< Luka 12 >

1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
Da imidlertid mange Tusinde Mennesker havde samlet sig, så at de trådte på hverandre, begyndte han at sige til sine Disciple: "Tager eder først og fremmest i Vare for Farisæernes Surdejg, som er Hykleri.
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
Men intet er skjult, som jo skal åbenbares, og intet er lønligt, som jo skal blive kendt.
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
Derfor, alt hvad I have sagt i Mørket, skal høres i Lyset; og hvad I have talt i Øret i Kamrene, skal blive prædiket på Tagene.
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
Men jeg siger til eder, mine Venner! frygter ikke for dem, som slå Legemet ihjel og derefter ikke formå at gøre mere.
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
Men jeg vil vise eder, for hvem I skulle frygte: Frygter for ham, som har Magt til, efter at have slået ihjel, at kaste i Helvede; ja, jeg siger eder: Frygter for ham! (Geenna g1067)
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Sælges ikke fem Spurve for to Penninge? og ikke een af dem er glemt hos Gud.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
Ja, endog Hårene på eders Hoved ere alle talte; frygter ikke, I ere mere værd end mange Spurve.
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
Men jeg siger eder: Enhver, som vedkender sig mig for Menneskene, ham vil også Menneskesønnen vedkende sig for Guds Engle.
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
Og den, som har fornægtet mig for Menneskene, skal fornægtes for Guds Engle.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Og enhver, som taler et Ord imod Menneskesønnen, ham skal det forlades; men den, som har talt bespotteligt imod den Helligånd, ham skal det ikke forlades.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
Men når de føre eder frem for Synagogerne og Øvrighederne og Myndighederne, da bekymrer eder ikke for, hvorledes eller hvormed I skulle forsvare eder, eller hvad I skulle sige.
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
Thi den Helligånd skal lære eder i den samme Time, hvad I bør sige."
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
Men en af Skaren sagde til ham: "Mester! sig til min Broder, at han skal dele Arven med mig."
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
Men han sagde til ham: "Menneske! hvem har sat mig til Dommer eller Deler over eder?"
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
Og han sagde til dem: "Ser til og vogter eder for al Havesyge; thi ingens Liv beror på, hvad han ejer, selv om han har Overflod."
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
Og han sagde en Lignelse til dem: "Der var en rig Mand, hvis Mark havde båret godt.
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
Og han tænkte ved sig selv og sagde: Hvad skal jeg gøre? thi jeg har ikke Rum, hvori jeg kan samle min Afgrøde.
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
Og han sagde: Dette vil jeg gøre, jeg vil nedbryde mine Lader og bygge dem større, og jeg vil samle deri al min Afgrøde og mit Gods;
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
og jeg vil sige til min Sjæl: Sjæl! du har mange gode Ting liggende for mange År; slå dig til Ro, spis, drik, vær lystig!
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
Men Gud sagde til ham: Du Dåre! i denne Nat kræves din Sjæl af dig; men hvem skal det høre til. som du har beredt?
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
Således er det med den, som samler sig Skatte og ikke er rig i Gud."
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
Men han sagde til sine Disciple: "Derfor siger jeg eder: Bekymrer eder ikke for Livet, hvad I skulle spise; ikke heller for Legemet, hvad I skulle iføre eder.
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
Livet er mere end Maden, og Legemet mere end Klæderne.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Giver Agt på Ravnene, at de hverken så eller høste og de have ikke Forrådskammer eller Lade, og Gud føder dem; hvor langt mere værd end Fuglene ere dog I?
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
Og hvem af eder kan ved at bekymre sig lægge en Alen til sin Vækst?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
Formå I altså ikke engang det mindste, hvorfor bekymre I eder da for det øvrige?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Giver Agt på Lillierne, hvorledes de vokse; de arbejde ikke og spinde ikke; men jeg siger eder: End ikke Salomon i al sin Herlighed var klædt som en af dem.
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
Klæder da Gud således det Græs på Marken, som i Dag står og i Morgen kastes i Ovnen, hvor meget mere eder, I lidettroende!
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
Og I, spørger ikke efter, hvad I skulle spise, og hvad I skulle drikke; og værer ikke ængstelige!
