< Luka 1 >
1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Many have undertaken to compose an account of the things that have been fulfilled among us,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
just as they were handed down to us by the initial eyewitnesses and servants of the word.
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
Therefore, having carefully investigated everything from the beginning, it seemed good also to me to write an orderly account for you, most excellent Theophilus,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
so that you may know the certainty of the things you have been taught.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
In the time of Herod king of Judea there was a priest named Zechariah, who belonged to the priestly division of Abijah, and whose wife Elizabeth was a daughter of Aaron.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Both of them were righteous in the sight of God, walking blamelessly in all the commandments and decrees of the Lord.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
But they had no children, because Elizabeth was barren, and they were both well along in years.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
One day while Zechariah’s division was on duty and he was serving as priest before God,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
he was chosen by lot, according to the custom of the priesthood, to enter the temple of the Lord and burn incense.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
And at the hour of the incense offering, the whole congregation was praying outside.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Just then an angel of the Lord appeared to Zechariah, standing at the right side of the altar of incense.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
When Zechariah saw him, he was startled and gripped with fear.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah, because your prayer has been heard. Your wife Elizabeth will bear you a son, and you are to give him the name John.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
He will be a joy and delight to you, and many will rejoice at his birth,
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
for he will be great in the sight of the Lord. He shall never take wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit even from his mother’s womb.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
Many of the sons of Israel he will turn back to the Lord their God.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
And he will go on before the Lord in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of the fathers to their children and the disobedient to the wisdom of the righteous—to make ready a people prepared for the Lord.”
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
“How can I be sure of this?” Zechariah asked the angel. “I am an old man, and my wife is well along in years.”
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
“I am Gabriel,” replied the angel. “I stand in the presence of God, and I have been sent to speak to you and to bring you this good news.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
And now you will be silent and unable to speak until the day this comes to pass, because you did not believe my words, which will be fulfilled at their proper time.”
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Meanwhile, the people were waiting for Zechariah and wondering why he took so long in the temple.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
When he came out and was unable to speak to them, they realized he had seen a vision in the temple. He kept making signs to them but remained speechless.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
And when the days of his service were complete, he returned home.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
After these days, his wife Elizabeth became pregnant and for five months remained in seclusion. She declared,
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
“The Lord has done this for me. In these days He has shown me favor and taken away my disgrace among the people.”
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
In the sixth month, God sent the angel Gabriel to a town in Galilee called Nazareth,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
to a virgin pledged in marriage to a man named Joseph, who was of the house of David. And the virgin’s name was Mary.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
The angel appeared to her and said, “Greetings, you who are highly favored! The Lord is with you.”
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Mary was greatly troubled at his words and wondered what kind of greeting this might be.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
So the angel told her, “Do not be afraid, Mary, for you have found favor with God.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
Behold, you will conceive and give birth to a son, and you are to give Him the name Jesus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
He will be great and will be called the Son of the Most High. The Lord God will give Him the throne of His father David,
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn )
and He will reign over the house of Jacob forever. His kingdom will never end!” (aiōn )
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
“How can this be,” Mary asked the angel, “since I am a virgin?”
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
The angel replied, “The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will overshadow you. So the Holy One to be born will be called the Son of God.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
Look, even Elizabeth your relative has conceived a son in her old age, and she who was called barren is in her sixth month.
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
For no word from God will ever fail.”
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
“I am the Lord’s servant,” Mary answered. “May it happen to me according to your word.” Then the angel left her.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
In those days Mary got ready and hurried to a town in the hill country of Judah,
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
where she entered the home of Zechariah and greeted Elizabeth.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
When Elizabeth heard Mary’s greeting, the baby leaped in her womb, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
In a loud voice she exclaimed, “Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
And why am I so honored, that the mother of my Lord should come to me?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
For as soon as the sound of your greeting reached my ears, the baby in my womb leaped for joy.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
Blessed is she who has believed that the Lord’s word to her will be fulfilled.”
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
Then Mary said: “My soul magnifies the Lord,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
and my spirit rejoices in God my Savior!
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
For He has looked with favor on the humble state of His servant. From now on all generations will call me blessed.
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
For the Mighty One has done great things for me. Holy is His name.
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
His mercy extends to those who fear Him, from generation to generation.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
He has performed mighty deeds with His arm; He has scattered those who are proud in the thoughts of their hearts.
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
He has brought down rulers from their thrones, but has exalted the humble.
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
He has filled the hungry with good things, but has sent the rich away empty.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
He has helped His servant Israel, remembering to be merciful,
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn )
as He promised to our fathers, to Abraham and his descendants forever.” (aiōn )
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Mary stayed with Elizabeth for about three months and then returned home.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
When the time came for Elizabeth to have her child, she gave birth to a son.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
Her neighbors and relatives heard that the Lord had shown her great mercy, and they rejoiced with her.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
On the eighth day, when they came to circumcise the child, they were going to name him after his father Zechariah.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
But his mother replied, “No! He shall be called John.”
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
They said to her, “There is no one among your relatives who bears this name.”
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
So they made signs to his father to find out what he wanted to name the child.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
Zechariah asked for a tablet and wrote, “His name is John.” And they were all amazed.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
Immediately Zechariah’s mouth was opened and his tongue was released, and he began to speak, praising God.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
All their neighbors were filled with awe, and people throughout the hill country of Judea were talking about these events.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
And all who heard this wondered in their hearts and asked, “What then will this child become?” For the Lord’s hand was with him.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
Then his father Zechariah was filled with the Holy Spirit and prophesied:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
“Blessed be the Lord, the God of Israel, because He has visited and redeemed His people.
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
He has raised up a horn of salvation for us in the house of His servant David,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn )
as He spoke through His holy prophets, those of ages past, (aiōn )
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
salvation from our enemies and from the hand of all who hate us,
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
to show mercy to our fathers and to remember His holy covenant,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
the oath He swore to our father Abraham, to grant us
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
deliverance from hostile hands, that we may serve Him without fear,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
in holiness and righteousness before Him all the days of our lives.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
And you, child, will be called a prophet of the Most High; for you will go on before the Lord to prepare the way for Him,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
to give to His people the knowledge of salvation through the forgiveness of their sins,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
because of the tender mercy of our God, by which the Dawn will visit us from on high,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
to shine on those who live in darkness and in the shadow of death, to guide our feet into the path of peace.”
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
And the child grew and became strong in spirit; and he lived in the wilderness until the time of his public appearance to Israel.