< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Seeing that many have attempted to draw up a narrative of the facts which are received with full assurance among us
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
on the authority of those who were from the beginning eye-witnesses and were devoted to the service of the divine Message,
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
it has seemed right to me also, after careful investigation of the facts from their commencement, to write for you, most noble Theophilus, a connected account,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
that you may fully know the truth of the things which you have been taught by word of mouth.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
There was in the time of Herod, the king of Judaea, a priest of the name of Zechariah, belonging to the class of Abijah. He had a wife who was a descendant of Aaron, and her name was Elizabeth.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
They were both of them upright before God, blamelessly obeying all the Lord's precepts and ordinances.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
But they had no child, because Elizabeth was barren; and both of them were far advanced in life.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Now while he was doing priestly duty before God in the prescribed course of his class,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
it fell to his lot--according to the custom of the priesthood--to go into the Sanctuary of the Lord and burn the incense;
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
and the whole multitude of the people were outside praying, at the hour of incense.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Then there appeared to him an angel of the Lord standing on the right side of the altar of incense;
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
and Zechariah on seeing him was agitated and terrified.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
But the angel said to him, "Do not be afraid, Zechariah, for your petition has been heard: and your wife Elizabeth will bear you a son, and you are to call his name John.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
Gladness and exultant joy shall be yours, and many will rejoice over his birth.
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
For he will be great in the sight of the Lord; no wine or fermented drink shall he ever drink; but he will be filled with the Holy Spirit from the very hour of his birth.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
Many of the descendants of Israel will he turn to the Lord their God;
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
and he will be His forerunner in the spirit and power of Elijah, to turn fathers' hearts to the children, and cause the rebellious to walk in the wisdom of the upright, to make a people perfectly ready for the lord."
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
"By what proof," asked Zechariah, "shall I know this? For I am an old man, and my wife is far advanced in years."
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
"I am Gabriel, who stand in the presence of God," answered the angel, "and I have been sent to talk with you and tell you this good news.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
And now you will be dumb and unable to speak until the day when this has taken place; because you did not believe my words--words which will be fulfilled at their appointed time."
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Meanwhile the people were waiting for Zechariah, and were surprised that he stayed so long in the Sanctuary.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
When, however, he came out, he was unable to speak to them; and they knew that he must have seen a vision in the Sanctuary; but he kept making signs to them and continued dumb.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
When his days of service were at an end, he went to his home;
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
and in course of time his wife Elizabeth conceived, and kept herself secluded five months.
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
"Thus has the Lord dealt with me," she said, "now that He has graciously taken away my reproach among men."
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
Now in the sixth month the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee called Nazareth,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
to a maiden betrothed to a man of the name of Joseph, a descendant of David. The maiden's name was Mary.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
So Gabriel went into the house and said to her, "Joy be to you, favoured one! the Lord is with you."
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
She was greatly agitated at his words, and wondered what such a greeting meant.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
But the angel said, "Do not be frightened, Mary, for you have found favour with God.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
You will conceive in your womb and bear a son; and you are to call His name JESUS.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
He will be great and He will be called 'Son of the Most High.' And the Lord God will give Him the throne of His forefather David;
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
and He will be King over the House of Jacob for the Ages, and of His Kingdom there will be no end." (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
"How can this be," Mary replied, "seeing that I have no husband?"
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
The angel answered, "The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will overshadow you; and for this reason your holy offspring will be called 'the Son of God.'
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
And see, your relative Elizabeth--she also has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who was called barren.
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
For no promise from God will be impossible of fulfilment."
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
"I am the Lord's maidservant," Mary replied; "may it be with me in accordance with your words!" And then the angel left her.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
Not long after this, Mary rose up and went in haste into the hill country to a town in Judah.
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
Here she came to the house of Zechariah and greeted Elizabeth;
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
and as soon as Elizabeth heard Mary's greeting, the babe leapt within her. And Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
and uttered a loud cry of joy. "Blest among women are you," she said, "and the offspring of your body is blest!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
But why is this honour done me, that the mother of my Lord should come to me?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
For, the moment your greeting reached my ears, the babe within me leapt for joy.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
And blessed is she who has believed, for the word spoken to her from the Lord shall be fulfilled."
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
Then Mary said: "My soul extols the Lord,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
And my spirit triumphs in God my Saviour;
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
Because He has not turned from His maidservant in her lowly position; For from this time forward all generations will account me happy,
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
Because the mighty One has done great things for me--Holy is His name!--
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
And His compassion is, generation after generation, Upon those who fear Him.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
He has manifested His supreme strength. He has scattered those who were haughty in the thoughts of their hearts.
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
He has cast monarchs down from their thrones, And exalted men of low estate.
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
The hungry He has satisfied with choice gifts, But the rich He has sent empty-handed away.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
His servant Israel He has helped, Remembering His compassion--
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
In fulfillment of His promises to our forefathers--For Abraham and his posterity for ever." (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
So Mary stayed with Elizabeth about three months, and then returned home.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
Now when Elizabeth's full time was come, she gave birth to a son;
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
and her neighbours and relatives heard how the Lord had had great compassion on her; and they rejoiced with her.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
And on the eighth day they came to circumcise the child, and were going to call him Zechariah, after his father.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
His mother, however, said, "No, he is to be called John."
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
"There is not one of your family," they said, "who has that name."
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
They asked his father by signs what he wished him to be called.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
So he asked for a writing-tablet, and wrote, "His name is John." And they all wondered.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
Instantly his mouth and his tongue were set free, and he began to speak and bless God.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
And all who lived round about them were filled with awe, and throughout the hill country of Judaea reports of all these things were spread abroad.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
All who heard the story treasured it in their memories. "What then will this child be?" they said. For the lord's hand was indeed with him.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
And Zechariah his father was filled with the Holy Spirit, and spoke in a rapture of praise.
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
"Blessed be the Lord, the God of Israel," he said, "Because He has not forgotten His people but has effected redemption for them,
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
And has raised up a mighty Deliverer for us In the house of David His servant--
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
As He has spoken from all time by the lips of His holy Prophets-- (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
To deliver us from our foes and from the power of all who hate us.
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
He dealt pitifully with our forefathers, And remembered His holy covenant,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
The oath which He swore to Abraham our forefather,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
To grant us to be rescued from the power of our foes And so render worship to Him free from fear,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
In piety and uprightness before Him all our days.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
And you moreover, O child, shall be called Prophet of the Most High; For you shall go on in front before the Lord to prepare the way for Him,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
To give to His People a knowledge of salvation In the forgiveness of their sins,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
Through the tender compassion of our God, Through which the daybreak from on high will come to us,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
Dawning on those who now dwell in the darkness and shadow of death--To direct our feet into the path of peace."
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
And the child grew and became strong in character, and lived in the Desert till the time came for him to appear publicly to Israel.

< Luka 1 >