< Luka 11 >

1 Wata rana Yesu yana addu’a a wani wuri. Da ya gama, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Ubangiji, ka koya mana yin addu’a, kamar yadda Yohanna ya koya wa almajiransa.”
有一天,耶稣在一个地方祈祷。祈祷结束后,有一个门徒问他说:“主啊,请教我们如何祈祷,就像约翰教导他的门徒一样。”
2 Sai ya ce musu, “Sa’ad da kuke yin addu’a ku ce, “‘Ya Uba, sunanka mai tsarki ne mulkinka ya zo.
耶稣说:“你们祷告的时候,要说:‘父啊,愿你的名被尊为神圣,愿你的国降临,
3 Ka ba mu kowace rana abincin yini.
请赐予我们每天需要的食物,
4 Ka gafarta mana zunubanmu, kamar yadda mu ma ke gafarta wa duk wanda ya yi mana laifi. Kada ka bari a kai mu cikin jarraba.’”
赦免我们的罪过,因为我们也宽恕了所有对我们犯下罪行之人,请保护我们不要被魔鬼试探。’”
5 Sa’an nan ya ce musu, “Da a ce ɗayanku yana da aboki, sa’an nan ya je wurinsa da tsakar dare ya ce, ‘Aboki, ranta mini burodi guda uku,
耶稣继续对他们说:“假设你半夜去找一个朋友,对他说‘请借给我三个饼,
6 domin wani abokina da yake tafiya ya sauka a wurina. Ga shi, ba ni da abinci da zan ba shi.’
因为我有一个朋友远行到此,我没有什么食物可以招待他。’
7 Sai wanda yake cikin ɗaki ya amsa ya ce, ‘Kada ka dame ni. An riga an kulle ƙofa, da ni da yarana kuwa mun kwanta, ba zan iya tashi in ba ka kome ba.’
但屋子里的朋友却回应说‘别打扰我了,我已经关好了门,和孩子都躺下了,不能起床给你拿食物。’
8 Ina gaya muku, ko da yake ba zai so ya tashi ya ba shi burodin don shi abokinsa ne ba, duk da haka, zai tashi ya ba shi yawan abin da yake bukata, saboda nacewarsa.
我告诉你们吧,尽管他不愿起床给你拿食物,只要你不断坚持,即使你不是他的朋友,他最终也会起来,把你要的东西拿给你。
9 “Don haka ina faɗa muku, ku roƙa, za a ba ku, ku nema za ku samu, ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
告诉你们吧,你要去求,自会获得;要去找,自会找到;要去叩门,门自会开。
10 Gama duk wanda ya roƙa, yana karɓa, mai nema yana samu, wanda ya ƙwanƙwasa kuma, za a buɗe masa ƙofa.
因为只要祈求都可以获得,只要寻觅都可找到,只要叩门就会将门打开。
11 “Wane mahaifi ne a cikinku, in ɗansa ya roƙe shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon,
如果你为人父,当你儿子想要鱼,你不可能给他蛇。
12 ko kuma in ya roƙi ƙwai, ya ba shi kunama?
如果儿子想要鸡蛋,你不可能给他蝎子。
13 In fa haka ne, ko da yake ku mugaye ne, kun san ba’ya’yanku kyautai masu kyau, balle fa Ubanku na sama, zai yi fiye da haka, ta wurin ba da Ruhu Mai Tsarki, ga masu roƙonsa!”
所以,即使你是邪恶的,如果你仍然知道给你的孩子好礼物,天父何况将圣灵赐给那些求他的人呢?”
14 Sa’ad da Yesu yake fitar da wani beben aljani daga wani mutum, da aljanin ya fita, sai mutumin wanda da bebe ne, ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki.
耶稣从一个人身上驱走恶鬼。这个人之前还是个哑巴,但现在可以说话了,众人都感到惊讶万分。
15 Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Be’elzebub, sarkin aljanu ne, yake fitar da aljanu.”
有人说耶稣:“他用的是魔鬼之王别西卜的力量驱鬼。”
16 Waɗansu kuma suka gwada shi, ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
又有人想要试探耶稣,要求他显化一个来自天堂的神迹。
17 Yesu kuwa ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa, zai lalace, kuma gidan da yake gaba da kansa zai rushe.
耶稣知道他们在想什么,就对他们说:“如果一个国家内战不断,必会分崩离析,如果一个家庭彼此争斗,必然败落。
18 In Shaiɗan yana gāba da kansa, yaya mulkinsa zai tsaya? Ina faɗin haka domin kun ce, da ikon Be’elzebub nake fitar da aljanu.
如果撒旦内部彼此为敌,他的王国怎能持久?你们居然说我是靠撒旦的力量驱鬼。
19 In da ikon Be’elzebub nake fitar da su, to, da ikon wa masu binku suke fitar da su? Saboda haka, za su zama alƙalanku ke nan.
