< Luka 1 >
1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Forasmuch as many have undertaken to compose a narrative of those things, which have been accomplished amongst us,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
as they, who were from the beginning, eye-witnesses, and afterwards ministers of the word, delivered them to us;
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
I have also determined, having exactly traced everything from the first, to write a particular account for you, most excellent Theophilus;
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
that you might know the certainty of those matters wherein you have been instructed.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
In the days of Herod, king of Judea, there was a priest named Zacharias, of the course of Abijah; and his wife, named Elizabeth, was of the daughters of Aaron.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
They were both righteous before God, blameless observers of all the Lord's commandments and ordinances.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
And they had no child, because Elizabeth was barren, and they were advanced in years.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Now when he came to officiate as priest in the order of his course,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
it fell to him by lot, according to the custom of the priesthood, to offer incense in the sanctuary.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
And while the incense was burning, the whole congregation were praying without.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Then there appeared to him an angel of the Lord, standing on the right side of the altar of incense.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
And Zacharias was discomposed at the sight, and in great terror.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
But the angel said to him, Fear not, Zacharias; for your prayer is heard, and Elizabeth your wife shall bear you a son, whom you shall name John.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
He shall be to you matter of joy and transport; and many shall rejoice because of his birth.
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
For he shall be great before the Lord; he shall not drink wine nor any fermented liquor; but he shall be filled with the Holy Spirit, even from his mother's womb.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
And many of the sons of Israel he shall bring back to the Lord their God.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
Moreover, he shall go before him in the spirit and power of Elijah, to reconcile fathers to their children, and by the wisdom of the righteous, to render the disobedient a people well disposed for the Lord.
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
And Zacharias said to the angel, How shall I know this: for I am old man, and my wife is advanced in years?
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
The angel answering, said to him, I am Gabriel, who attend in the presence of God, and am sent to tell you this joyful news.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
But know that you shall be dumb, and shall not recover your speech, till the day when these things happen, because you have not believed my words, which shall be fulfilled in due time.
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Meanwhile the people waited for Zacharias, and wondered that he staid so long in the sanctuary.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
But when he came out, he could not speak to them; and they perceived that he had seen a vision in the sanctuary; for he made them understand by signs, and remained speechless.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
And when his days of officiating were expired, he returned home.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
Soon after, Elizabeth his wife conceived, and lived in retirement five months, and said,
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
The Lord has done this for me, purposing now to deliver me from the reproach I lay under among men.
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
Now, in the sixth month, God sent Gabriel his angel, to Nazareth, a city of Galilee;
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
to a virgin betrothed to a man called Joseph, of the house of David, and the virgin's name was Mary.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
When the angel entered, he said to her, Hail, favorite of heaven! the Lord be with you, happiest of women!
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
At his appearance and words, she was perplexed, and revolved in her mind what this salutation could mean.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
And the angel said to her, Fear not, Mary, for you have found favor with God.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
And behold, you shall conceive and bear a son, whom you shall name Jesus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
He shall be great, and shall be called the Son of the Highest. And the Lord God will give him the throne of David his Father.
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn )
And he shall reign over the house of Jacob forever: his reign shall never end. (aiōn )
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
Then said Mary to the angel, How shall this be, since I have no intercourse with man?
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
The angel answering, said to her, The Holy Spirit will descend upon you, and the power of the Highest will overshadow you; therefore the holy progeny shall be called the Son of God.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
And lo! your cousin Elizabeth also has conceived, a son in her old age; and she who is called barren, is now in her sixth month;
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
for nothing is impossible with God.
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
And Mary said, Behold the handmaid of the Lord. Be it to me according to your word. Then the angel departed.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
In those days Mary set out, and traveled expeditiously into the hill country; to a city of Judah;
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
where having entered the house of Zacharias, she saluted Elizabeth.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
As soon as Elizabeth heard Mary's salutation, the babe leaped in her womb; and Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
and cried with a loud voice, You are the most blessed of women, and blessed is the fruit of your womb.
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
But how have I deserved this honor, to be visited by the mother of my Lord!
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
for know, that as soon as the sound of your salutation reached my ears, the babe leaped in my womb for joy.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
And happy is she who believed that the things which the Lord has promised her, shall be performed.
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
Then Mary said, My soul magnifies the Lord,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
and my spirit rejoices in God my Saviour;
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
because he has not disdained the low condition of his handmaid; for henceforth, all posterity will pronounce me happy.
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
For the Almighty, whose name is venerable, has done wonders for me.
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
His mercy on them who fear him, extends to generations of generations.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
He displays the strength of his arm, and dispels the vain imaginations of the proud.
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
He pulls down potentates from their thrones, and exalts the lowly.
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
The needy he loads with benefits; but the rich he spoils of everything.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
He supports Israel his servant, ever inclined to mercy,
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn )
(as he promised to our fathers) toward Abraham and his race. (aiōn )
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
And Mary, after staying with Elizabeth about three months, returned home.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
When the time for Elizabeth's delivery was come, she brought forth a son;
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
and her neighbors and relations who heard that the Lord had shown her great kindness, rejoiced with her.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
And, on the eighth day, when they came to the circumcision of the child, they would have called him by his father's name, Zacharias.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
And his mother interposed, saying, No; but he shall be called John.
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
They said to her, There is none of your kindred of that name.
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
They, therefore, asked his father by signs, how he would have him called.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
He, having demanded a table-book, wrote upon it, His name is John, which surprised them all.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
And his mouth was opened directly, and his tongue loosed. And he spoke, praising God.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
Now all in the neighborhood were struck with awe; and the fame of these things spread throughout all the hill country of Judea.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
And all who heard these things, pondering them in their hearts, said, What will this child hereafter be? And the hand of the Lord was with him.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
Then Zacharias, his father, being filled with the Holy Spirit, prophesied, saying,
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
Blessed be the Lord, the God of Israel, because he has visited and redeemed his people;
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
and has raised a Prince for our deliverance in the house of David his servant;
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn )
(as anciently he promised by his holy prophets) (aiōn )
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
for our deliverance from our enemies, and from the hands of all who hate us;
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
in kindness to our forefathers, and remembrance of his holy institution;
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
the oath which he swore to our father Abraham,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
to grant to us, that being rescued out of the hands of our enemies, we might serve him boldly,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
in piety and uprightness all our days.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
And you, child, shall be called a prophet of the Most High; for you shall go before the Lord, to prepare his way,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
by giving the knowledge of salvation to his people, in the remission of their sins,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
through the tender compassion of our God, who has caused a light to spring from on high to visit us,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
to enlighten those who abide in darkness and in the shades of death; to direct our feet into the way of peace.
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
Meantime the child grew, and acquired strength of mind, and continued in the deserts, until the time when he made himself known to Israel.