< Luka 11 >

1 Wata rana Yesu yana addu’a a wani wuri. Da ya gama, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Ubangiji, ka koya mana yin addu’a, kamar yadda Yohanna ya koya wa almajiransa.”
І сталось, як молився Він у місці одно́му, і коли перестав, озвався до Нього один із Його у́чнів: „Господи, навчи нас молитися, як і Іван навчив своїх учнів.“
2 Sai ya ce musu, “Sa’ad da kuke yin addu’a ku ce, “‘Ya Uba, sunanka mai tsarki ne mulkinka ya zo.
Він же промовив до них: „Коли молитеся, говоріть: „Отче наш, що на небі! Нехай святиться Ім'я́ Твоє, нехай при́йде Царство Твоє, нехай бу́де воля Твоя, як на небі, так і на землі.
3 Ka ba mu kowace rana abincin yini.
Хліба нашого щоденного дай нам на кожний день.
4 Ka gafarta mana zunubanmu, kamar yadda mu ma ke gafarta wa duk wanda ya yi mana laifi. Kada ka bari a kai mu cikin jarraba.’”
І прости нам наші гріхи́, бо й самі ми прощаємо кожному боржнико́ві нашому. І не введи нас у випробо́вування, але визволи нас від лукавого!“
5 Sa’an nan ya ce musu, “Da a ce ɗayanku yana da aboki, sa’an nan ya je wurinsa da tsakar dare ya ce, ‘Aboki, ranta mini burodi guda uku,
І сказав Він до них: „Хто з вас матиме при́ятеля, і пі́де до нього опі́вночі, і скаже йому: „Позич мені, друже, три хліби́,
6 domin wani abokina da yake tafiya ya sauka a wurina. Ga shi, ba ni da abinci da zan ba shi.’
бо прийшов із дороги до мене мій при́ятель, я ж не маю, що́ дати йому“.
7 Sai wanda yake cikin ɗaki ya amsa ya ce, ‘Kada ka dame ni. An riga an kulle ƙofa, da ni da yarana kuwa mun kwanta, ba zan iya tashi in ba ka kome ba.’
А той із сере́дини в відповідь скаже: „Не роби мені кло́поту, — уже за́мкнені двері, і мої діти зо мною на ліжкові. Не можу я встати та дати тобі“.
8 Ina gaya muku, ko da yake ba zai so ya tashi ya ba shi burodin don shi abokinsa ne ba, duk da haka, zai tashi ya ba shi yawan abin da yake bukata, saboda nacewarsa.
Кажу вам: коли він не встане, і не дасть ради дружби йому, то за докуча́ння його він устане та й дасть йому, скільки той потребу́є.
9 “Don haka ina faɗa muku, ku roƙa, za a ba ku, ku nema za ku samu, ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
І Я вам кажу́: просіть, — і буде вам да́но, шукайте — і знайдете, стукайте — і відчинять вам!
10 Gama duk wanda ya roƙa, yana karɓa, mai nema yana samu, wanda ya ƙwanƙwasa kuma, za a buɗe masa ƙofa.
Бо кожен, хто просить — одержує, хто шукає — знахо́дить, а тому́, хто стукає — відчинять.
11 “Wane mahaifi ne a cikinku, in ɗansa ya roƙe shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon,
І котри́й з вас, батьків, як син хліба проси́тиме, подасть йому каменя? Або, як проситиме риби, замість риби подасть йому га́дину?
12 ko kuma in ya roƙi ƙwai, ya ba shi kunama?
Або, як яйця́ він проситиме, дасть йому скорпіо́на?
13 In fa haka ne, ko da yake ku mugaye ne, kun san ba’ya’yanku kyautai masu kyau, balle fa Ubanku na sama, zai yi fiye da haka, ta wurin ba da Ruhu Mai Tsarki, ga masu roƙonsa!”