如果真是如此,给自己人驱鬼又要靠谁的力量呢?他们自己就会评判你是错误的。
20 Amma in da ikon Allah ne ni nake fitar da aljanu, ashe, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
我若靠上帝的能力驱鬼,这就代表上帝之国已经降临,就在你们之中。
21 “Sa’ad da mutum mai ƙarfi, wanda yake da makamai yana gadin gidan kansa, an tsare lafiyar dukiyarsa ke nan.
一个壮汉全副武装地看守自己的房屋,让自己的家财保持安全。
22 Amma in wani wanda ya fi shi ƙarfi, ya faɗa masa ya kuma sha ƙarfinsa, yakan ƙwace makaman da mutumin ke dogara da su, ya kuma rarraba ganima.
但如果来了比他更强的人,打败他,夺去他所依赖的武器,就会抢走他的所有财产。
23 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni, wanda kuma ba ya tarawa da ni, watsarwa yake yi.
如果你没有与我站在一起,就是反对我。没有和我一起修建楼宇之人,楼宇就会倒塌。
24 “Lokacin da mugun ruhu ya fita daga mutum, sai ya bi ta wuraren da ba mutane, yana neman hutu, amma ya kāsa samu, sai ya ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’
一个恶灵从人体中被驱赶出来,走遍沙漠,寻找栖身之所,却没有找到。于是就说:‘我要回到我之前离开的那房子。’
25 Sa’ad da ya koma, ya tarar da gidan a share da tsabta, kuma a shirye.
它回到老屋后,看见里面已经打扫干净,整整齐齐,
26 Sai ya je ya ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, sai su shiga su zauna a wurin. Ƙarshen wannan mutum kuwa zai fi farkonsa muni.”
他于是又找了另外七个更邪恶的污灵,一起住进去。后来那个男人变得比以前更坏了。”
27 Da Yesu yake cikin faɗin waɗannan abubuwa, sai wata mace daga cikin taron ta ɗaga murya ta ce masa, “Mai albarka ce uwar da ta haife ka, wadda ka sha mamanta.”
耶稣正在说话之际,民众中有一个女人高喊:“孕育和哺育你的人有福了!”
28 Yesu ya amsa ya ce, “A maimakon, masu albarka ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma biyayya da ita.”
但耶稣说:“但不如听到并遵守上帝之道的人有福。”
29 Da taron mutane suka ƙaru, sai Yesu ya ce, “Wannan mugun zamani ne. Tana neman wani abin banmamaki, amma ba ko ɗaya da za a ba ta, sai dai ta Yunana.
众人围坐在耶稣身边,耶稣就说:“这是个邪恶的世界,因为他们寻求神迹,可是除了约拿的神迹以外,他们看不到其他神迹。
30 Kamar yadda Yunana ya zama alama ga mutanen Ninebe, haka ma Ɗan Mutum zai zama ga zamanin nan.
约拿如何成为尼尼微人的神迹,人子就会怎样成为这个世界的神迹。
31 A ranar shari’a, Sarauniyar Kudu za tă tashi tsaye tare da wannan zamani, ta yanke wa wannan zamani hukunci, domin ta zo daga ƙarshen duniya ta saurari hikimar Solomon, ga shi kuwa, shi wanda ya fi Solomon girma, na nan.
在审判中,南方女王将和这世界之人一起崛起,定众人的罪,因为她来自极地,想要听所罗门的智慧之语。但现在,这里有人比所罗门更伟大!
32 A ranar shari’a, mutanen Ninebe za su tashi tsaye tare da wannan zamani, su yanke wa wannan zamani hukunci. Gama sun tuba sa’ad da Yunana ya yi musu wa’azi. Ga shi yanzu, shi wanda ya fi Yunana girma, na nan.
在审判的时候,尼尼微人要和这世界之人一起崛起,定众人的罪,因为尼尼微人听了约拿说的讯息后就悔改了。但现在,这里有人比约拿更伟大。
33 “Babu wanda yakan ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta, ko ya rufe ta da murfi ba. A maimako, yakan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, don masu shiga su ga haske.
没有人在点灯后将它藏起来,或放在大碗下面。不,你应该把它放在灯台上,让进到屋内的人可以看得见光。
34 Idonka shi ne fitilar jikinka. Sa’ad da idanunka suna da lafiya, dukan jikinka ma na cike da haske, amma sa’ad da idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma na cike da duhu.
你的眼睛就是身体的灯。眼睛健康,身体就充满光,眼睛不健康,身体就进入黑暗。
35 Ka lura fa, kada hasken da yake cikinka ya zamana duhu ne.
所以如果你身体中其实是一片黑暗,不要误以为那是光让你身体的光成为一片黑暗。
36 Saboda haka, in dukan jikinka yana cike da haske, ba inda ke da duhu, jikinka kuwa zai kasance da haske gaba ɗaya, kamar yadda hasken fitila yake haskaka ka.”
