< Luka 12 >

1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
In the meantime, when many thousands of the people were gathered together, so much that they trampled on each other, he began to say to his disciples first of all, “Beware of the yeast of the Pharisees, which is hypocrisy.
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
But there is nothing concealed that will not be revealed, and nothing hidden that will not be known.
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
So whatever you have said in the darkness will be heard in the light, and what you have spoken in the ear in the inner rooms will be proclaimed upon the housetops.
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
I say to you my friends, do not be afraid of those who kill the body, and after that they have no more that they can do.
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
But I will warn you about whom to fear. Fear the one who, after he has killed, has authority to throw you into hell. Yes, I say to you, fear him. (Geenna g1067)
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Are not five sparrows sold for two small coins? Yet not one of them is forgotten in the sight of God.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
But even the hairs of your head are all numbered. Do not fear. You are more valuable than many sparrows.
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
I say to you, everyone who confesses me before men, the Son of Man will also confess before the angels of God,
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
but he who denies me before men will be denied before the angels of God.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Everyone who speaks a word against the Son of Man, it will be forgiven him, but to him who blasphemes against the Holy Spirit, it will not be forgiven.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
When they bring you before the synagogues, the rulers, and the authorities, do not worry about how you will speak in your defense, or what you will say,
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
for the Holy Spirit will teach you in that hour what you should say.”
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
Then someone from the crowd said to him, “Teacher, tell my brother to divide the inheritance with me.”
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
Jesus said to him, “Man, who made me a judge or a mediator over you?”
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
He said to them, “Watch that you keep yourselves from all greedy desires, because a person's life does not consist of the abundance of his possessions.”
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
Then Jesus told them a parable, saying, “The field of a rich man yielded abundantly,
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
and he reasoned with himself, saying, 'What will I do, because I do not have a place to store my crops?'
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
He said, 'This is what I will do. I will pull down my barns and build bigger ones, and there I will store all of my grain and other goods.
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
I will say to my soul, “Soul, you have many goods stored up for many years. Rest easy, eat, drink, be merry.”'
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
But God said to him, 'Foolish man, tonight your soul is required of you, and the things you have prepared, whose will they be?'
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
That is what someone is like who stores up treasure for himself and is not rich toward God.”
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
Jesus said to his disciples, “Therefore I say to you, do not worry about your life, what you will eat—or about your body, what you will wear.
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
For life is more than food, and the body is more than clothes.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Consider the ravens, that they do not sow or reap. They have no storeroom or barn, but God feeds them. How much more valuable you are than the birds!
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
Which of you by being anxious can add a cubit to his lifespan?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
If then you are not able to do such a very little thing, why do you worry about the rest?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Consider the lilies—how they grow. They do not labor, neither do they spin. Yet I say to you, even Solomon in all his glory was not clothed like one of these.
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
If God so clothes the grass in the field, which exists today, and tomorrow is thrown into the oven, how much more will he clothe you, O you of little faith!
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
Do not look for what you will eat and what you will drink, and do not be anxious.
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
For all the nations of the world look for these things, and your Father knows that you need them.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
But seek his kingdom, and these things will be added to you.
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
Do not fear, little flock, because your Father is very pleased to give you the kingdom.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
Sell your possessions and give to the poor. Make for yourselves purses which will not wear out—treasure in the heavens that does not run out, where no thief comes near, and no moth destroys.
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
For where your treasure is, there your heart will be also.
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Let your long clothing be tucked in at your belt, and let your lamps be kept burning,
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
and be like people looking for their master when he returns from the marriage feast, so that when he comes and knocks, they may immediately open the door for him.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Blessed are those servants whom the master will find watching when he comes. Truly I say to you, he will tuck in his long clothing at his belt, and have them sit down at the table, and he will come and serve them.
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
If the master comes in the second watch of the night, or if even in the third watch, and finds them ready, blessed are those servants.
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
But understand this, that if the master of the house had known the hour the thief was coming he would not have let his house be broken into.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Be ready also, because you do not know the hour when the Son of Man comes.”
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
Peter said, “Lord, are you telling this parable only to us, or also to everyone?”
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
The Lord said, “Who then is the faithful and wise manager whom his lord will set over his other servants to give them their portion of food at the right time?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Blessed is that servant whom his lord finds doing that when he comes.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
Truly I say to you that he will set him over all his property.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
But if that servant says in his heart, 'My lord delays his return,' and begins to beat the male and female servants, and to eat and drink, and to become drunk,
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
the lord of that servant will come in a day when he does not expect, and in an hour that he does not know, and will cut him in pieces and appoint a place for him with the unfaithful.
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
That servant, having known his lord's will, and not having prepared or done according to his will, will be beaten with many blows.
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
But the one who did not know and did what deserved a beating, he will be beaten with a few blows. But everyone who has been given much, from them much will be required, and the one who has been entrusted with much, even more will be asked.
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
I came to cast fire upon the earth, and how I wish that it were already kindled.
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
But I have a baptism to be baptized with, and how I am distressed until it is completed!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Do you think that I came to bring peace on the earth? No, I tell you, but rather division.
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
For from now on there will be five in one house divided—three people against two, and two people against three.
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
They will be divided, father against son, and son against father; mother against daughter, and daughter against mother; mother-in-law against her daughter-in-law, and daughter-in-law against mother-in-law.”
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
Jesus was saying to the crowds also, “When you see a cloud rising in the west, immediately you say, 'A shower is coming,' and so it happens.
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
When a south wind is blowing, you say, 'There will be a scorching heat,' and it happens.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
Hypocrites, you know how to interpret the appearance of the earth and the heavens, but how is it that you do not know how to interpret the present time?
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Why do you not judge what is right for yourselves?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
For when you go with your adversary before the magistrate, on the way make an effort to settle the matter with him so that he does not drag you to the judge, and so that the judge does not deliver you to the officer, and the officer does not throw you into prison.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
I say to you, you will never come out from there until you have paid the very last bit of money.”

< Luka 12 >