Отож, коли ви, бувши злі, потра́пите добрі дари́ своїм дітям давати, — скільки ж більше Небесний Отець подасть Духа Святого всім тим, хто проситиме в Нього?“
14 Sa’ad da Yesu yake fitar da wani beben aljani daga wani mutum, da aljanin ya fita, sai mutumin wanda da bebe ne, ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki.
Раз виго́нив Він де́мона, який був німий. І коли демон вийшов, німий заговорив. А наро́д дивувався.
15 Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Be’elzebub, sarkin aljanu ne, yake fitar da aljanu.”
А деякі з них гомоніли: „Виганяє Він де́монів силою Вельзеву́ла, князя де́монів“.
16 Waɗansu kuma suka gwada shi, ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
А інші, випробовуючи, хотіли від Нього ознаки із неба.
17 Yesu kuwa ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa, zai lalace, kuma gidan da yake gaba da kansa zai rushe.
Він же знав думки їхні, і промовив до них: „Кожне царство, само проти себе поді́лене, запусті́є, і дім на дім упаде́.
18 In Shaiɗan yana gāba da kansa, yaya mulkinsa zai tsaya? Ina faɗin haka domin kun ce, da ikon Be’elzebub nake fitar da aljanu.
А коли й сатана́ поділився сам супроти себе, — як стоятиме царство його? А ви кажете, що Вельзеву́лом виго́ню Я демонів.
19 In da ikon Be’elzebub nake fitar da su, to, da ikon wa masu binku suke fitar da su? Saboda haka, za su zama alƙalanku ke nan.
Коли ж Вельзеву́лом виго́ню Я демонів, то чим виганяють їх ваші сини? Тому вони стануть вам су́ддями.
20 Amma in da ikon Allah ne ni nake fitar da aljanu, ashe, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
А коли пальцем Божим виго́ню Я де́монів, то справді прийшло до вас Боже Царство.
21 “Sa’ad da mutum mai ƙarfi, wanda yake da makamai yana gadin gidan kansa, an tsare lafiyar dukiyarsa ke nan.
Коли сильний збройно свій двір стереже, то в безпе́ці маєток його.
22 Amma in wani wanda ya fi shi ƙarfi, ya faɗa masa ya kuma sha ƙarfinsa, yakan ƙwace makaman da mutumin ke dogara da su, ya kuma rarraba ganima.
Коли ж дужчий від нього його нападе́ й переможе, то всю збро́ю йому забере́, на яку покладався був той, і роздасть свою здо́бич.
23 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni, wanda kuma ba ya tarawa da ni, watsarwa yake yi.
Хто не зо Мною, той проти Мене; і хто не збирає зо Мною, той розкидає!
24 “Lokacin da mugun ruhu ya fita daga mutum, sai ya bi ta wuraren da ba mutane, yana neman hutu, amma ya kāsa samu, sai ya ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’
Коли дух нечистий виходить з люди́ни, то блукає місцями безві́дними, відпочинку шукаючи, але, не знахо́дячи, каже: „Верну́ся до хати своєї, звідки я вийшов“.
25 Sa’ad da ya koma, ya tarar da gidan a share da tsabta, kuma a shirye.
А як ве́рнеться він, то хату знахо́дить заме́тену й при́брану.
26 Sai ya je ya ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, sai su shiga su zauna a wurin. Ƙarshen wannan mutum kuwa zai fi farkonsa muni.”
Тоді він іде та й приводить сімох інших духів, лютіших за себе, — і входять вони та й живуть там. І буде останнє люди́ні тій гірше за перше!“
27 Da Yesu yake cikin faɗin waɗannan abubuwa, sai wata mace daga cikin taron ta ɗaga murya ta ce masa, “Mai albarka ce uwar da ta haife ka, wadda ka sha mamanta.”
І сталось, як Він це говорив, одна жінка з народу свій голос підне́сла й сказала до Нього: „Блаженна утро́ба, що носила Тебе, і груди, що Ти ссав їх!“
28 Yesu ya amsa ya ce, “A maimakon, masu albarka ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma biyayya da ita.”
