< Luka 10 >
1 Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
After this, the Master appointed seventy-two other disciples, and sent them on as his messengers, two and two, in advance, to every town and place that he was himself intending to visit.
2 Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
‘The harvest,’ he said, ‘is abundant, but the labourers are few. Therefore pray to the owner of the harvest to send labourers to gather in his harvest.
3 Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
Now, go. Remember, I am sending you out as my messengers like lambs among wolves.
4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
Do not take a purse with you, or a bag, or sandals; and do not stop to greet anyone on your journey.
5 “Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
Whatever house you go to stay at, begin by praying for a blessing on it.
6 In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
Then, if anyone there is deserving of a blessing, your blessing will rest on him; but if not, it will come back on yourselves.
7 Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
Remain at that same house, and eat and drink whatever they offer you; for the worker is worth their wages. Do not keep changing from one house to another.
8 “Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
Whatever town you visit, if the people welcome you, eat what is set before you;
9 Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
cure the sick there, and tell people that the kingdom of God is close at hand.
10 Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
But, whatever town you go to visit, if the people do not welcome you, go out into its streets and say
11 ‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
“We wipe off the dust of your town which has clung to Our feet; still, be assured that the kingdom of God is close at Hand.”
12 Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
I tell you that the doom of Sodom will be more bearable on that day than the doom of that town.
13 “‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
Alas for you, Chorazin! Alas for you, Bethsaida! For, if the miracles which have been done in you had been done in Tyre and Sidon, they would have sat in sackcloth and ashes and repented long ago.
14 A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
Yet the doom of Tyre and Sidon will be more bearable at the judgment than yours.
15 Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
And you, Capernaum! Will you exalt yourself to heaven? You will be flung down to Hades. (Hadēs )
16 “Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
Anyone who listens to you is listening to me, and anyone who rejects you is rejecting me; while the person who rejects me is rejecting him who sent me as his messenger.’
17 Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
When the seventy-two returned, they exclaimed joyfully, ‘Master, even the demons submit to us when we use your name.’
18 Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
And Jesus replied, ‘I have had visions of Satan, fallen, like lightning from the heavens.
19 Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
Remember, I have given you the power to trample on snakes and scorpions, and to meet all the strength of the Enemy. Nothing will ever harm you in any way.
20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
Yet do not rejoice in the fact that the spirits submit to you, but rejoice that your names have been enrolled in heaven.’
21 A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
At that same time, moved to exultation by the Holy Spirit, Jesus said: ‘I thank you, Father, Lord of heaven and earth, that, though you have hidden these things from the wise and learned, you have revealed them to the childlike! Yes, Father, I thank you that this has seemed good to you.
22 “Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
Everything has been committed to me by my Father; nor does anyone know who the Son is, except the Father, or who the Father is, except the Son and those to whom the Son may choose to reveal him.’
23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
Then, turning to his disciples, Jesus said to them alone, ‘Blessed are the eyes that see what you are seeing;
24 Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
for, I tell you, many prophets and kings wished for the sight of the things which you are seeing, yet never heard them.’
25 Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
Just then a student of the Law came forward to test Jesus further. ‘Teacher,’ he said, ‘what must I do if I am to gain eternal life?’ (aiōnios )
26 Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
‘What is said in the Law?’ answered Jesus. ‘What do you read there?’
27 Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
His reply was – ‘You must love the Lord your God with all your heart, and with all your soul, and with all your strength, and with all your mind; and your neighbour as you love yourself.’
28 Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
‘You have answered right,’ said Jesus, ‘Do that, and you will live.’
29 Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
But the man, wanting to justify himself, said to Jesus, ‘And who is my neighbour?’
30 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
To which Jesus replied, ‘A man was once going down from Jerusalem to Jericho when he fell into the hands of robbers, who stripped him of everything, and beat him, and went away leaving him half dead.
31 Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
As it chanced, a priest was going down by that road. He saw the man, but passed by on the opposite side.
32 Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
A Levite, too, did the same; he came up to the spot, but, when he saw the man, passed by on the opposite side.
33 Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
But a Samaritan, traveling that way, came upon the man, and, when he saw him, he was moved with compassion.
34 Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
He went to him and bound up his wounds, dressing them with oil and wine, and then put him on his own mule, and brought him to an inn, and took care of him.
35 Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
The next day he took out two silver coins and gave them to the innkeeper. “Take care of him,” he said, “and whatever more you may spend I will myself repay you on my way back.”
36 “A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
Now which, do you think, of these three men,’ asked Jesus, ‘proved himself a neighbour to the man who fell into the robbers’ hands?’
37 Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
‘The one that took pity on him,’ was the answer; at which Jesus said, ‘Go and do the same yourself.’
38 Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
As they continued their journey, Jesus came to a village, where a woman named Martha welcomed him to her house.
39 Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
She had a sister called Mary, who seated herself at the Master’s feet, and listened to his teaching;
40 Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
but Martha was distracted by the many preparations that she was making. So she went up to Jesus and said, ‘Master, do you approve of my sister’s leaving me to make preparations alone? Tell her to help me.’
41 Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
‘Martha, Martha,’ replied the Master, ‘you are anxious and trouble yourself about many things;
42 Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”
but only a few are necessary, or rather one. Mary has chosen the good part, and it will not be taken away from her.’