< Firistoci 7 >
1 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodi na hadaya don laifi, hadaya ce tsattsarka.
Og dette er loven om skyldofferet: Det er høihellig.
2 Za a yanka hadaya don laifi a inda ake yanka hadaya ta ƙonawa, za a kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagade.
På det sted hvor brennofferet slaktes, skal skyldofferet slaktes, og dets blod skal sprenges rundt om på alteret.
3 Za a miƙa kitsen abin hadaya duka, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki,
Og alt fettet skal ofres, både halen og fettet som dekker innvollene,
4 da ƙodoji biyu da kitsen da yake a bisansu kusa da kwiɓi, da kuma rufin hanta, wanda za a cire tare da ƙodoji.
og begge nyrene med det fett som er på dem, ved lendene, og den store leverlapp; den skal tas ut sammen med nyrene.
5 Firist zai ƙone su a kan bagade, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji. Hadaya ce don laifi.
Og presten skal brenne det på alteret som ildoffer til Herren; det er et skyldoffer.
6 Kowane da namiji cikin iyalin firistoci zai iya ci. Sai a tsattsarkan wuri ne za a ci; gama abu mafi tsarki ne.
Alt mannkjønn blandt prestene kan ete det; på et hellig sted skal det etes; det er høihellig.
7 “‘Hadaya don laifi kamar hadaya don zunubi take, saboda haka ƙa’ida hanyar yinsu iri ɗaya ce. Su ɗin na firist da ya yi kafara da su ne.
Med skyldofferet skal det være likesom med syndofferet; det gjelder én lov for begge; den prest som gjør soning med det, ham skal det tilhøre.
8 Firist da ya miƙa hadaya ta ƙonawa domin wani, zai iya ajiye fatar wa kansa.
Når en prest ofrer brennoffer for nogen, så skal huden av det brennoffer han har ofret, tilhøre den samme prest.
9 Kowace hadaya ta garin da aka toya a tanda, ko aka dafa a tukunya ko a kan kaskon tuya, na firist da ya miƙa ta ne,
Og ethvert matoffer som bakes i ovn, eller som stekes i panne eller på helle, skal tilhøre den prest som ofrer det.
10 kuma kowace hadaya ta gari wadda aka kwaɓa da mai, ko wadda ba a kwaɓa ba, ita ma, ta dukan’ya’ya Haruna ne maza.
Og ethvert matoffer som er blandet med olje, eller som er tørt, skal høre alle Arons sønner til, den ene som den andre.
11 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodin hadaya don zumuncin da mutum zai iya miƙa ga Ubangiji.
Og dette er loven om takkofferet som ofres til Herren:
12 “‘In ya miƙa hadayar a matsayin hadaya ta godiya ce, to, zai miƙa ta tare da burodi mai kauri marar yisti, wanda aka kwaɓa da mai, da burodi marar kauri, wanda aka shafa wa mai, da kuma burodi mai kauri da aka yi da gari mai laushi wanda aka kwaɓa sosai da mai.
Dersom nogen ofrer det til lovprisning, så skal han foruten slaktofferet som bæres frem til lovprisning, ofre usyrede kaker med olje i og usyrede brødleiver smurt med olje, og fint mel knadd til kaker med olje i.
13 Tare da hadayarsa don zumunci ta godiya, zai miƙa dunƙulen burodin da aka yi da yisti.
Dette er den offergave han skal bære frem foruten det slaktoffer som bæres frem til takk og lovprisning, og dessuten syrede kaker.
14 Zai kuma kawo ɗaya daga kowace a matsayin hadaya, baiko ne ga Ubangiji. Wannan zai zama na firist da ya yafa jinin hadaya ta salama ne.
Av dette offer skal han bære frem én kake av hvert slag som gave til Herren; det skal tilhøre presten som sprenger takkofferets blod på alteret.
15 Za a ci wannan nama na hadaya don zumunci ta godiya a ranar da aka miƙa ta, kada yă bar wani abu daga naman yă kwana.
Kjøttet av et takkoffer som bæres frem til lovprisning, skal etes på den dag det ofres; intet av det skal bli liggende til om morgenen.
16 “‘In hadayarsa cika wa’adin rantsuwa ce ko kuwa ta yardar rai ce, sai a ci hadayar a ranar da ya miƙa ta, amma za a iya cin duk abin da ya rage kashegari.
Dersom nogens slaktoffer er et lovet offer eller et frivillig offer, skal det etes på den dag det ofres; men det som levnes, kan etes den næste dag.
17 Duk naman hadayar da ya rage har kwana uku, dole a ƙone shi.
Men hvad som enda blir tilovers av slaktofferets kjøtt, skal på den tredje dag brennes op med ild.
18 Idan aka ci naman hadayarsa ta salama a rana ta uku, ba za a karɓi wanda ya ba da hadayar har ya sami albarkar hadayar ba, naman zai zama abin ƙyama, duk wanda ya ci kuwa ya yi laifi.
Om nogen på den tredje dag eter av takkofferets kjøtt, da har Herren ikke velbehag i offeret; det skal ikke regnes den som ofret det, til gode, det skal være en vederstyggelighet, og den som eter av det, gjør en misgjerning som han kommer til å bøte for.
