< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Яко ж бо многі заходились опоряджувати повість про добре знані нам речі,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
як передали нам ті, що з почину були самовидцями й слугами слова;
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
то здалось і менї гаразд, довідавшись од почину про все пильно, поряду тобі написати, високоповажний Теофиле,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
щоб знав певноту того, чого тебе навчено.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
Був за Ірода, царя Юдейського, один сьвященик, на ймя Захарія, з черги Авиїної, а жінка його з дочок Ааронових, а ймя її Єлисавета.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Були ж праведні обоє перед Богом, ходячи у всіх заповідях та наказах Господнїх безпорочні.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
і не було в них дитини: бо Єлисавета була неплідна, й обоє постарілись у днях своїх.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Стало ся ж, як служив він порядком черги своєї перед Богом,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
то, звичаєм сьвященства, довелось йому кадити, увійшовши в церкву Господню.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
А все множество народу молилось ізнадвору під час кадження.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Явив ся ж йому ангел Господень, стоячи правобіч жертівнї кадильної.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
І вжахнув ся Захарія побачивши, і страх обняв його.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
Рече ж до него ангел: Не лякай ся, Захаріє: бо вислухана молитва твоя, і жінка твоя Єлисавета вродить сина тобі, й даси ймя йому Йоан.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
І буде радість тобі й веселість; і многі різдвом його радувати муть ся.
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
Буде бо великий перед Господем, і вина нї міцного напитку не пити ме; й Духом сьвятим сповнить ся ще з утроби матери своєї.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
І многих синів Ізраїлевих наверне до Господа Бога їх.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
І йти ме він перед Ним духом і силою Ілиї, щоб навернути серця батьків до дїтей, і неслухняних до мудрости праведних, приготовити Господеві людей готових.
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
І рече Захарія до ангела: По чім же знати му се? я бо старий, і жінка моя ізстарілась у днях своїх.
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
І озвавшись ангел, рече йому: Я Гавриїл, що стою перед Господем; і послано мене промовити до тебе та сповістити тебе про се.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
І ось замовкнеш і не зможеш говорити, аж по день, коли станеть ся се, за те що не поняв віри словам моїм, котрі справдять ся пори своєї.
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
І ждав народ Захарії, і дивував ся, що барить ся він у церкві.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
Вийшовши ж він, не зміг промовити до них; і постерегли вони, що видїннє бачив у церкві; бо він кивав до них, і зоставсь нїмий.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
І сталось, як сповнились днї служення його, пійшов до господи своєї.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
Після ж тих днїв зачала Єлисавета, жінка його, й втаїлась пять місяцїв, говорячи:
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
Що так менї дав Господь у ті днї, як зглянув ся, зняти з мене докір між людьми.
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
Місяця ж шестого післав Бог ангела Гавриїла в город Галилейський, званий Назарет,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
до дїви, зарученої чоловікові, на ймя Йосифові, з дому Давидового; а ймя дїви Мария.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
І прийшовши ангел до неї, рече: Радуй ся, благодатная. Господь з тобою; благословенна єси між женами.
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Вона ж, побачивши його, вжахнулась словами його, та й подумала, що б се було за витаннє таке.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
І рече ангел їй: Не лякай ся, Мариє: знайшла бо єси ласку в Бога.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
І ось зачнеш ти в утробі твоїй, і вродиш Сина, й наречеш імя Йому Ісус.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
Сей буде великий, і Сином Вишнього звати меть ся, і дасть Йому Господь Бог престол Давида, отця Його:
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
і царювати ме Він над домом Якововим по віки, й царству Його не буде кінця. (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
Рече ж Мария до ангела: Як буде се, коли чоловіка не знаю?
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
І озвавшись ангел, рече їй: Дух сьвятий найде на тебе, й сила Вишнього отїнить тебе; тим і, що вродить ся сьвяте, звати меть ся Сином Божим.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
І ось Єлисавета, родичка твоя і вона також зачала, сина в старості своїй, і се шестий місяць званій неплідною.
