< Luka 10 >
1 Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
After this the Lord appointed seventy others, and sent them before Him, by twos, to go to every town or place which He Himself intended to visit.
2 Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
And He addressed them thus: "The harvest is abundant, but the reapers are few: therefore entreat the Owner of the harvest to send out more reapers into His fields. And now go.
3 Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
Remember that I am sending you out as lambs into the midst of wolves.
4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
Carry no purse, bag, nor change of shoes; and salute no one on your way."
5 “Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
"Whatever house you enter, first say, 'Peace be to this house!'
6 In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
And if there is a lover of peace there, your peace shall rest upon it; otherwise come back upon you.
7 Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
And in that same house stay, eating and drinking at their table; for the labourer deserves his wages. Do not move from one house to another.
8 “Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
"And whatever town you come to and they receive you, eat what they put before you.
9 Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
Cure the sick in that town, and tell them, "'The Kingdom of God is now at your door.'
10 Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
"But whatever town you come to and they will not receive you, go out into the broader streets and say,
11 ‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
"'The very dust of your town that hangs about us we wipe off as a protest. Only be sure of this, that the Kingdom of God is close at hand.'
12 Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
"I tell you that it will be more endurable for Sodom on the great day than for that town.
13 “‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
"Alas for thee, Chorazin! Alas for thee, Bethsaida! For had the miracles been performed in Tyre and Sidon which have been performed in you, long ere now they would have repented, sitting in sackcloth and ashes.
14 A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
However, for Tyre and Sidon it will be more endurable at the Judgement than for you.
15 Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
And thou, Capernaum, shalt thou be lifted high as Heaven? Thou shalt be driven down as low as Hades. (Hadēs )
16 “Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
"He who listens to you listens to me; and he who disregards you disregards me, and he who disregards me disregards Him who sent me."
17 Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
When the Seventy returned, they exclaimed joyfully, "Master, even the demons submit to us when we utter your name."
18 Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
"I saw Satan fall like a lightning-flash out of Heaven," He replied.
19 Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
"I have given you power to tread serpents and scorpions underfoot, and to trample on all the power of the Enemy; and in no case shall anything do you harm.
20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
Nevertheless rejoice not at this, that the spirits submit to you; but rejoice that your names are registered in Heaven."
21 A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
On that same occasion Jesus was filled by the Holy Spirit with rapturous joy. "I give Thee fervent thanks," He exclaimed, "O Father, Lord of Heaven and earth, that Thou hast hidden these things from sages and men of understanding, and hast revealed them to babes. Yes, Father, for such has been Thy gracious will.
22 “Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
All things are delivered to me by my Father; and no one knows who the Son is but the Father, nor who the Father is but the Son, and he to whom the Son may choose to reveal Him."
23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
And He turned towards His disciples and said to them apart, "Blessed are the eyes which see what you see!
24 Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
For I tell you that many Prophets and kings have desired to see the things you see, and have not seen them, and to hear the things you hear, and have not heard them."
25 Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
Then an expounder of the Law stood up to test Him with a question. "Rabbi," he asked, "what shall I do to inherit the Life of the Ages?" (aiōnios )
26 Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
"Go to the Law," said Jesus; "what is written there? how does it read?"
27 Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
"'Thou shalt love the Lord thy God,'" he replied, "'with thy whole heart, thy whole soul, thy whole strength, and thy whole mind; and thy fellow man as much as thyself.'"
28 Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
"A right answer," said Jesus; "do that, and you shall live."
29 Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
But he, desiring to justify himself, said, "But what is meant by my 'fellow man'?"
30 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
Jesus replied, "A man was once on his way down from Jerusalem to Jericho when he fell among robbers, who after both stripping and beating him went away, leaving him half dead.
31 Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
Now a priest happened to be going down that way, and on seeing him passed by on the other side.
32 Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
In like manner a Levite also came to the place, and seeing him passed by on the other side.
33 Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
But a certain Samaritan, being on a journey, came where he lay, and seeing him was moved with pity.
34 Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
He went to him, and dressed his wounds with oil and wine and bound them up. Then placing him on his own mule he brought him to an inn, where he bestowed every care on him.
35 Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
The next day he took out two shillings and gave them to the innkeeper. "'Take care of him,' he said, 'and whatever further expense you are put to, I will repay it you at my next visit.'
36 “A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
"Which of those three seems to you to have acted like a fellow man to him who fell among the robbers?"
37 Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
"The one who showed him pity," he replied. "Go," said Jesus, "and act in the same way."
38 Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
As they pursued their journey He came to a certain village, where a woman named Martha welcomed Him to her house.
39 Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
She had a sister called Mary, who seated herself at the Lord's feet and listened to His teaching.
40 Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
Martha meanwhile was busy and distracted in waiting at table, and she came and said, "Master, do you not care that my sister is leaving me to do all the waiting? Tell her to assist me."
41 Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
"Martha, Martha," replied Jesus, "you are anxious and worried about a multitude of things;
42 Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”
and yet only one thing is really necessary. Mary has chosen the good portion and she shall not be deprived of it."