jha kyakulya, ni mb'ele ndo zaidi jha mavazi.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Mulangayi fidege fya anga, bhilema lepi bhwala kuvuna. Bhajhelepi ni kichumba bhwala ghala lya kubhekela, lakini Dadi jhinu akabhalasya. Muenga bora lepi kuliko fidege!
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
Jholekhu kati jha muenga akakisumbulayi ibhwesya kujhongesya dhiraa jhimonga katika maisha gha muene?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
Ikajhiajhi mwibhwesya lepi kuketa naha ekhu khenu kidusu kyepesi kwandajha kiki kusumbukila aghu ghangi?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Mulangayi maua -kyaghimele. Ghibhomba lepi mbombo wala kusokota. Lakini nikabhajobhela, hata Sulemani mu utukufu bhwa muene bhoha afwekibhu lepi kama mmonga ghwa agha,
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
Kama K'yara akaghafueka kinofu mat'ondo ghakondeni, ambagho lelu ghajhele, ni kilabhu ghitaghibhwa mu muoto. Je si nesu akabhafueka muenga? mwebha imani haba!
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
Msisumbukili juu jha kujha mwibeta kulya kiki au mwibeta kunywa kiki, bhwala musijhi ni hofu.
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
Kwakujha Mataifa ghoha gha dunia ghisumbukila mambo agha. Ni Dadi jhinu amanyili kujha mwilonda aghu.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
Lakini mulondayi ufalme bhwa muene hoti, ni aghu ghangi mwibeta kuzidishibhwa,
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
Musitili muenga likundi lidebe, kwandabha Dadi jhinu ohobhwiki kubhap'ela muenga ufalme obhu.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
Muhemelesiajhi mali sya muenga ni mali mubhapelayi maskini, mukifanyilayi mifuko ghyaghushibhwa lepi hazina jha kumbinguni jhajhimalika lepi, sehemu ambajho bhaheji bhibeta lepi kukaribila wala nondo jhibeta lepi kuharibu.
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
Kwakujha pajhe ni hazina jha jhobhi, ndipo ni roho jha jhobhi pajhibekujha.
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Nghobho sya jhomu sitali sijhelayi sikongibhu kwa n'kanda, ni taa sya jhomu sihakikisibhwayi kujha sijhendelela kujhaka,
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
na mujhelayi kama bhanu bhabhakandendela Bwana ghwa bhene kuhomela mu sherehe jha harusi, ili kwamba ahidayi ni kupiga hodi, bhibeta kubhwesya kun'dendulila ndiangu kwa haraka.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Bhabarikibhu bhala bhatumishi, ambabho Bwana ibeta kubhekolela mihu. Hakika ibeta kukonga nghobhu jha muene jhitali kwa n'kanda, kisha ibeta kubhatamika pasi kwa kyakulya, Kisha kubhahudumila.
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
Kama Bwana ibeta kuhida kwa zamu jha pili jha ulinzi jha pakiru, au zamu jha tatu jha ulinzi, nu kubhakolela bhajhe tayari, ibeta kujha heri kwa abhu bhatumishi.
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
Zaidi jha aghu, mmanyayi ele, kama Bwana n'kolo nyumba ngaajhimanyi saa ambajho mmeji ihida, ngaanihusuililepi nyumba jha muene jhibomolibhwayi.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Mujhiajhi tayari kwani mumanyilepi ndo wakati gani Mwana ghwa Adamu ibeta kerebhuka.
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
Petro akajobha, “Bwana, ukatujobhela tete twebhene mifano ejhe, au ukan'jobhela khila munu?
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
Bwana akabhajobhela, “Niani mtumwa mwaminifu au mwenye hekima ambaye Bwana ghwa muene ibeta kumbeka panani pa bhatumishi bhangi, ili abhag'abhilayi kyakulya kwa wakati muafaka?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Abarikibhu mtumishi jhola, ambajhe Bwana ghwake akahidajhi ibeta kun'kolela ibhomba ghala gha alaghisibhu.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
Hakika nikabhajobhela muenga jha kujha ibeta kumbeka panani pa mali jha muene jhioha.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
Lakini mtumishi jhola akajobha mu muoyo ghwa muene, “bwana ikabhela kukerebhuka; hivyo akajhanda kubhatobha bhala bhatumishi bha kigosi ni kidala, kisha akajhanda kulya, kunywa ni kugala,
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
bwana ghwa muene mtumwa jhola ibeta kuhida ligono lya ategemeleghe lepi ni saa jhaajhimanyilepi, ni muene ibeta kun'dumula fipandi ni kumbeka sehemu jhimonga ni bhabhabelikujha bhaaminifu'
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
Mtumishi, jhaamanyili mapenzi gha Bwana ghwa muene, ni muene akakiandele lepi wala aketili lepi kinofu ni mapenzi gha muene ibetakutobhibhwa fiboko fimehele.
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
Lakini mtumishi jhaamanyilepi mapenzi gha bwana ghwa muene, na adhabu, ibeta kutobhibhwa fiboko fidebe. Kwa kujha muene jha apelibhu fimehele, idaibhwa kuhoma kwa muene, ni muene jhaaminibhu kwa fimehele, kwa muene fibetakudaibhwa fimehele zaidi.
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
Nihidili kubhwasya muoto duniani, na ninoghele ujhelayi umalikujhaka,
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
Lakini nijheni ubatizo ambabho nibetakubatisibhwa na nijhe ni huzuni mpaka pa wibeta kukamilika!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Je mwifikiri nihidili kuleta amani duniani? Lepi, nikabhajobhela, badala jhiake niletili mgawanyiku.
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
kuh'omela henu ni kujhendelela kubetakujha ni bhanu bhahanu mu nyumba jhimonga bhagawanyiki, na bhadatu bhibetakujha kinyume ni bhabhele bhibetakujha kinyume ni bhadatu.
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
Bhibeta kugabhwanyika, Dadi ibetakujha kinyume ni mwanabhe ni ibetakujha kinyume ni Dadijhe, mabhu ibetakujha kinyume ni mwali munu ni mwali munu ibetakujha kinyume ni nyinamunu, Mama mkwe ibetakujha kinyume ni n'kwibhi ni nkwibhi ibeta kujha kinyume ni Mama mkwe ghu muene.
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
Yesu akajhe akabhajobhela makutano kabhele, “Mara pa mwibhona mabhengu ghihomela magharibi, mwijobha nyakati sya fula sifikili; na ndo kya jhijha,
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
Ni mpongo ghwa kusini ukabhumayi, mwijobha, pibeta kujha ni joto kali, na ndo kya jhijha.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
Enyi bhanafiki, mwibhwesya kutafsiri mwonekano bhwa nchi ni anga, lakini jhijha bhuli mwisindwa kutafsiri wakati bhwa ujhele?
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Kwandajha kiki khila mmonga bhinu. asipambanuli lyalijhele sahihi kwa muene wakati ambapo angali ajhe ni nafasi jha kubhomba aghu?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
Ndabha mkalotayi ni mshitaki ghwa jhobhi pa hakimu, kitahidiajhi kupatana ni mshitaki ghwa jhobhi mugati mwako na munjela asije akakupeleka kwa hakimu, ni hakimu kulongosya kwa ofisa, ni ofisa kusopa mu ligereza.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
Nikujobhela, wibetalepi kupita okhu hadi ulepayi mpaka senti jha mwishu.