< Firistoci 9 >

1 A rana ta takwas, Musa ya kira Haruna da’ya’yansa maza da kuma dattawan Isra’ila.
در روز هشتم، موسی هارون و پسرانش را با مشایخ اسرائیل جمع کرد
2 Ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki ɗan maraƙi domin hadayarka don zunubi da kuma ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, dukan biyu su kasance marar lahani, ka miƙa su a gaban Ubangiji.
و به هارون گفت: «یک گوسالهٔ نر سالم و بی‌عیب برای قربانی گناه و یک قوچ سالم و بی‌عیب برای قربانی سوختنی بگیر و آنها را به حضور خداوند تقدیم کن.
3 Sa’an nan ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ku ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa,
بعد به قوم اسرائیل بگو که یک بزغالهٔ نر برای قربانی گناه خود و یک گوساله و یک بره که هر دو یک ساله و بی‌عیب باشند برای قربانی سوختنی بیاورند.
4 da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.’”
همچنین قوم اسرائیل باید یک گاو و یک قوچ برای قربانی سلامتی، و آرد مخلوط با روغن زیتون برای هدیهٔ آردی به خداوند تقدیم کنند زیرا امروز خداوند بر ایشان ظاهر خواهد شد.»
5 Suka ɗauki abubuwan da Musa ya umarta zuwa gaban Tentin Sujada, sai dukan jama’a suka zo kusa suka tsaya a gaban Ubangiji.
پس قوم آنچه را که موسی امر فرموده بود، جلوی خیمۀ ملاقات آوردند و تمام جماعت نزدیک شده، در حضور خداوند ایستادند.
6 Sa’an nan Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarce ku ku yi, domin ɗaukakar Ubangiji za tă bayyana gare ku.”
موسی به ایشان گفت: «خداوند فرموده دستورهای او را انجام دهید تا حضور پرجلال خود را بر شما ظاهر کند.»
7 Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama’a. Ka kuma kawo hadayar jama’a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.”
آنگاه موسی به هارون گفت: «نزدیک مذبح بیا و همان‌طور که خداوند فرموده است قربانی گناه و قربانی سوختنی خود را تقدیم کرده، برای خود کفاره کن و سپس قربانیهای قوم را تقدیم نموده، برای آنها کفاره نما.»
8 Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa.
بنابراین هارون به مذبح نزدیک شد و گوسالهٔ قربانی گناه خود را ذبح کرد.
9 ’Ya’yan Haruna maza suka kawo masa jinin, ya kuma tsoma yatsarsa a cikin jinin ya zuba cikin ƙahonin bagade; sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden.
پسرانش خون گوساله را پیش وی آوردند و او انگشت خود را در خون فرو برد و بر شاخهای مذبح مالید و باقیماندهٔ خون را به پای مذبح ریخت.
10 A kan bagaden, ya ƙone kitsen, ƙodojin, da abin da ya rufe hanta, daga hadaya don zunubi, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
بعد همان‌طور که خداوند به موسی دستور داده بود، چربی، قلوه‌ها و سفیدی روی جگر قربانی گناه را بر مذبح،
11 Naman da fatar kuwa ya ƙone waje da sansanin.
و گوشت و پوست آن را بیرون از اردوگاه سوزانید.
12 Sa’an nan ya yanka hadaya ta ƙonawa.’Ya’yan Haruna maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagaden.
پس از آن هارون قربانی سوختنی را ذبح کرد و پسرانش خون قربانی را آوردند و هارون آن را بر چهار طرف مذبح پاشید.
13 Suka miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa-gunduwa, haɗe da kan, ya kuwa ƙone su a bisa bagaden.
ایشان کله و قطعه‌های دیگر حیوان را نزد هارون آوردند و او آنها را بر مذبح سوزانید.
14 Sai ya wanke kayan ciki da ƙafafun, ya kuwa ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a kan bagade.
دل و روده و پاچه‌ها را شست و اینها را نیز به عنوان قربانی سوختنی بر مذبح سوزانید.
15 Sa’an nan Haruna ya kawo hadayar da take domin mutane. Ya ɗauki akuya ta hadaya don zunubin mutane, ya yanka shi, ya miƙa shi domin hadaya don zunubi kamar yadda ya yi da na farko.
سپس هارون قربانی قوم اسرائیل را تقدیم کرد. او بز قربانی گناه قوم را ذبح نموده، آن را مانند قربانی گناه خود برای گناه قوم تقدیم کرد.
16 Ya kawo hadaya ta ƙonawa ya kuma miƙa ta yadda aka tsara.
آنگاه مطابق قوانین، قربانی سوختنی ایشان را به خداوند تقدیم نمود.
17 Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗiba a tafi hannu ya ƙone a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa ta safe.
بعد هدیهٔ آردی را آورد و مشتی از آن را گرفت و بر مذبح سوزانید. (این قربانی غیر از قربانی سوختنی‌ای بود که هر روز صبح تقدیم می‌شد.)
18 Haruna ya yanka maraƙin da ragon a matsayin hadaya ta salama domin mutane.’Ya’yansa maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagade.
پس از آن هارون گاو و قوچ را به عنوان قربانی سلامتی قوم ذبح کرد. پسران هارون خون قربانی را نزد او آوردند و او آن را بر چهار طرف مذبح پاشید.
19 Amma sashen kitsen maraƙin da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji da kuma kitsen da ya rufe hanta,
سپس چربی گاو و قوچ را که شامل چربی داخل شکم و قلوه‌ها و سفیدی روی جگر گاو و قوچ می‌شد، گرفت
20 suka shimfiɗa waɗannan a kan ƙirjin, sa’an nan Haruna ya ƙone kitsen a kan bagade.
و آنها را روی سینه‌های حیوان گذاشته، نزدیک مذبح آورد و تمام چربی را روی مذبح سوزانید.
21 Sai Haruna ya kaɗa ƙirjin da kuma cinyar dama a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa, kamar yadda Musa ya umarta.
همان‌طور که موسی دستور داده بود، هارون سینه‌ها، و رانهای راست حیوان را به عنوان هدیهٔ مخصوص در حضور خداوند تکان داد.
22 Sa’an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa wajen mutane ya sa musu albarka. Da yake ya miƙa hadaya don zunubi, hadaya ta ƙonawa da kuma hadaya ta salama, sai ya sauka.
پس از تقدیم قربانیها، هارون دستهای خود را به طرف قوم اسرائیل دراز کرده، ایشان را برکت داد و از مذبح به زیر آمد.
23 Sai Musa da Haruna suka shiga cikin Tentin Sujada. Da suka fita, sai suka sa wa mutane albarka; sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutane.
موسی و هارون به خیمۀ ملاقات رفتند. وقتی از آنجا بیرون آمدند قوم اسرائیل را برکت دادند. آنگاه حضور پرجلال خداوند بر تمام جماعت ظاهر شد
24 Sai wuta ta fito daga gaban Ubangiji ta cinye hadaya ta ƙonawa da sassan kitsen a kan bagaden. Sa’ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suna farin ciki, suka fāɗi rubda ciki, suka yi sujada.
و از حضور خداوند آتش فرود آمده، قربانی سوختنی و چربی روی مذبح را بلعید. بنی‌اسرائیل وقتی این را دیدند، فریاد برآورده، در حضور خداوند به خاک افتادند.

< Firistoci 9 >