< Luka 11 >
1 Wata rana Yesu yana addu’a a wani wuri. Da ya gama, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Ubangiji, ka koya mana yin addu’a, kamar yadda Yohanna ya koya wa almajiransa.”
Cuando terminó de orar en un lugar, uno de sus discípulos le dijo: “Señor, enséñanos a orar, como también Juan enseñó a sus discípulos.”
2 Sai ya ce musu, “Sa’ad da kuke yin addu’a ku ce, “‘Ya Uba, sunanka mai tsarki ne mulkinka ya zo.
Les dijo: “Cuando oréis, decid, ‘Padre nuestro que estás en el cielo’, que tu nombre sea sagrado. Que venga tu Reino. Que se haga tu voluntad en la tierra, como en el cielo.
3 Ka ba mu kowace rana abincin yini.
Danos cada día el pan de cada día.
4 Ka gafarta mana zunubanmu, kamar yadda mu ma ke gafarta wa duk wanda ya yi mana laifi. Kada ka bari a kai mu cikin jarraba.’”
Perdona nuestros pecados, porque nosotros también perdonamos a todos los que están en deuda con nosotros. No nos dejes caer en la tentación, pero líbranos del maligno”.
5 Sa’an nan ya ce musu, “Da a ce ɗayanku yana da aboki, sa’an nan ya je wurinsa da tsakar dare ya ce, ‘Aboki, ranta mini burodi guda uku,
Les dijo: “¿Quién de vosotros, si va a un amigo a medianoche y le dice: “Amigo, préstame tres panes,
6 domin wani abokina da yake tafiya ya sauka a wurina. Ga shi, ba ni da abinci da zan ba shi.’
porque un amigo mío ha venido de viaje y no tengo nada que ponerle delante”,
7 Sai wanda yake cikin ɗaki ya amsa ya ce, ‘Kada ka dame ni. An riga an kulle ƙofa, da ni da yarana kuwa mun kwanta, ba zan iya tashi in ba ka kome ba.’
y él, desde dentro, le responde y le dice: “No me molestes. La puerta está cerrada y mis hijos están conmigo en la cama. No puedo levantarme y dárselo’?
8 Ina gaya muku, ko da yake ba zai so ya tashi ya ba shi burodin don shi abokinsa ne ba, duk da haka, zai tashi ya ba shi yawan abin da yake bukata, saboda nacewarsa.
Os digo que, aunque no se levante a dárselo porque es su amigo, por su insistencia se levantará y le dará todos los que necesite.
9 “Don haka ina faɗa muku, ku roƙa, za a ba ku, ku nema za ku samu, ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
“Os digo que sigáis pidiendo y se os dará. Sigan buscando y encontrarán. Seguid llamando, y se os abrirá.
10 Gama duk wanda ya roƙa, yana karɓa, mai nema yana samu, wanda ya ƙwanƙwasa kuma, za a buɗe masa ƙofa.
Porque todo el que pide recibe. El que busca encuentra. Al que llama se le abrirá.
11 “Wane mahaifi ne a cikinku, in ɗansa ya roƙe shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon,
“¿Quién de vosotros, padres, si su hijo le pide pan, le dará una piedra? O si le pide un pescado, acaso le dará una serpiente en lugar de un pescado, ¿verdad?
12 ko kuma in ya roƙi ƙwai, ya ba shi kunama?
O si le pide un huevo, no le dará un escorpión, ¿verdad?
13 In fa haka ne, ko da yake ku mugaye ne, kun san ba’ya’yanku kyautai masu kyau, balle fa Ubanku na sama, zai yi fiye da haka, ta wurin ba da Ruhu Mai Tsarki, ga masu roƙonsa!”
Si ustedes, siendo malos, saben dar buenos regalos a sus hijos, ¿cuánto más su Padre celestial dará el Espíritu Santo a los que se lo pidan?”
14 Sa’ad da Yesu yake fitar da wani beben aljani daga wani mutum, da aljanin ya fita, sai mutumin wanda da bebe ne, ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki.