要让你充满了光,不会陷入黑暗。”
37 Da Yesu ya gama magana, sai wani Bafarisiye ya gayyace shi cin abinci tare da shi. Sai kuwa ya shiga ya zauna a tebur.
耶稣说完这番话,一个法利赛人请耶稣和他一起吃饭。于是他于是就坐下吃饭。
38 Amma Bafarisiyen ya lura cewa, Yesu bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba, sai mamaki ya kama shi.
这个法利赛人很惊讶地发现,耶稣吃饭前不洗手。
39 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ku Farisiyawa, kukan wanke bayan kwano da kwaf, amma a ciki kuna cike da kwaɗayi da mugunta.
主对他说:“你们法利赛人把杯盘的外面洗净,但里面却充满了贪念和邪恶。
40 Ku wawayen mutane! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ne kuma ya yi cikin ba?
愚蠢的人啊,你们认为那创造外在的人,也会创造内在吗?
41 Ku ba matalauta abin da yake cikin kwano, kuma kome zai zama muku da tsabta.
当你对他人做出善举,只有发自内心,才能将你们的一切变得洁净。
42 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kuna ba wa Allah zakka na na’ana’arku, da ƙarƙashinku, da kuma sauran ganyen lambunku iri-iri, amma kun ƙyale adalci da ƙaunar Allah. Ya kamata da kun kiyaye na ƙarshen, ban ba barin na farkon.
你们法利赛人有祸了!因为你们献上了十分之一的药草和植物,却忽视了公义和对上帝的爱。你们需要关注后者,但前者也不能疏忽。
43 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kun cika son wuraren zama masu daraja a majami’u, da kuma yawan gaisuwa a wuraren kasuwanci.
你们法利赛人有祸了!你们喜欢在犹太教堂里占据最好的座位,希望在市场中获得尊重。
44 “Kaitonku, domin ku kamar kaburbura ne da ba a sa musu alama ba, waɗanda mutane suke takawa don rashin sani.”
你们有祸了!因为你们就像没有刻字的坟墓,人们走在上面也不知情。”
45 Sai ɗaya daga cikin masanan dokoki ya ce wa Yesu, “Malam, in ka faɗi waɗannan abubuwa haka, kai kuma ka zage mu ke nan.”
研究法律的专家中有一个回答他:“老师,你这样说,也是在侮辱我们!”
46 Yesu ya amsa ya ce, “Ku masanan dokoki ma, kaitonku, domin kun ɗora wa mutane kaya masu nauyi waɗanda da ƙyar suke ɗaukawa, amma ku da kanku ba za ku sa ko yatsa ɗaya, don ku taimake su ba.
耶稣回答:“你们研究法律的专家也有祸了!因为你们让其他人背上难以承受的重负,自己却连一个指头也不动。
47 “Kaitonku, domin kun gina kaburbura saboda annabawa, nan kuwa kakannin-kakanninku ne suka kashe su.
你们有祸了!你们建造纪念陵墓来纪念先知,但杀死他们的正是你们自己的父辈!
48 Wannan ya shaida cewa kun amince da abin da kakannin-kakanninku suka yi. Sun karkashe annabawa, ku kuma kun gina kaburburansu.
你们这样做就等于成为证人,表明你们同意祖先的行为。他们杀害先知,然后又修造先知的坟墓。
49 Saboda haka, Allah a cikin hikimarsa ya ce, ‘Zan aika musu da annabawa da manzanni. Za su kashe waɗansu, su kuma tsananta wa waɗansu.’
所以上帝很睿智地说:‘我要把先知和门徒派到他们中间,有的被他们杀害,有的被他们迫害。’
50 Saboda haka, alhakin jinin dukan annabawa da aka kashe, tun farkon duniya, yana kan wannan zamani,
最终,创世以来众先知所流的血,
51 wato, tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya, wanda aka kashe tsakanin bagade da mazauni. I, ina gaya muku, alhakinsu duka yana kan wannan zamani.
从亚伯开始,直到在祭坛和神庙之间被害的撒迦利亚,都要向这世界追讨。是的,我告诉你们,这一切都要向这世界追讨。
52 “Kaitonku, masanan dokoki, domin kun ɗauke mabuɗin ilimi. Ku kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana wa waɗanda suke shiga, su shiga.”
你们研究法律的专家有祸了!因为你们拿走了知识的钥匙,自己不进去,却又阻止其他人进去。”
53 Da Yesu ya bar wurin, sai Farisiyawa da malaman dokoki suka fara gaba mai tsanani da shi, kuma suna tsokanansa da tambayoyi.
耶稣离开的时候,宗教老师和法利赛人开始用言语激烈地攻击他,提出很多问题激怒他。
54 Suna fakonsa, don su kama shi a kan wata magana da zai faɗa.
他们希望抓住他的漏洞,想从他的言语中找到可以攻击的地方。

< Luka 11 >