19 “‘Ba za a ci naman da ya taɓa wani abu marar tsarki ba; dole a ƙone shi. Game da sauran nama, kowa da yake mai tsarki zai iya ci.
Kjøtt som kommer nær noget urent, skal ikke etes, det skal brennes op med ild; ellers kan alle som er rene, ete av kjøttet.
20 Amma in wani wanda ba shi da tsarki ya ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
Men den som eter kjøtt av Herrens takkoffer mens det er noget urent på ham, han skal utryddes av sitt folk.
21 Idan wani mutum ya taɓa abu marar tsarki, ko mutum ne, ko dabba ce, ko wani abu na banƙyama, ya kuma ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.’”
Og når nogen rører ved noget urent, enten det er et menneskes urenhet eller et urent dyr eller noget annet urent og vederstyggelig, og så eter av kjøttet av Herrens takkoffer, da skal han utryddes av sitt folk.
22 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
23 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Kada ku ci wani kitsen shanu, ko na tumaki, ko kuwa na awaki.
Tal til Israels barn og si: I skal ikke ete fett av okse eller får eller gjet.
24 Za a iya yin wani amfani da kitsen dabbar da ta mutu mushe, ko kitsen dabbar da namun jeji su yayyaga, amma kada a kuskura a ci.
Fettet av et selvdødt dyr eller av et sønderrevet dyr kan brukes til alle slags arbeid; men ete det må I ikke;
25 Duk wanda ya ci kitsen dabbar da aka miƙa ta wuta ga Ubangiji, za a fid da shi daga mutanensa.
for hver den som eter fettet av noget dyr som det ofres ildoffer av til Herren, han skal utryddes av sitt folk.
26 Kuma duk inda kuke zama, ba za ku ci jinin wani tsuntsu ko na dabba ba.
Og blod skal I ikke ete, hverken av fugl eller fe, hvor I så bor.
27 Duk wanda ya ci jini, za a fid da mutumin daga mutanensa.’”
Enhver som nogensinne eter blod, han skal utryddes av sitt folk.
28 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
29 “Faɗa wa Isra’ilawa, ‘Duk wanda ya kawo hadaya ta salama ga Ubangiji, sai ya kawo hadayarsa ga Ubangiji daga cikin hadayu na salama.
Tal til Israels barn og si: Den som ofrer sitt takke-slaktoffer til Herren, han skal bære frem for Herren sin offergave av sitt takke-slaktoffer.
30 Da hannuwansa zai kawo hadayar da za a ƙona ga Ubangiji; zai kawo kitsen tare da ƙirjin, yă kuma kaɗa ƙirjin a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
Med egne hender skal han bære frem Herrens ildoffer; både fettet og brystet skal han bære frem, og brystet skal svinges for Herrens åsyn.
31 Firist zai ƙone kitsen a bisa bagade, amma ƙirjin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza.
Og presten skal brenne fettet på alteret; men brystet skal høre Aron og hans sønner til.
32 Za ku ba da cinya ta dama ta hadaya don zumuncinku ga firist a matsayin baiko.
Og det høire lår skal I gi presten som gave av eders takkoffer.
33 Ɗan Haruna da ya miƙa jini da kitsen hadaya ta salama, zai ɗauki cinyar tă zama rabonsa.
Den av Arons sønner som ofrer takkoffer-blodet og fettet, han skal ha det høire lår som sin del;
34 Daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa, na ɗauki ƙirjin da aka kaɗa da kuma cinyar da aka miƙa, na ba da su ga Haruna firist da kuma’ya’yansa maza a matsayin rabonsu na kullum daga Isra’ilawa.’”
for svinge-brystet og løfte-låret har jeg tatt fra Israels barn av deres takke-slaktoffer og gitt til Aron, presten, og til hans sønner som en evig rettighet de kan kreve av Israels barn.
35 Wannan shi ne sashen hadayar da aka ba wa Haruna da’ya’yansa maza, hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta, tun ranar da aka gabatar da su don su yi wa Ubangiji hidima a matsayin firist.
Dette er Arons del og hans sønners del av Herrens ildoffer, som gis dem på den dag de føres frem for å tjene Herren som prester,
36 A ranar da aka keɓe su, Ubangiji ya umarta cewa Isra’ilawa su ba da wannan a gare su a matsayin rabonsu na kullum, a dukan tsararraki masu zuwa.
den del som Herren befalte skulde gis dem av Israels barn på den dag de salves, en evig rettighet, fra slekt til slekt.
37 Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, hadaya don zunubi, hadaya don laifi, hadaya ta naɗi da kuma hadaya ta salama,
Dette er loven om brennofferet, om matofferet og om syndofferet og om skyldofferet og om innvielsesofferet og om takkofferet,
38 waɗanda Ubangiji ya ba wa Musa a Dutsen Sinai, a Hamadar Sinai, a ranar da ya umarci Isra’ilawa su kawo hadayunsu ga Ubangiji.
den som Herren gav Moses på Sinai berg den dag han bød Israels barn å ofre Herren sine offer i Sinai ørken.