< Luka 10 >

1 Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
Now after these things, the Lord appointed seventy others also, and sent them two by two ahead of Him to every town and place where He Himself was about to go.
2 Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
Then He said to them: “The harvest is indeed great, but the workers are few; therefore pray to the Lord of the harvest that He may send out workers into His harvest.
3 Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
“Go! Yes, I am sending you out like lambs among wolves.
4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
Do not carry a purse, nor a knapsack, nor sandals; and greet no one along the road.
5 “Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
Into whatever house you enter, first say, ‘Peace to this house.’
6 In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
If a son of peace is there, your peace will rest upon him; but if not, it will return to you.
7 Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
Remain in that same house, eating and drinking what they offer, because the worker is worthy of his wages. Do not move around from house to house.
8 “Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
“And into whatever town you enter, and they receive you, eat the things that are set before you.
9 Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
Heal the sick therein and say to them, ‘The Kingdom of God has come near to you.’
10 Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
But into whatever town you enter, and they do not receive you, go out into its streets and say:
11 ‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
‘Even the dust of your town that clings to us we wipe off against you. Nonetheless know this, that the Kingdom of God has come near to you.’
12 Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
I say to you that it will be more tolerable in that Day for Sodom than for that town.
13 “‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
“Woe to you, Chorazin! Woe to you, Bethsaida! Because if the mighty works that were done in you had been done in Tyre and Sidon, they would have repented long ago, sitting in sackcloth and ashes.
14 A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
Nevertheless it will be more tolerable for Tyre and Sidon at the Judgment than for you.
15 Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs g86)
And you, Capernaum, who are ‘exalted to heaven’, will be brought down to Hades. (Hadēs g86)
16 “Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
“He who listens to you listens to me, and he who rejects you rejects me; but he who rejects me rejects Him who sent me!”
17 Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
Then the seventy returned with joy, saying, “Lord, even the demons are subject to us in your name!”
18 Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
So He said to them: “I watched Satan fall like lightning out of heaven.
19 Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
Take note, I am giving you the authority to trample on snakes and scorpions, and over all the power of the enemy, and nothing at all may harm you.
20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
However, do not rejoice in this, that the spirits are subject to you; rather rejoice because your names are written in heaven.”
21 A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
In that same hour Jesus exulted in His spirit and said: “I praise you, Father, Lord of heaven and earth, that you have hidden these things from the wise and intelligent, and have revealed them to ‘infants’. Yes, Father, because it pleased you to do so.”
22 “Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
And turning to the disciples He said: “All things have been entrusted to me by my Father; also, no one knows who the Son is except the Father, and who the Father is except the Son, and to whomever the Son may choose to reveal Him.”
23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
Then turning to His disciples privately He said: “Blessed are the eyes that are seeing the things that you see;
24 Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
for I say to you that many prophets and kings have desired to see what you are seeing but did not, and to hear what you are hearing but did not.”
25 Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
And then, a certain lawyer stood up to test Him, saying, “Teacher, what must I do to inherit eternal life?” (aiōnios g166)
26 Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
So He said to him: “What is written in the Law? How do you read it?”
27 Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
In answer he said: “You shall love the Lord your God with all your heart, and with all your soul, and with all your strength, and with all your mind, and, your neighbor as yourself.”
28 Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
So He said to him, “You have answered correctly; do this and you will live!”
29 Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
But he, wanting to justify himself, said to Jesus, “And who is my neighbor?”
30 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
By way of reply Jesus said: “A certain man was going down from Jerusalem to Jericho, and as it chanced he ran into robbers, who after having stripped and wounded him, departed, leaving him half dead.
31 Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
Now by coincidence a certain priest was going down that road, and when he saw him he passed by on the other side.
32 Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
So too, a Levite, when he arrived at the place, came and looked, and passed by on the other side.
33 Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
But a certain Samaritan, as he traveled, came by there, and upon seeing him was moved with compassion;
34 Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
and going to him he bound up his wounds, applying oil and wine. Then he placed him on his own mount, brought him to an inn, and took care of him.
35 Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
On the next day, when he departed, he took out two denarii, gave them to the innkeeper, and said to him, ‘Take care of him; and should you spend more, I will repay you when I return.’
36 “A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
So which of these three, would you say, was ‘neighbor’ to him who ran into the robbers?”
37 Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
He said, “The one who showed mercy on him.” So Jesus said to him, “Go and do likewise!”
38 Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
Now it happened as they traveled that He entered a certain village; and a certain woman named Martha welcomed Him into her house.
39 Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
And she had a sister called Mary, who actually sat at Jesus' feet listening to His words.
40 Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
Well Martha was distracted with much serving; so coming up she said: “Lord, don't you care that my sister has left me to serve alone? Do please tell her to help me!”
41 Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
But in answer Jesus said to her: “Martha, Martha, you are anxious and agitated about many things,
42 Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”
but only one is needed. However, Mary has chosen the good part, which will not be taken away from her.”

< Luka 10 >