Estaba expulsando a un demonio, y éste era mudo. Cuando el demonio salió, el mudo habló; y las multitudes se maravillaron.
15 Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Be’elzebub, sarkin aljanu ne, yake fitar da aljanu.”
Pero algunos de ellos decían: “Expulsa los demonios por Beelzebul, el príncipe de los demonios.”
16 Waɗansu kuma suka gwada shi, ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
Otros, poniéndole a prueba, pedían de él una señal del cielo.
17 Yesu kuwa ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa, zai lalace, kuma gidan da yake gaba da kansa zai rushe.
Pero él, conociendo sus pensamientos, les dijo: “Todo reino dividido contra sí mismo es asolado. Una casa dividida contra sí misma cae.
18 In Shaiɗan yana gāba da kansa, yaya mulkinsa zai tsaya? Ina faɗin haka domin kun ce, da ikon Be’elzebub nake fitar da aljanu.
Si también Satanás está dividido contra sí mismo, ¿cómo permanecerá su reino? Porque decís que yo expulso los demonios por Beelzebul.
19 In da ikon Be’elzebub nake fitar da su, to, da ikon wa masu binku suke fitar da su? Saboda haka, za su zama alƙalanku ke nan.
Pero si yo expulso los demonios por Beelzebul, ¿por quién los expulsan vuestros hijos? Por tanto, ellos serán vuestros jueces.
20 Amma in da ikon Allah ne ni nake fitar da aljanu, ashe, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
Pero si yo expulso los demonios por el dedo de Dios, entonces el Reino de Dios ha llegado a vosotros.
21 “Sa’ad da mutum mai ƙarfi, wanda yake da makamai yana gadin gidan kansa, an tsare lafiyar dukiyarsa ke nan.
“Cuando el hombre fuerte, completamente armado, vigila su propia morada, sus bienes están a salvo.
22 Amma in wani wanda ya fi shi ƙarfi, ya faɗa masa ya kuma sha ƙarfinsa, yakan ƙwace makaman da mutumin ke dogara da su, ya kuma rarraba ganima.
Pero cuando alguien más fuerte lo ataca y lo vence, le quita toda la armadura en la que confiaba y reparte su botín.
23 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni, wanda kuma ba ya tarawa da ni, watsarwa yake yi.
“El que no está conmigo está contra mí. El que no se reúne conmigo se dispersa.
24 “Lokacin da mugun ruhu ya fita daga mutum, sai ya bi ta wuraren da ba mutane, yana neman hutu, amma ya kāsa samu, sai ya ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’
El espíritu inmundo, cuando ha salido del hombre, pasa por lugares secos, buscando descanso; y al no encontrarlo, dice: ‘Me volveré a mi casa de donde salí’.
25 Sa’ad da ya koma, ya tarar da gidan a share da tsabta, kuma a shirye.
Cuando regresa, la encuentra barrida y ordenada.
26 Sai ya je ya ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, sai su shiga su zauna a wurin. Ƙarshen wannan mutum kuwa zai fi farkonsa muni.”
Entonces va y toma otros siete espíritus más malos que él, y entran y habitan allí. El último estado de ese hombre llega a ser peor que el primero”.
27 Da Yesu yake cikin faɗin waɗannan abubuwa, sai wata mace daga cikin taron ta ɗaga murya ta ce masa, “Mai albarka ce uwar da ta haife ka, wadda ka sha mamanta.”
Mientras decía estas cosas, una mujer de entre la multitud alzó la voz y le dijo: “¡Bendito sea el vientre que te llevó y los pechos que te amamantaron!”
28 Yesu ya amsa ya ce, “A maimakon, masu albarka ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma biyayya da ita.”
Pero él dijo: “Al contrario, bienaventurados los que escuchan la palabra de Dios y la guardan”.
29 Da taron mutane suka ƙaru, sai Yesu ya ce, “Wannan mugun zamani ne. Tana neman wani abin banmamaki, amma ba ko ɗaya da za a ba ta, sai dai ta Yunana.