А Він відказав: „Так. Блаженні ж і ті, хто слухає Божого Слова і його береже́!“
29 Da taron mutane suka ƙaru, sai Yesu ya ce, “Wannan mugun zamani ne. Tana neman wani abin banmamaki, amma ba ko ɗaya da za a ba ta, sai dai ta Yunana.
А як люди збира́лися, Він почав промовляти: „Рід цей — рід лукавий: він ознаки шукає, та ознаки йому не дадуть, крім ознаки проро́ка Йо́ни.
30 Kamar yadda Yunana ya zama alama ga mutanen Ninebe, haka ma Ɗan Mutum zai zama ga zamanin nan.
Бо як Йо́на ознакою був для ніневі́тян, так буде й Син Лю́дський для роду цього́.
31 A ranar shari’a, Sarauniyar Kudu za tă tashi tsaye tare da wannan zamani, ta yanke wa wannan zamani hukunci, domin ta zo daga ƙarshen duniya ta saurari hikimar Solomon, ga shi kuwa, shi wanda ya fi Solomon girma, na nan.
Цариця півде́нна на суд стане з му́жами роду цього́, — і їх засудить, бо вона з кінця світу прийшла Соломо́нову мудрість послухати. А тут ось Хтось більший, аніж Соломо́н!
32 A ranar shari’a, mutanen Ninebe za su tashi tsaye tare da wannan zamani, su yanke wa wannan zamani hukunci. Gama sun tuba sa’ad da Yunana ya yi musu wa’azi. Ga shi yanzu, shi wanda ya fi Yunana girma, na nan.
Ніневі́тяни стануть на суд із цим родом, — і засудять його, вони бо пока́ялися через Йонину проповідь. А тут ось Хтось більший, ніж Йона!
33 “Babu wanda yakan ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta, ko ya rufe ta da murfi ba. A maimako, yakan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, don masu shiga su ga haske.
Засвіченого світла ніхто в схо́вок не ставить, ані під посу́дину, але на світи́льника, щоб бачили світло, хто входить.
34 Idonka shi ne fitilar jikinka. Sa’ad da idanunka suna da lafiya, dukan jikinka ma na cike da haske, amma sa’ad da idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma na cike da duhu.
Око твоє — то світи́льник для тіла; тому́, як око твоє буде дуже, то й усе тіло твоє буде світле. А коли б твоє око нездатне було́, то й усе тіло твоє буде темне.
35 Ka lura fa, kada hasken da yake cikinka ya zamana duhu ne.
Отож, уважай, щоб те світло, що в тобі, не сталося те́мрявою!
36 Saboda haka, in dukan jikinka yana cike da haske, ba inda ke da duhu, jikinka kuwa zai kasance da haske gaba ɗaya, kamar yadda hasken fitila yake haskaka ka.”
Бо коли твоє тіло все світле, і не має жа́дної темної частини, то все буде світле, неначе б світильник ося́яв блиском тебе“.
37 Da Yesu ya gama magana, sai wani Bafarisiye ya gayyace shi cin abinci tare da shi. Sai kuwa ya shiga ya zauna a tebur.
Коли Він говорив, то один фарисей став благати Його пообідати в нього. Він же прийшов та й сів при столі.
38 Amma Bafarisiyen ya lura cewa, Yesu bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba, sai mamaki ya kama shi.
Фарисей же, побачивши це, здивувався, що перед обідом Він перш не обмився.
39 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ku Farisiyawa, kukan wanke bayan kwano da kwaf, amma a ciki kuna cike da kwaɗayi da mugunta.
Господь же промовив до нього: „Тепер ви, фарисеї, он чистите зо́внішність ку́хля та миски, а ваше нутро́ повне зди́рства та кривди!
40 Ku wawayen mutane! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ne kuma ya yi cikin ba?
Нерозумні, — чи ж Той, Хто створив оте зо́внішнє, не створив Він і внутрішнє?
41 Ku ba matalauta abin da yake cikin kwano, kuma kome zai zama muku da tsabta.
Тож милостиню подавайте з унутрішнього, — і ось все буде вам чисте.