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
Бо не буде неможливе у Бога всяке слово.
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
Рече ж Мария: Се рабиня Господня: нехай станеть ся менї по слову твоєму. І пійшов від неї ангел.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
Уставши ж Мария тими днями, пійшла швидко в підгіррє, у город Юдин;
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
і ввійшла в господу Захаріїну, і виталась із Єлисаветою.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
І сталось, як почула Єлисавета витаннє Мариїне, кинулась дитина в утробі її; і сповнилась Єлисавета Духом сьвятим,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
і промовила голосом великим, і рече: Благословенна єси між женами, й благословенний плід утроби твоєї.
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
І звідкіля менї се, що прийшла мати Господа мого до мене?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
Ось бо, як дійшов голос витання твого до ушей моїх, кинулась з радости дитина в утробі моїй.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
І благословенна, що увірувала, бо сповнить ся, що сказано їй від Господа.
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
І рече Мария: Величає душа моя Господа,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
і зрадував ся дух мій у Бозї Спасї моїм,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
що споглянув на смиреннє слуги своєї: ось бо від нинї блаженною звати муть мене всї роди:
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
бо зробив менї велике Сильний; і сьвяте імя Його.
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
І милості Його від роду до роду на боячих ся Його.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
Зробив силу рукою своєю, розсипав гордих у думках сердець їх;
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
поскидав потужних з престолів, і підняв угору смиренних;
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
голодних сповнив добром, а багатих одіслав упорожнї;
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
прийняв Ізраїля, слугу свого, на спомин милости,
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
(як промовив до батьків наших) Авраамові й насінню його по віки. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Пробувала ж Мария з нею місяцїв зо три, та й вернулась до домівки своєї.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
Єлисаветї ж сповнив ся час родити, й вродила вона сина.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
І чули сусіде її і родина її, що Господь показав велику милость свою до неї, і радувались із нею.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
І сталось, восьмого дня прийшли обрізати хлопятко, і хотіли назвати його ймям батька його, Захарією.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
І озвавшись мати його, каже: Нї, а нехай назветь ся Йоаном.
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
І казали до неї: Що нікого нема в родині твоїй, щоб звав ся імям сим.
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
Кивали ж батькові його, як схотів би назвати його.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
І, попросивши таблицї, написав слова: Йоан буде ймя йому. І дивувались усї.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
Відкрили ся яе уста його зараз, і язик його, й заговорив, прославляючи Бога.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
І був на всїх страх, що жили кругом них; і по всьому підгіррю Юдейському пронеслись усї слова ті.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
І положили всі, хто чув, у серці своїм, кажучи: Що ж то за дитина се буде! І рука Господня була з ним.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
І Захарія, батько його, сповнив ся Духом сьвятим, і прорік, глаголючи:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
Благословен Господь Бог Ізраїлїв, що одвідав і зробив ізбавленнє народові своєму,
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
і підняв ріг спасення нам у дому Давида, слуги свого,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
(як промовляв устами сьвятих од віку пророків своїх, ) (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
спасеннє од ворогів наших і з руки всіх ненавидників наших,
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
щоб зробити милость отцям нашим, і спогадати завіт свій сьвятий,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
клятьбу, що кляв ся перед Авраамом, отцем нашим,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
та що дасть нам без страху, з рук ворогів наших визволившись,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
служити Йому в сьвятостї та праведності перед Ним, по всі днї життя нашого.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
А ти, дитино, пророком Вишнього звати меш ся: ходити меш бо перед лицем Господнім, готовити дороги Його;
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
щоб давати знаннє спасення народові Його в оставленню гріхів їх,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
по благій милості Бога нашого, в котрій одвідав нас Схід з висоти,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
щоб засияв сидячим у темряві і тїнї смертній, щоб направити ноги наші на дорогу впокою.
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
Хлопятко ж росло та міцніло духом, і пробувало в пустині аж до дня явлення свого перед Ізраїлем.

< Luka 1 >