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
Thi efter alt dette søge Hedningerne i Verden; men eders Fader ved, at I have disse Ting nødig.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
Men søger hans Rige, så skulle disse Ting gives eder i Tilgift.
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
Frygt ikke, du lille Hjord! thi det var eders Fader velbehageligt at give eder Riget.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
Sælger, hvad I eje, og giver Almisse! Gører eder Punge, som ikke ældes, en Skat i Himlene, som ikke slipper op, der hvor ingen Tyv kommer nær, og intet Møl ødelægger.
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
Thi hvor eders Skat er, der vil også eders Hjerte være.
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Eders Lænder være omgjordede, og eders Lys brændende!
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
Og værer I ligesom Mennesker, der vente på deres Herre, når han vil bryde op fra Brylluppet, for at de straks, når han kommer og banker på, kunne lukke op for ham.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Salige ere de Tjenere, som Herren finder vågne, når han kommer. Sandelig, siger jeg eder, at han skal binde op om sig og sætte dem til Bords og gå om og varte dem op,
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
Og dersom han kommer i den anden Nattevagt og kommer i den tredje Nattevagt og finder det således, da ere disse Tjenere salige.
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
Men dette skulle I vide, at dersom Husbonden vidste, i hvilken Time Tyven vilde komme, da vågede han og tillod ikke, at der skete Indbrud i hans Hus.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Vorder også I rede; thi Menneskesønnen kommer i den Time, som I ikke mene."
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
Men Peter sagde til ham: "Herre! siger du denne Lignelse til os eller også til alle?"
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
Og Herren sagde: "Hvem er vel den tro og forstandige Husholder, som Herren vil sætte over sit Tyende til at give dem den bestemte Kost i rette Tid?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Salig er den Tjener, hvem hans Herre, når han kommer, finder handlende således.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
Sandelig, siger jeg eder, han skal sætte ham over alt, hvad han ejer.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
Men dersom hin Tjener siger i sit Hjerte: "Min Herre tøver med at komme" og så begynder at slå Karlene og Pigerne og at spise og drikke og beruse sig,
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
da skal den Tjeners Herre komme på den Dag, han ikke venter, og i den Time, han ikke ved, og hugge ham sønder og give ham hans Lod sammen med de utro:
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
Men den Tjener, som har kendt sin Herres Villie og ikke har truffet Forberedelser eller handlet efter hans Villie, skal have mange Hug;
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
men den, som ikke har kendt den og har gjort, hvad der er Hug værd, skal have få Hug. Enhver, hvem meget er givet, af ham skal man kræve meget; og hvem meget er betroet, af ham skal man forlange mere.
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
Ild er jeg kommen at kaste på Jorden, og hvor vilde jeg, at den var optændt allerede!
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
Men en Dåb har jeg at døbes med, og hvor ængstes jeg, indtil den er fuldbyrdet!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Mene I, at jeg er kommen for at give Fred på Jorden? Nej, siger jeg eder, men Splid,
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
Thi fra nu af skulle fem i eet Hus være i Splid indbyrdes, tre imod to, og to imod tre.
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
De skulle være i Splid, Fader med Søn og Søn med Fader, Moder med Datter og Datter med Moder, Svigermoder med sin Svigerdatter og Svigerdatter med sin Svigermoder."
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
Men han sagde også til Skarerne: "Når I se en Sky komme op i Vester, sige I straks: Der kommer Regn, og det sker således.
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
Og når I se en Søndenvind blæse, sige I: Der kommer Hede: og det sker.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
I Hyklere! Jordens og Himmelens Udseende vide I at skønne om; men hvorfor have I da intet Skøn om den nærværende Tid?
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Og hvorfor dømme I ikke også fra eder selv, hvad der er det rette?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
Thi medens du går hen med din Modpart til Øvrigheden, da gør dig Flid på Vejen for at blive forligt med ham, for at han ikke skal trække dig for Dommeren, og Dommeren skal overgive dig til Slutteren, og Slutteren skal kaste dig i Fængsel.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
Jeg siger dig: Du skal ingenlunde komme ud derfra, førend du får betalt endog den sidste Skærv."

< Luka 12 >