< Luka 12 >
1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
In the meantime, myriads of the multitude having gathered together, So that they trode on one another, He began to speak to His disciples first; Take heed unto yourselves from the leaven of the Pharisees, which is hypocrisy.
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
But there is nothing hidden, which shall not be revealed: and concealed, that shall not be made known.
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
Therefore so many things as you spoke in the darkness shall be heard in the light; and whatsoever you spoke in the ear in the secret chambers shall be proclaimed upon the houses.
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
And I say unto you, my friends, Be not afraid of those killing the body, and after these things, having nothing more to do.
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna )
But I will show you whom you must fear: Fear him, who after he kills has power to cast into hell. Yea, I say unto you, Fear him. (Geenna )
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Are not five sparrows sold for two pennies? and one of them is not forgotten before God.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
But even the hairs of your head are all numbered. Fear not: ye are more important than many sparrows.
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
But I say unto you, that every one who may confess me before the people, the Son of man will also confess him before the angels of God.
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
But the one denying me before the people will be denied before the angels of God.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
And every one who shall speak a word against the Son of man, it shall be forgiven him: but to him having blasphemed against the Holy Ghost, it shall not be forgiven.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
But when they may carry you into the synagogues, and tribunals, and authorities; do not be solicitous as to what you may apologize, or what you may say:
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
for the Holy Spirit will teach you in that hour the things which it behooveth you to speak.
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
And a certain one from the multitude said to Him, Teacher, speak to my brother, to divide the inheritance with me.
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
And He said to him; Man, who established me judge or a divider over you?
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
And He said to them, See, and beware of all covetousness: because his life is not in that which aboundeth to any one, from those things belonging to him.
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
He spake a parable to them, saying, The farm of a certain rich man was very productive:
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
and he was reasoning in himself, saying, What shall I do, because I have no place where I shall store my fruits?
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
And he said, I will do this: I will take down my barns, and build greater, and there I will gather all my fruits and my goods.
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
And I will say to my soul, Soul, thou hast much goods laid up for many years; take thine ease, eat, drink, be merry.
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
But God said to him, Thou fool, this night they are demanding thy soul from thee; and to whom shall those things which thou hast prepared, belong?
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
So is every one laying up treasure for himself, and not rich toward God.
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
And He spoke to His disciples, Therefore I say unto you, Be not solicitous for your soul, what you may eat; nor for your body, what you may put on.
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
The soul is more than food, and the body more than raiment.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Observe the ravens, because they neither sow nor reap; to which there is no storehouse nor barn, and God feeds them; are you not much better than the fowls?
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
And which one of you being solicitous is able to add one moment to his existence?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
If then you are powerless in the smallest matter, why are you solicitous about other things?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Observe the lilies, how they toil not, neither do they spin: and I say unto you, That Solomon in all his glory was not arrayed as one of these.
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
And if God so clothes the verdure flourishing in the fields to-day, and to-morrow cast into the oven; how much more are you, O ye of little faith?
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
And do not seek what you may eat, and what you may drink, and with what you are clothed;
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
for the heathens of the world are seeking after all these things: but your Father knows that you have need of these things.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
Moreover seek His kingdom and these things shall be added unto you.
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
Fear not, little flock; because your Father is well pleased to give you the kingdom.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
Sell your possessions and give alms; make for yourselves purses that will not get old, and treasure in the heavens which can not be stolen, where the thief does not draw nigh, nor the moth corrupt.
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
For where your treasure is, there your heart will be.
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Let your loins be girted, and your lamps burning;
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
and be you like unto men waiting for their lord, when he may rise up from the marriage feast; in order that, coming and knocking, they may open unto him immediately.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Blessed are those servants, whom the lord having come will find watching: truly I say unto you, that he will gird himself, and have them sit down, and having come will serve them.
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
If at the second, and third, watch he may come, happy are ye.
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
Know this, that if the landlord knew at what hour the thief cometh, he would not have permitted his house to be broken into.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Be ye also ready: because at an hour you do not think the Son of man cometh.
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
And Peter said to Him, Lord, do you speak this parable to us, or to all?
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
The Lord said, Who then is the faithful, wise steward, whom the lord will establish over his house-hold, to give them their food in season?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Happy is that servant, whom his lord having come shall thus find watching.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
Truly I say unto you, that he will establish him over all his possessions.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
But if that servant may say in his heart, my lord delayeth his coming, and may begin to smite the servants and handmaidens, and to eat and drink, and be drunken;
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
the lord of that servant will come in a day in which he does not expect, and in an hour in which he does not know, and will cut him off, and will appoint his part with the unbelievers.
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
But that servant knowing the will of his lord, and not preparing or doing according to his will, shall be beaten with many stripes.
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
But the one not knowing, and doing things worthy of stripes, shall be beaten with few. But to every one to whom much is given, much will be required of him: and to whom they commit much, of him they will ask the more.
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
I have come to send fire on the earth; and what do I will, if it is already kindled?
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
And I have a baptism to be baptized with; and how am I straitened till it may be perfected!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Do you think that I have come to give peace on the earth? I say unto you, Nay, but division.
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
For from now, there shall be five in one house divided, three shall be divided against two, and two against three:
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
the father against the son, and the son against the father; and the mother against the daughter, and the daughter against the mother; the mother-in-law against the daughter-in-law, and the daughter-in-law against the mother-in-law.
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
And he also spoke to the multitudes, When you may see a cloud rising from the west, you immediately say, that the rain cometh; and it is so:
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
and when the south wind is blowing, you say, that it will be hot; and it is so.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
You hypocrites, you know how to discern the face of the earth and the firmament; and how do you not discern this time?
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Why do you not judge righteous judgment, even with reference to yourselves?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
For as you go with your adversary to the ruler, give attention on the way that you be reconciled with him; lest he may deliver you to the judge, and the judge shall turn you over to the officer, and the officer will cast you into prison.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
I say unto you, You can by no means come out thence, till you have even paid the last mite.