< Firistoci 8 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And he spoke Yahweh to Moses saying.
2 “Kawo Haruna da’ya’yansa maza, ka ɗauki rigunansu, man keɓewa, bijimi domin hadaya don zunubi,’yan raguna biyu da kuma kwandon da yake da burodi marar yisti,
Take Aaron and sons his with him and the garments and [the] oil of anointing and - [the] bull of the sin offering and [the] two the rams and [the] basket of unleavened bread.
3 ka kuma tara dukan jama’a a ƙofar Tentin Sujada.”
And all the congregation assemble to [the] entrance of [the] tent of meeting.
4 Sai Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi, jama’a kuwa suka taru a ƙofar Tentin Sujada.
And he did Moses just as he had commanded Yahweh him and it assembled the congregation to [the] entrance of [the] tent of meeting.
5 Sai Musa ya ce wa jama’ar, “Ga abin da Ubangiji ya umarta a yi.”
And he said Moses to the congregation this [is] the word which he has commanded Yahweh to do.
6 Sa’an nan Musa ya kawo Haruna da’ya’yansa maza gaba, ya kuma wanke su da ruwa.
And he presented Moses Aaron and sons his and he washed them with water.
7 Ya sa wa Haruna taguwa, ya ɗaura igiya kewaye da shi, ya sa masa riga, ya sa masa efod. Ya kuma ɗaura masa efod wanda aka yi masa saƙar gwaninta.
And he put on him the tunic and he girded him with the sash and he clothed him the robe and he put on him the ephod and he girded him with [the] girdle of the ephod and he girded [the] ephod to him with it.
8 Ya sa masa ƙyallen maƙalawa a ƙirji, ya kuma sa Urim da Tummim a ƙyallen maƙalawa a ƙirjin.
And he placed on him the breastpiece and he put into the breastpiece the Urim and the Thummim.
9 Sai ya naɗa masa rawani, daga gaban rawanin ya sa allon zinariya, wato, kambi tsattsarka, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he placed the turban on head his and he placed on the turban to [the] front of face his [the] plate of gold [the] crown of holiness just as he had commanded Yahweh Moses.
10 Sa’an nan Musa ya ɗauki man keɓewa ya keɓe tabanakul da kuma kowane abin da yake cikinsa, ta haka ya tsarkake su.
And he took Moses [the] oil of anointing and he anointed the tabernacle and all that [was] in it and he set apart as holy them.
11 Ya yayyafa mai a kan bagade sau bakwai, yana keɓe bagade da dukan kayayyaki, da daro, da abin da yake tsaya a kai, don yă tsarkake su.
And he spattered some of it on the altar seven times and he anointed the altar and all utensils its and the laver and base its to set apart as holy them.
12 Ya zuba man keɓewa a kan Haruna, ya kuma keɓe shi don yă tsarkake shi.
And he poured some of [the] oil of anointing on [the] head of Aaron and he anointed him to set apart as holy him.
13 Sa’an nan ya kawo’ya’yan Haruna maza, ya sa musu taguwoyi, ya ɗaɗɗaura igiyoyi kewaye da su, ya kuma sa musu huluna yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he presented Moses [the] sons of Aaron and he clothed them tunics and he girded them a sash and he bound on to them headdresses just as he had commanded Yahweh Moses.
14 Sa’an nan ya miƙa bijimi domin hadaya don zunubi, sai Haruna da’ya’yansa suka ɗibiya hannuwansu a bijimin.
And he brought near [the] bull of the sin offering and he leaned Aaron and sons his hands their on [the] head of [the] bull of the sin offering.
15 Musa ya yanka bijimin ya ɗauki jinin, ya sa yatsarsa ya zuba a dukan ƙahonin bagade don yă tsarkake bagaden. Ya zuba sauran jinin a gindin bagade. Ta haka ya tsarkake shi don yă yi kafara dominsa.
And he cut [the] throat of [it] and he took Moses the blood and he put [it] on [the] horns of the altar all around with finger his and he cleansed from sin the altar and the blood he poured to [the] base of the altar and he set apart as holy it to make atonement on it.
16 Musa ya ɗebo dukan kitsen da yake kewaye da kayan ciki, da kuma wanda ya rufe hanta, da ƙodojin, da kuma kitsensu, ya kuma ƙone su a kan bagade.
And he took all the fat which [was] on the entrails and [the] lobe of the liver and [the] two the kidneys and fat their and he made [them] smoke Moses the altar towards.
17 Amma bijimin da fatarsa da namansa da kuma ƙashinsa ya ƙone su a bayan sansani, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And the bull and hide its and flesh its and offal its he burned with fire from [the] outside of the camp just as he had commanded Yahweh Moses.
18 Sa’an nan ya miƙa ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan rago.
And he presented [the] ram of the burnt offering and they leaned Aaron and sons his hands their on [the] head of the ram.
19 Sa’an nan Musa ya yanka ɗan ragon, ya kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagaden.
And he cut [the] throat of [it] and he sprinkled Moses the blood on the altar all around.
20 Ya yanka ragon gunduwa-gunduwa ya ƙone kan, ya kuma ƙone gunduwa-gunduwan da kitsen.
And the ram he cut in pieces into pieces its and he made smoke Moses the head and the pieces and the suet.