42 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kuna ba wa Allah zakka na na’ana’arku, da ƙarƙashinku, da kuma sauran ganyen lambunku iri-iri, amma kun ƙyale adalci da ƙaunar Allah. Ya kamata da kun kiyaye na ƙarshen, ban ba barin na farkon.
Горе вам, фарисеям, — бо ви десятину даєте з м'яти та рути й усякого зілля, але обминаєте суд та Божу любов; це треба робити, і того́ не лишати!
43 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kun cika son wuraren zama masu daraja a majami’u, da kuma yawan gaisuwa a wuraren kasuwanci.
Горе вам, фарисеям, що любите перші лавки́ в синагогах та привіти на ри́нках!
44 “Kaitonku, domin ku kamar kaburbura ne da ba a sa musu alama ba, waɗanda mutane suke takawa don rashin sani.”
Горе вам, — бо ви як гроби́ непомітні, — люди ж ходять по них і не знають того“.
45 Sai ɗaya daga cikin masanan dokoki ya ce wa Yesu, “Malam, in ka faɗi waɗannan abubuwa haka, kai kuma ka zage mu ke nan.”
Озвався ж один із зако́нників, і каже Йому: „Учителю, кажучи це, Ти і нас ображаєш!“
46 Yesu ya amsa ya ce, “Ku masanan dokoki ma, kaitonku, domin kun ɗora wa mutane kaya masu nauyi waɗanda da ƙyar suke ɗaukawa, amma ku da kanku ba za ku sa ko yatsa ɗaya, don ku taimake su ba.
А Він відказав: „Горе й вам, зако́нникам, бо ви на людей тягарі́ накладаєте, які важко носити, а самі й одним пальцем своїм не дото́ркуєтесь тягарі́в!
47 “Kaitonku, domin kun gina kaburbura saboda annabawa, nan kuwa kakannin-kakanninku ne suka kashe su.
Горе вам, бо надгро́бки пророкам ви ставите, — ваші ж батьки́ були їх повбивали.
48 Wannan ya shaida cewa kun amince da abin da kakannin-kakanninku suka yi. Sun karkashe annabawa, ku kuma kun gina kaburburansu.
Так, — визнаєте ви й хвалите вчинки батьків своїх: бо вони їх повбивали, а ви їм надгро́бки будуєте!
49 Saboda haka, Allah a cikin hikimarsa ya ce, ‘Zan aika musu da annabawa da manzanni. Za su kashe waɗansu, su kuma tsananta wa waɗansu.’
Через те й мудрість Божа сказала: „Я пошлю їм пророків й апо́столів, — вони ж декого з них повбивають, а декого ви́женуть,
50 Saboda haka, alhakin jinin dukan annabawa da aka kashe, tun farkon duniya, yana kan wannan zamani,
щоб на роді оцім відомстилася кров усіх пророків, що пролита від ство́рення світу,
51 wato, tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya, wanda aka kashe tsakanin bagade da mazauni. I, ina gaya muku, alhakinsu duka yana kan wannan zamani.
від крови Авеля аж до крови Заха́рія, що загинув між же́ртівником і храмом“! Так, кажу вам, — відомсти́ться це все на цім роді!
52 “Kaitonku, masanan dokoki, domin kun ɗauke mabuɗin ilimi. Ku kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana wa waɗanda suke shiga, su shiga.”
Горе вам, зако́нникам, бо взяли́ ви ключа́ розумі́ння: самі не ввійшли, і тим, хто хотів увійти, борони́ли!“
53 Da Yesu ya bar wurin, sai Farisiyawa da malaman dokoki suka fara gaba mai tsanani da shi, kuma suna tsokanansa da tambayoyi.
А коли Він вихо́див ізвідти, стали книжники та фарисеї сильно тиснути та від Нього допитуватись про багато речей, —
54 Suna fakonsa, don su kama shi a kan wata magana da zai faɗa.
вони чатува́ли на Нього, щоб зловити що з уст Його (і щоб оска́ржити Його́).

< Luka 11 >