< Firistoci 9 >

1 A rana ta takwas, Musa ya kira Haruna da’ya’yansa maza da kuma dattawan Isra’ila.
Ja tapahtui kahdeksantena päivänä, että Moses kutsui Aaronin ja hänen poikansa, niin myös vanhimmat Israelista.
2 Ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki ɗan maraƙi domin hadayarka don zunubi da kuma ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, dukan biyu su kasance marar lahani, ka miƙa su a gaban Ubangiji.
Ja sanoi Aaronille: ota sinulles nuori vasikka rikosuhriksi, ja oinas polttouhriksi, molemmat virheettömät, ja tuo Herran eteen.
3 Sa’an nan ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ku ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa,
Ja puhu Israelin lapsille, sanoen: ottakaat kauris rikosuhriksi, ja vasikka ja karitsa, molemmat vuosikuntaiset ja virheettömät, polttouhriksi.
4 da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.’”
Ja myös härkä ja oinas uhrattaa kiitosuhriksi Herran edessä, ja ruokauhri sekoitettu öljyllä; sillä tänäpänä ilmestyy Herra teille.
5 Suka ɗauki abubuwan da Musa ya umarta zuwa gaban Tentin Sujada, sai dukan jama’a suka zo kusa suka tsaya a gaban Ubangiji.
Ja he toivat ne kuin Moses käskenyt oli, seurakunnan majan oven eteen: ja kaikki kansa kävi edes, ja seisoi Herran edessä.
6 Sa’an nan Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarce ku ku yi, domin ɗaukakar Ubangiji za tă bayyana gare ku.”
Niin sanoi Moses: tämä on se, minkä Herra käskenyt on teidän tehdä, ja Herran kunnia ilmestyy teille.
7 Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama’a. Ka kuma kawo hadayar jama’a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.”
Ja Moses sanoi Aaronille: astu alttarin tykö, ja tee rikosuhris, ja poltouhris ja sovita sinuas ja kansaa, ja tee sitte kansan uhri ja sovita heitä, niinkuin Herra käskenyt on.
8 Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa.
Ja Aaron astui alttarin tykö ja teurasti vasikan rikosuhriksensa.
9 ’Ya’yan Haruna maza suka kawo masa jinin, ya kuma tsoma yatsarsa a cikin jinin ya zuba cikin ƙahonin bagade; sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden.
Ja Aaronin pojat kantoivat veren hänen tykönsä, ja hän kasti sormensa vereen, ja sivui alttarin sarviin, ja veren kaasi hän alttarin pohjalle.
10 A kan bagaden, ya ƙone kitsen, ƙodojin, da abin da ya rufe hanta, daga hadaya don zunubi, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Ja lihavuuden, ja munaskuut, ja maksan kalvon rikosuhrista, poltti hän alttarilla, niinkuin Herra oli Mosekselle käskenyt.
11 Naman da fatar kuwa ya ƙone waje da sansanin.
Mutta lihan ja nahan poltti hän tulessa ulkona leiristä.
12 Sa’an nan ya yanka hadaya ta ƙonawa.’Ya’yan Haruna maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagaden.
Sitte hän teurasti polttouhrin, ja Aaronin pojat kantoivat veren hänen tykönsä, ja hän priiskotti sen alttarille ympäri.
13 Suka miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa-gunduwa, haɗe da kan, ya kuwa ƙone su a bisa bagaden.
Ja he toivat myös polttouhrin hänelle, kappaleiksi leikatun, ja pään, ja hän poltti ne alttarilla.
14 Sai ya wanke kayan ciki da ƙafafun, ya kuwa ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a kan bagade.
Ja hän pesi sisällykset ja jalat, ja poltti ne polttouhrin päällä, alttarilla.
15 Sa’an nan Haruna ya kawo hadayar da take domin mutane. Ya ɗauki akuya ta hadaya don zunubin mutane, ya yanka shi, ya miƙa shi domin hadaya don zunubi kamar yadda ya yi da na farko.
Sitte kantoi hän kansan uhrin edes, ja otti kauriin, joka oli kansan rikosuhri, ja teurasti sen, ja teki siitä rikosuhrin, niinkuin sen entisenkin.
16 Ya kawo hadaya ta ƙonawa ya kuma miƙa ta yadda aka tsara.
Ja hän toi myös polttouhrin, ja valmisti sen tavan jälkeen.
17 Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗiba a tafi hannu ya ƙone a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa ta safe.
Ja toi ruokauhrin, ja otti siitä pivonsa täyden, ja poltti ne alttarilla, paitsi aamullista polttouhria.
18 Haruna ya yanka maraƙin da ragon a matsayin hadaya ta salama domin mutane.’Ya’yansa maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagade.
Sitte teurasti hän härjän ja oinaan kansan kiitosuhriksi, ja Aaronin pojat kantoivat veren hänelle, ja hän priiskotti sen alttarin ympäri.
19 Amma sashen kitsen maraƙin da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji da kuma kitsen da ya rufe hanta,
Mutta härjän lihavuuden, ja oinaan saparon, ja sisällysten lihavuuden, ja munaskuut, ja maksan kalvon:
20 suka shimfiɗa waɗannan a kan ƙirjin, sa’an nan Haruna ya ƙone kitsen a kan bagade.
Kaiken tämän lihavuuden panivat he rintain päälle, ja polttivat lihavuuden alttarilla.
21 Sai Haruna ya kaɗa ƙirjin da kuma cinyar dama a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa, kamar yadda Musa ya umarta.
Mutta rinnat ja oikian lavan häälytti Aaron häälytykseksi Herran edessä, niinkuin Herra oli käskenyt Mosekselle.
22 Sa’an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa wajen mutane ya sa musu albarka. Da yake ya miƙa hadaya don zunubi, hadaya ta ƙonawa da kuma hadaya ta salama, sai ya sauka.
Ja Aaron nosti kätensä kansan puoleen, ja siunasi heitä: ja sittekuin hän rikosuhrin, polttouhrin ja kiitosuhrin tehnyt oli, meni hän alas.
23 Sai Musa da Haruna suka shiga cikin Tentin Sujada. Da suka fita, sai suka sa wa mutane albarka; sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutane.
Niin Moses ja Aaron menivät seurakunnan majaan, ja koska he jälleen sieltä läksivät, siunasivat he kansan. Niin Herran kunnia ilmestyi kaiken kansan edessä:
24 Sai wuta ta fito daga gaban Ubangiji ta cinye hadaya ta ƙonawa da sassan kitsen a kan bagaden. Sa’ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suna farin ciki, suka fāɗi rubda ciki, suka yi sujada.
Sillä tuli tuli Herralta alas, ja kulutti polttouhrin, ja sen lihavuuden, alttarilta: ja koska kaikki kansa sen näki, riemuitsivat he sangen suuresti, ja lankesivat maahan kasvoillensa.

< Firistoci 9 >