< Firistoci 9 >

1 A rana ta takwas, Musa ya kira Haruna da’ya’yansa maza da kuma dattawan Isra’ila.
And it came to pass on the eighth day, that Moses called for Aaron, and for his sons, —and for the elders of Israel;
2 Ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki ɗan maraƙi domin hadayarka don zunubi da kuma ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, dukan biyu su kasance marar lahani, ka miƙa su a gaban Ubangiji.
and said unto Aaron—Take for thyself a choice calf, as a sin-bearer, and a ram for an ascending-sacrifice, each without defect, —and bring them near before Yahweh;
3 Sa’an nan ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ku ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa,
and unto the sons of Israel, shalt thou speak, saying, —Take ye a he-goat, as a sin-bearer, and a calf and a young sheep, each a year old, without defect for an ascending-sacrifice;
4 da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.’”
and an ox and a ram for peace-offerings, to sacrifice before Yahweh, and a meal-offering overflowed with oil, —for, to-day, doth, Yahweh, appear unto you.
5 Suka ɗauki abubuwan da Musa ya umarta zuwa gaban Tentin Sujada, sai dukan jama’a suka zo kusa suka tsaya a gaban Ubangiji.
So they brought that which Moses commanded before the tent of meeting, —and all the assembly drew near, and stood before Yahweh.
6 Sa’an nan Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarce ku ku yi, domin ɗaukakar Ubangiji za tă bayyana gare ku.”
And Moses said—This, is the thing which Yahweh hath commanded that ye shall do, —that the glory of Yahweh may appear unto you.
7 Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama’a. Ka kuma kawo hadayar jama’a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.”
and Moses said unto Aaron—Draw near unto the altar, and offer thy sin-bearer and thine ascending-sacrifice, and put a propitiatory-covering about thyself and about the people, —and offer the oblation of the people and put a propitiatory-covering about them, As Yahweh hath commanded.
8 Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa.
So Aaron drew near unto the altar, —and slew the sin-bearing calf which was for himself;
9 ’Ya’yan Haruna maza suka kawo masa jinin, ya kuma tsoma yatsarsa a cikin jinin ya zuba cikin ƙahonin bagade; sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden.
and the sons of Aaron brought the blood unto him, and he dipped his finger in the blood, and put [thereof] upon the horns of the altar, —and the [remainder of the] blood, poured he out at the base of the altar;
10 A kan bagaden, ya ƙone kitsen, ƙodojin, da abin da ya rufe hanta, daga hadaya don zunubi, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
and with the fat and the kidneys and the caul a from the liver, of the sin-bearer, made he a perfume at the altar, —As Yahweh commanded Moses.
11 Naman da fatar kuwa ya ƙone waje da sansanin.
But, the flesh and the skin, consumed he with fire, outside the camp.
12 Sa’an nan ya yanka hadaya ta ƙonawa.’Ya’yan Haruna maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagaden.
Then slew he the ascending-sacrifice, —and the sons of Aaron presented unto him the blood, and he dashed it against the altar round about.
13 Suka miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa-gunduwa, haɗe da kan, ya kuwa ƙone su a bisa bagaden.
And the ascending-sacrifice, presented they unto him piece by piece thereof also the head, —and he made a perfume upon the altar:
14 Sai ya wanke kayan ciki da ƙafafun, ya kuwa ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a kan bagade.
and he bathed the inwards and the legs, —and made a perfume upon the ascending-sacrifice at the altar.
15 Sa’an nan Haruna ya kawo hadayar da take domin mutane. Ya ɗauki akuya ta hadaya don zunubin mutane, ya yanka shi, ya miƙa shi domin hadaya don zunubi kamar yadda ya yi da na farko.
Then brought he near the oblation of the people, —and took the sin-bearing goat which pertained to the people, and slew it and made therewith a sin-bearer, like the first.
16 Ya kawo hadaya ta ƙonawa ya kuma miƙa ta yadda aka tsara.
Then brought he near the ascending-sacrifice, —and offered it, according to the regulation,
17 Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗiba a tafi hannu ya ƙone a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa ta safe.
Then brought he near the meal-offering, and filled his hand therefrom, and made a perfume upon the altar, —in addition to the ascending-sacrifice of the morning.
18 Haruna ya yanka maraƙin da ragon a matsayin hadaya ta salama domin mutane.’Ya’yansa maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagade.
Then slew he the ox, and the ram, as a peace-offering, which pertained unto the people, —and the sons of Aaron presented the blood unto him, and he dashed it against the altar, round about;
19 Amma sashen kitsen maraƙin da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji da kuma kitsen da ya rufe hanta,
and the portions of fat from the ox, —and from the ram, the fat-tail, and the covering, and the kidneys, and the caul of the liver;
20 suka shimfiɗa waɗannan a kan ƙirjin, sa’an nan Haruna ya ƙone kitsen a kan bagade.
and they put the portions of fat upon the breasts, —and he made a perfume with the fat at the altar;
21 Sai Haruna ya kaɗa ƙirjin da kuma cinyar dama a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa, kamar yadda Musa ya umarta.
but the breasts and the right shoulder, did Aaron wave as a wave-offering, before Yahweh, —as Moses commanded,
22 Sa’an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa wajen mutane ya sa musu albarka. Da yake ya miƙa hadaya don zunubi, hadaya ta ƙonawa da kuma hadaya ta salama, sai ya sauka.
Then Aaron lifted up his hands towards the people, and blessed them, —and he came down from offering the sin-bearer, and the ascending-sacrifice and the peace-offering.
23 Sai Musa da Haruna suka shiga cikin Tentin Sujada. Da suka fita, sai suka sa wa mutane albarka; sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutane.
And when Moses and Aaron had entered into the tent of meeting, —and had come forth, and blessed the people, then appeared the glory of Yahweh, unto all the people;
24 Sai wuta ta fito daga gaban Ubangiji ta cinye hadaya ta ƙonawa da sassan kitsen a kan bagaden. Sa’ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suna farin ciki, suka fāɗi rubda ciki, suka yi sujada.
yea, there came forth fire from before Yahweh, and consumed upon the altar, the ascending-sacrifice and the portions of fat, —and all the people beheld and shouted, and fell down upon their faces.

< Firistoci 9 >