< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Kad već mnogi poduzeše sastaviti izvješće o događajima koji se ispuniše među nama -
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
kako nam to predadoše oni koji od početka bijahu očevici i sluge Riječi -
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
pošto sam sve, od početka, pomno ispitao, naumih i ja tebi, vrli Teofile, sve po redu napisati
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
da se tako osvjedočiš o pouzdanosti svega u čemu si poučen.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
U dane Heroda, kralja judejskoga, bijaše neki svećenik imenom Zaharija iz razreda Abijina. Žena mu bijaše od kćeri Aronovih, a ime joj Elizabeta.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Oboje bijahu pravedni pred Bogom: živjeli su besprijekorno po svim zapovijedima i odredbama Gospodnjim.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
No nisu imali djeteta jer Elizabeta bijaše nerotkinja, a oboje već poodmakle dobi.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Dok je Zaharija jednom po redu svoga razreda obavljao svećeničku službu pred Bogom,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
ždrijebom ga zapade po bogoslužnom običaju da uđe u Svetište Gospodnje i prinese kad.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
Za vrijeme kađenice sve je ono mnoštvo naroda vani molilo.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
A njemu se ukaza anđeo Gospodnji. Stajao je s desne strane kadionoga žrtvenika.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
Ugledavši ga, Zaharija se prepade i strah ga spopade.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
No anđeo mu reče: “Ne boj se, Zaharija! Uslišana ti je molitva: žena će ti Elizabeta roditi sina. Nadjenut ćeš mu ime Ivan.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
Bit će ti radost i veselje i rođenje će njegovo mnoge obradovati.
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
Bit će doista velik pred Gospodinom. Ni vina ni drugoga opojnog pića neće piti. Duha Svetoga bit će pun već od majčine utrobe.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
Mnoge će sinove Izraelove obratiti Gospodinu, Bogu njihovu.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
Ići će pred njim u duhu i sili Ilijinoj da obrati srce otaca k sinovima i nepokorne k razumnosti pravednih te spremi Gospodinu narod pripravan.”
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
Nato Zaharija reče anđelu: “Po čemu ću ja to razaznati. Ta star sam i žena mi poodmakle dobi.”
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
Anđeo mu odgovori: “Ja sam Gabriel koji stojim pred Bogom. Poslan sam da govorim s tobom i da ti donesem ovu radosnu poruku.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
I evo, budući da nisi povjerovao mojim riječima, koje će se ispuniti u svoje vrijeme, zanijemjet ćeš i nećeš moći govoriti do dana dok se to ne zbude.”
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Narod je iščekivao Zahariju i čudio se što se toliko zadržao u Svetištu.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
Kad je napokon izašao, nije im mogao ništa reći pa zaključiše da je u Svetištu imao viđenje. Nastojao im se doduše izraziti znakovima, ali osta nijem.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
Kad se navršiše dani njegove službe, otiđe kući.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
Nakon tih dana zatrudnje Elizabeta, njegova žena. Krila se pet mjeseci govoreći:
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
“Evo, to mi je učinio Gospodin u dane kad mu se svidje skinuti s mene sramotu među ljudima.”
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
U šestome mjesecu posla Bog anđela Gabriela u galilejski grad imenom Nazaret
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
k djevici zaručenoj s mužem koji se zvao Josip iz doma Davidova; a djevica se zvala Marija.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
Anđeo uđe k njoj i reče: “Zdravo, milosti puna! Gospodin s tobom!”
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Na tu se riječ ona smete i stade razmišljati kakav bi to bio pozdrav.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
No anđeo joj reče: “Ne boj se, Marijo! Ta našla si milost u Boga.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
Evo, začet ćeš i roditi sina i nadjenut ćeš mu ime Isus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
On će biti velik i zvat će se Sin Svevišnjega. Njemu će Gospodin Bog dati prijestolje Davida, oca njegova,
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
i kraljevat će nad domom Jakovljevim uvijeke i njegovu kraljevstvu neće biti kraja.” (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
Nato će Marija anđelu: “Kako će to biti kad ja muža ne poznajem?”
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
Anđeo joj odgovori: “Duh Sveti sići će na te i sila će te Svevišnjega osjeniti. Zato će to čedo i biti sveto, Sin Božji.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
A evo tvoje rođakinje Elizabete: i ona u starosti svojoj zače sina. I njoj, nerotkinjom prozvanoj, ovo je već šesti mjesec.