Cuando las multitudes se reunieron con él, comenzó a decir: “Esta es una generación malvada. Busca una señal. No se le dará otra señal que la del profeta Jonás.
30 Kamar yadda Yunana ya zama alama ga mutanen Ninebe, haka ma Ɗan Mutum zai zama ga zamanin nan.
Porque así como Jonás fue una señal para los ninivitas, así también lo será el Hijo del Hombre para esta generación.
31 A ranar shari’a, Sarauniyar Kudu za tă tashi tsaye tare da wannan zamani, ta yanke wa wannan zamani hukunci, domin ta zo daga ƙarshen duniya ta saurari hikimar Solomon, ga shi kuwa, shi wanda ya fi Solomon girma, na nan.
La Reina del Sur se levantará en el juicio con los hombres de esta generación y los condenará, porque ha venido desde los confines de la tierra para escuchar la sabiduría de Salomón; y he aquí que uno más grande que Salomón está aquí.
32 A ranar shari’a, mutanen Ninebe za su tashi tsaye tare da wannan zamani, su yanke wa wannan zamani hukunci. Gama sun tuba sa’ad da Yunana ya yi musu wa’azi. Ga shi yanzu, shi wanda ya fi Yunana girma, na nan.
Los hombres de Nínive se levantarán en el juicio con esta generación y la condenarán, porque se arrepintieron ante la predicación de Jonás; y he aquí que uno más grande que Jonás está aquí.
33 “Babu wanda yakan ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta, ko ya rufe ta da murfi ba. A maimako, yakan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, don masu shiga su ga haske.
“Nadie, cuando ha encendido una lámpara, la pone en un sótano o debajo de un cesto, sino sobre un soporte, para que los que entren puedan ver la luz.
34 Idonka shi ne fitilar jikinka. Sa’ad da idanunka suna da lafiya, dukan jikinka ma na cike da haske, amma sa’ad da idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma na cike da duhu.
La lámpara del cuerpo es el ojo. Por eso, cuando tu ojo es bueno, todo tu cuerpo está también lleno de luz; pero cuando es malo, también tu cuerpo está lleno de oscuridad.
35 Ka lura fa, kada hasken da yake cikinka ya zamana duhu ne.
Mira, pues, si la luz que hay en ti no es oscuridad.
36 Saboda haka, in dukan jikinka yana cike da haske, ba inda ke da duhu, jikinka kuwa zai kasance da haske gaba ɗaya, kamar yadda hasken fitila yake haskaka ka.”
Si, pues, todo tu cuerpo está lleno de luz, sin que haya ninguna parte oscura, estará totalmente lleno de luz, como cuando la lámpara con su resplandor te alumbra.”
37 Da Yesu ya gama magana, sai wani Bafarisiye ya gayyace shi cin abinci tare da shi. Sai kuwa ya shiga ya zauna a tebur.
Mientras hablaba, un fariseo le pidió que cenara con él. Entró y se sentó a la mesa.
38 Amma Bafarisiyen ya lura cewa, Yesu bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba, sai mamaki ya kama shi.
Cuando el fariseo lo vio, se maravilló de que no se hubiera lavado antes de cenar.
39 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ku Farisiyawa, kukan wanke bayan kwano da kwaf, amma a ciki kuna cike da kwaɗayi da mugunta.
El Señor le dijo: “Ahora bien, vosotros, fariseos, limpiáis el exterior de la copa y del plato, pero vuestro interior está lleno de extorsión y de maldad.
40 Ku wawayen mutane! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ne kuma ya yi cikin ba?
Vosotros, insensatos, ¿no hizo también lo de dentro el que hizo lo de fuera?
41 Ku ba matalauta abin da yake cikin kwano, kuma kome zai zama muku da tsabta.
Pero dad por regalos a los necesitados lo que hay dentro, y he aquí que todo os quedará limpio.