21 Ya wanke kayan cikin da ƙafafun a ruwa, ya kuma ƙone dukan ragon a bisa bagade kamar hadaya ta ƙonawa, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And the entrails and the legs he washed with water and he made smoke Moses all the ram the altar towards [was] a burnt offering it to an odor of soothing [was] a fire offering it to Yahweh just as he had commanded Yahweh Moses.
22 Sai ya miƙa ɗayan ɗan ragon, ɗan ragon naɗin, sai Haruna da’ya’yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan ɗan ragon.
And he presented the ram second [the] ram of installation offering and they leaned Aaron and sons his hands their on [the] head of the ram.
23 Musa kuwa ya yanka ɗan ragon ya ɗibi jinin ya sa leɓatun kunnen dama na Haruna, ya kuma sa a babbar yatsarsa ta hannun dama da kuma a babbar yatsar ƙafarsa ta dama.
And he cut [the] throat of [it] - and he took Moses some of blood its and he put [it] on [the] lobe of [the] ear of Aaron right and on [the] thumb of hand his right and on [the] big toe of foot his right.
24 Musa ya kuma kawo’ya’yan Haruna gaba, ya sa jini a leɓatun kunnuwansu na dama, ya kuma sa a manyan yatsotsinsu na hannun dama da kuma a manyan yatsotsinsu na ƙafafunsu na dama. Sa’an nan ya yayyafa jinin a kowane gefen bagade.
And he presented [the] sons of Aaron and he put Moses some of the blood on [the] lobe of ear their right and on [the] thumb of hand their right and on [the] big toe of foot their right and he sprinkled Moses the blood on the altar all around.
25 Ya ɗibi kitsen, da wutsiya mai kitse, da kuma dukan kitsen da ke kewaye da kayan ciki, da wanda ya rufe hanta, ƙodoji biyu da kitsensu da kuma cinya ta dama.
And he took the fat and the fat tail and all the fat which [was] on the entrails and [the] lobe of the liver and [the] two the kidneys and fat their and [the] thigh of the right.
26 Sa’an nan daga cikin kwandon burodi marar yisti wanda yake a gaban Ubangiji, ya ɗauko dunƙulen burodi, da kuma guda da aka yi da mai, da kuma ƙosai; ya sa waɗannan a sassan kitsen, da kuma a cinya ta dama.
And from [the] basket of unleavened bread which - [was] before Yahweh he took a round perforated bread of unleavened bread one and a round perforated bread of bread of oil one and a thin bread one and he placed [them] on the fat and on [the] thigh of the right.
27 Ya sa waɗannan a hannuwan Haruna da’ya’yansa, suka kuma kaɗa su a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
And he put everything on [the] palms of Aaron and on [the] palms of sons his and he waved them a wave-offering before Yahweh.
28 Sa’an nan Musa ya karɓe su daga hannuwansu ya ƙone a bagade a bisa hadaya ta ƙonawa a matsayin hadaya ta naɗi, mai daɗin ƙanshi, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
And he took Moses them from on palms their and he made [them] smoke the altar towards on the burnt offering [were] installation offerings they to an odor of soothing [was] a fire offering it to Yahweh.
29 Ya kuma ɗauki ƙirjin; rabon Musa na ɗan ragon naɗi, ya kaɗa shi a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
And he took Moses the breast and he waved it a wave-offering before Yahweh from [the] ram of installation offering to Moses it belonged to a portion just as he had commanded Yahweh Moses.
30 Sai Musa ya ɗibi man keɓewa da jini daga bagade, ya yayyafa su a kan Haruna da rigunansa, da kuma a kan’ya’yansa da rigunansu, don yă tsarkake Haruna da rigunansa da kuma’ya’yansa da rigunansu.
And he took Moses some of [the] oil of anointing and some of the blood which [was] on the altar and he spattered [it] on Aaron on garments his and on sons his and on [the] garments of sons his with him and he set apart as holy Aaron garments his and sons his and [the] garments of sons his with him.
31 Sai Musa ya ce wa Haruna da’ya’yansa maza, “Ku dafa naman a ƙofar Tentin Sujada, ku kuma ci shi a can tare da burodi daga kwandon naɗi, yadda na umarta, cewa, ‘Haruna da’ya’yansa maza za su ci shi.’
And he said Moses to Aaron and to sons his boil the meat [the] entrance of [the] tent of meeting and there you will eat it and the bread which [is] in [the] basket of the installation offering just as I commanded saying Aaron and sons his they will eat it.
32 Sa’an nan ku ƙone sauran naman da kuma burodin.
And the remainder in the meat and in the bread with fire you will burn.
33 Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada har kwana bakwai, sai ranakun naɗi suka cika, gama naɗinku zai ɗauki kwana bakwai.
And from [the] entrance of [the] tent of meeting not you must go out seven days until [the] day are completed [the] days of installation your for seven days he will fill hand your.
34 Abin da aka yi a yau umarni ne daga Ubangiji don yin kafara saboda ku.
Just as someone has done on the day this he has commanded Yahweh to do to make atonement on you.
35 Dole ku kasance a ƙofar Tentin Sujada dare da rana har kwana bakwai, ku kuma yi abin da Ubangiji yake bukata, don kada ku mutu; gama abin da aka umarce ni ke nan.”
And [the] entrance of [the] tent of meeting you will remain by day and night seven days and you will keep [the] duty of Yahweh and not you will die for thus I have been commanded.
36 Saboda haka Haruna da’ya’yansa maza suka yi kome da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
And he did Aaron and sons his all the things which he had commanded Yahweh by [the] hand of Moses.

< Firistoci 8 >