< Luka 10 >
1 Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
And after these things, the Lord appointed seventy others, also, and sent them, two and two, before his face, into every city and place to which he himself was about to go.
2 Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
He said, therefore, to them: The harvest truly is great, but the laborers are few; pray, therefore, the Lord of the harvest that he send out laborers into his harvest.
3 Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
Go; behold, I send you as lambs in the midst of wolves.
4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
Carry no purse, nor bag, nor sandals; and salute no one on the road.
5 “Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
Whatever house you enter, first say, Peace be to this house.
6 In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
And if a son of peace be there, your peace shall rest on him; but, if not, it shall return upon you.
7 Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
And in that house remain, eating and drinking what they have to give; for the laborer is worthy of his hire; go not from house to house.
8 “Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
And whatever city you enter, and they receive you, eat what is set before you;
9 Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
and heal those in it who are sick, and say to them: The kingdom of God has come near to you.
10 Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
But whatever city you enter, and they receive you not, go out into the streets of it, and say:
11 ‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
Even the dust of your city, which cleaves to us, we do wipe off against you; yet know this, that the kingdom of God has come near to you.
12 Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
I say to you, It shall be more tolerable, in that day, for Sodom, than for that city.
13 “‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
Alas for thee, Chorazin! alas for thee, Bethsaida! for, if the mighty works which have been done in you, had been done in Tyre and Sidon, they would have repented long ago, sitting in sackcloth and ashes.
14 A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
But for Tyre and Sidon it shall be more tolerable in the judgment, than for you.
15 Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs )
And thou, Capernaum, who hast been exalted to heaven, shalt be brought down to hades. (Hadēs )
16 “Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
He that hears you, hears me; and he that rejects you, rejects me; and he that rejects me, rejects him that sent me.
17 Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
And the seventy returned with joy, and said: Lord, even the demons are subject to us through thy name.
18 Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
And he said to them: I saw Satan, like lightning from heaven, falling.
19 Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
Behold, I give you authority to tread on serpents and scorpions, and authority over all the power of the enemy; and nothing shall by any means hurt you.
20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
However, rejoice not in this, that the spirits are subject to you; but rejoice that your names are written in heaven.
21 A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
In that hour Jesus rejoiced in spirit, and said: I thank thee, Father, Lord of heaven and earth, because thou hast hid these things from the wise and prudent, and hast revealed them to babes; even so, Father, for so it seemed good in thy sight.
22 “Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
All things are delivered to me by my Father; and no one knows who the Son is but the Father, and who the Father is but the Son, and he to whom the Son will reveal him.
23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
And he turned to his disciples, and said privately: Blessed are the eyes that see what you see.
24 Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
For I say to you, that many prophets and kings desired to see what you see, and did not see; and to hear what you hear, and did not hear.
25 Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
And, behold, a certain lawyer stood up to tempt him, and said: Teacher, what shall I do to inherit eternal life? (aiōnios )
26 Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
He said to him: What is written in the law? How do you read?
27 Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
He answered and said: You shall love the Lord your God with your whole heart, and with your whole soul, and with your whole strength, and with your whole understanding, and your neighbor as yourself.
28 Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
He said to him: You have answered correctly; do this, and you shall live.
29 Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
But, wishing to justify himself, he said to Jesus: And who is my neighbor?
30 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
And Jesus answered and said: A certain man went down from Jerusalem to Jericho, and fell among; robbers, who stripped him of his raiment, and wounded him, and went away, leaving him half dead.
31 Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
And by chance a certain priest went down along that road, and when he saw him, he passed by on the other side.
32 Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
In like manner, also, a Levite, when he came to the place, went and looked on him, and passed by on the other side.
33 Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
But a certain Samaritan, who was on a journey, came near him; and when he saw him, he had compassion on him.
34 Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
And he went to him, and bound up his wounds, pouring in oil and wine; and he put him on his own beast, and carried him to an inn, and took care of him.
35 Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
And on the morrow, when he departed, he took out two denarii, and gave them to the innkeeper, and said to him: Take care of him; and whatever you spend more, on my return, I will repay you.
36 “A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
Which, then, of these three do you think was neighbor to him that fell among the robbers?
37 Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
He replied: He that showed mercy to him. Jesus said to him: Go, and do you likewise.
38 Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
And it came to pass, as they continued their journey, that he entered a certain village, and a certain woman named Martha received him into her house.
39 Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
And she had a sister called Mary, who also sat at the feet of Jesus, and heard his word.
40 Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
But Martha made herself busy with much serving; and she came to him, and said: Lord, dost thou not care that my sister has left me to serve alone? Bid her, therefore, that she help me.
41 Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
But Jesus answered and said to her: Martha, Martha, you are anxious and troubled about many things:
42 Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”
one thing is needful; and Mary has chosen the good part, which shall not be taken from her.