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
Ta Bogu ništa nije nemoguće!”
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
Nato Marija reče: “Evo službenice Gospodnje, neka mi bude po tvojoj riječi!” I anđeo otiđe od nje.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
Tih dana usta Marija i pohiti u Gorje, u grad Judin.
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
Uđe u Zaharijinu kuću i pozdravi Elizabetu.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
Čim Elizabeta začu Marijin pozdrav, zaigra joj čedo u utrobi. I napuni se Elizabeta Duha Svetoga
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
i povika iz svega glasa: “Blagoslovljena ti među ženama i blagoslovljen plod utrobe tvoje!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
Ta otkuda meni da mi dođe majka Gospodina mojega?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
Gledaj samo! Tek što mi do ušiju doprije glas pozdrava tvojega, zaigra mi od radosti čedo u utrobi.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
Blažena ti što povjerova da će se ispuniti što ti je rečeno od Gospodina!”
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
Tada Marija reče: “Veliča duša moja Gospodina,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
klikće duh moj u Bogu, mome Spasitelju,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
što pogleda na neznatnost službenice svoje: odsad će me, evo, svi naraštaji zvati blaženom.
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
Jer velika mi djela učini Svesilni, sveto je ime njegovo!
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
Od koljena do koljena dobrota je njegova nad onima što se njega boje.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
Iskaza snagu mišice svoje, rasprši oholice umišljene.
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
Silne zbaci s prijestolja, a uzvisi neznatne.
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
Gladne napuni dobrima, a bogate otpusti prazne.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
Prihvati Izraela, slugu svoga, kako obeća ocima našim:
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
spomenuti se dobrote svoje prema Abrahamu i potomstvu njegovu dovijeka.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Marija osta s Elizabetom oko tri mjeseca, a onda se vrati kući.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
Elizabeti se međutim navršilo vrijeme da rodi. I porodi sina.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
Kad su njezini susjedi i rođaci čuli da joj Gospodin obilno iskaza dobrotu, radovahu se s njome.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
Osmoga se dana okupe da obrežu dječaka. Htjedoše ga prozvati imenom njegova oca - Zaharija,
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
no mati se njegova usprotivi: “Nipošto, nego zvat će se Ivan!”
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
Rekoše joj na to: “Ta nikoga nema od tvoje rodbine koji bi se tako zvao.”
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
Tada znakovima upitaju oca kojim ga imenom želi prozvati.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
On zaiska pločicu i napisa “Ivan mu je ime!” Svi se začude,
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
a njemu se umah otvoriše usta i jezik te progovori blagoslivljajući Boga.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
Strah obuze sve njihove susjede, a po svem su se Gorju judejskom razglašavali svi ti događaji.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
I koji su god čuli, razmišljahu o tome pitajući se: “Što li će biti od ovoga djeteta?” Uistinu, ruka Gospodnja bijaše s njime.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
A Zaharija, otac njegov, napuni se Duha Svetoga i stade prorokovati:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
“Blagoslovljen Gospodin Bog Izraelov, što pohodi i otkupi narod svoj!
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
Podiže nam snagu spasenja u domu Davida, sluge svojega,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
kao što obeća na usta svetih proroka svojih odvijeka: (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
spasiti nas od neprijatelja naših i od ruke sviju koji nas mrze;
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
iskazati dobrotu ocima našim i sjetiti se svetog Saveza svojega,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
zakletve kojom se zakle Abrahamu, ocu našemu: da će nam dati
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
te mu, izbavljeni iz ruku neprijatelja, služimo bez straha
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
u svetosti i pravednosti pred njim u sve dane svoje.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
A ti, dijete, prorok ćeš se Svevišnjega zvati jer ćeš ići pred Gospodinom da mu pripraviš putove,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
da pružiš spoznaju spasenja narodu njegovu po otpuštenju grijeha njihovih,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
darom premilosrdnog srca Boga našega po kojem će nas pohoditi Mlado sunce s visine
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
da obasja one što sjede u tmini i sjeni smrtnoj, da upravi noge naše na put mira.”
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
Dječak je međutim rastao i duhom jačao. Boravio je u pustinji sve do dana svoga javnog nastupa pred Izraelom.

< Luka 1 >