42 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kuna ba wa Allah zakka na na’ana’arku, da ƙarƙashinku, da kuma sauran ganyen lambunku iri-iri, amma kun ƙyale adalci da ƙaunar Allah. Ya kamata da kun kiyaye na ƙarshen, ban ba barin na farkon.
Pero ¡ay de vosotros, fariseos! Porque diezmáis la menta y la ruda y toda hierba, pero dejáis de lado la justicia y el amor de Dios. Deberíais haber hecho esto, y no haber dejado de hacer lo otro.
43 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kun cika son wuraren zama masu daraja a majami’u, da kuma yawan gaisuwa a wuraren kasuwanci.
¡Ay de vosotros, fariseos! Porque amáis los mejores asientos en las sinagogas y los saludos en las plazas.
44 “Kaitonku, domin ku kamar kaburbura ne da ba a sa musu alama ba, waɗanda mutane suke takawa don rashin sani.”
¡Ay de vosotros, escribas y fariseos, hipócritas! Porque sois como sepulcros ocultos, y los hombres que andan sobre ellos no lo saben”.
45 Sai ɗaya daga cikin masanan dokoki ya ce wa Yesu, “Malam, in ka faɗi waɗannan abubuwa haka, kai kuma ka zage mu ke nan.”
Uno de los abogados le respondió: “Maestro, al decir esto también nos insultas”.
46 Yesu ya amsa ya ce, “Ku masanan dokoki ma, kaitonku, domin kun ɗora wa mutane kaya masu nauyi waɗanda da ƙyar suke ɗaukawa, amma ku da kanku ba za ku sa ko yatsa ɗaya, don ku taimake su ba.
Dijo: “¡Ay de ustedes, los abogados! Porque cargáis a los hombres con cargas difíciles de llevar, y vosotros mismos no levantáis ni un dedo para ayudar a llevar esas cargas.
47 “Kaitonku, domin kun gina kaburbura saboda annabawa, nan kuwa kakannin-kakanninku ne suka kashe su.
¡Ay de ustedes! Porque construís las tumbas de los profetas, y vuestros padres los mataron.
48 Wannan ya shaida cewa kun amince da abin da kakannin-kakanninku suka yi. Sun karkashe annabawa, ku kuma kun gina kaburburansu.
Así pues, vosotros dais testimonio y consentid en las obras de vuestros padres. Porque ellos los mataron, y vosotros construís sus tumbas.
49 Saboda haka, Allah a cikin hikimarsa ya ce, ‘Zan aika musu da annabawa da manzanni. Za su kashe waɗansu, su kuma tsananta wa waɗansu.’
Por eso también la sabiduría de Dios dijo: ‘Les enviaré profetas y apóstoles; y a algunos de ellos los matarán y perseguirán,
50 Saboda haka, alhakin jinin dukan annabawa da aka kashe, tun farkon duniya, yana kan wannan zamani,
para que la sangre de todos los profetas, que fue derramada desde la fundación del mundo, sea requerida de esta generación,
51 wato, tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya, wanda aka kashe tsakanin bagade da mazauni. I, ina gaya muku, alhakinsu duka yana kan wannan zamani.
desde la sangre de Abel hasta la sangre de Zacarías, que pereció entre el altar y el santuario.’ Sí, os digo que se exigirá a esta generación.
52 “Kaitonku, masanan dokoki, domin kun ɗauke mabuɗin ilimi. Ku kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana wa waɗanda suke shiga, su shiga.”
¡Ay de vosotros, abogados! Porque os habéis llevado la llave del conocimiento. Vosotros mismos no entrasteis, y a los que entraban, se lo impedisteis”.
53 Da Yesu ya bar wurin, sai Farisiyawa da malaman dokoki suka fara gaba mai tsanani da shi, kuma suna tsokanansa da tambayoyi.
Mientras les decía estas cosas, los escribas y los fariseos empezaron a enojarse terriblemente, y con vehemencia le hacían preguntas,
54 Suna fakonsa, don su kama shi a kan wata magana da zai faɗa.
acechándole y buscando sorprenderle en algo que pudiera decir, para acusarle.