< Firistoci 7 >
1 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodi na hadaya don laifi, hadaya ce tsattsarka.
Voici aussi la loi de l’hostie pour le délit, elle est très sainte:
2 Za a yanka hadaya don laifi a inda ake yanka hadaya ta ƙonawa, za a kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagade.
C’est pourquoi là où sera immolé l’holocauste, sera aussi tuée la victime pour le délit; son sang sera répandu autour de l’autel.
3 Za a miƙa kitsen abin hadaya duka, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki,
On en offrira la queue et la graisse qui couvre les entrailles:
4 da ƙodoji biyu da kitsen da yake a bisansu kusa da kwiɓi, da kuma rufin hanta, wanda za a cire tare da ƙodoji.
Les deux reins, la graisse qui est près des flancs et la membrane réticulaire du foie avec les reins;
5 Firist zai ƙone su a kan bagade, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji. Hadaya ce don laifi.
Et le prêtre les brûlera sur l’autel: c’est l’holocauste du Seigneur pour le délit.
6 Kowane da namiji cikin iyalin firistoci zai iya ci. Sai a tsattsarkan wuri ne za a ci; gama abu mafi tsarki ne.
Tout mâle de la race sacerdotale mangera de ces chairs dans un lieu saint, parce que c’est une chose très sainte.
7 “‘Hadaya don laifi kamar hadaya don zunubi take, saboda haka ƙa’ida hanyar yinsu iri ɗaya ce. Su ɗin na firist da ya yi kafara da su ne.
Comme pour le péché est offerte l’hostie, de même aussi l’hostie pour le délit: une seule loi sera pour les deux hosties: c’est au prêtre qui les a offertes qu’elles appartiendront.
8 Firist da ya miƙa hadaya ta ƙonawa domin wani, zai iya ajiye fatar wa kansa.
Le prêtre qui offre la victime de l’holocauste, en aura la peau.
9 Kowace hadaya ta garin da aka toya a tanda, ko aka dafa a tukunya ko a kan kaskon tuya, na firist da ya miƙa ta ne,
Et toute offrande de fleur de farine qui se cuit dans le four ou qui s’apprête sur un gril ou dans la poêle, sera au prêtre par lequel elle est offerte:
10 kuma kowace hadaya ta gari wadda aka kwaɓa da mai, ko wadda ba a kwaɓa ba, ita ma, ta dukan’ya’ya Haruna ne maza.
Qu’elle soit arrosée d’huile ou qu’elle soit sèche, elle sera partagée entre tous les fils d’Aaron en une égale mesure.
11 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodin hadaya don zumuncin da mutum zai iya miƙa ga Ubangiji.
Voici la loi de l’hostie des sacrifices pacifiques qui est offerte au Seigneur.
12 “‘In ya miƙa hadayar a matsayin hadaya ta godiya ce, to, zai miƙa ta tare da burodi mai kauri marar yisti, wanda aka kwaɓa da mai, da burodi marar kauri, wanda aka shafa wa mai, da kuma burodi mai kauri da aka yi da gari mai laushi wanda aka kwaɓa sosai da mai.
Si c’est une oblation pour action de grâces, on offrira des pains sans levain, arrosés d’huile, des beignets azymes, oints d’huile, de la fleur de farine cuite, des galettes mêlées et arrosées d’huile;
13 Tare da hadayarsa don zumunci ta godiya, zai miƙa dunƙulen burodin da aka yi da yisti.
Et aussi des pains fermentés, avec l’hostie d’action de grâces, qui est immolée pour les sacrifices pacifiques.
14 Zai kuma kawo ɗaya daga kowace a matsayin hadaya, baiko ne ga Ubangiji. Wannan zai zama na firist da ya yafa jinin hadaya ta salama ne.
Un de ces pains sera offert pour prémices au Seigneur, et il sera au prêtre qui répandra le sang de l’hostie,
15 Za a ci wannan nama na hadaya don zumunci ta godiya a ranar da aka miƙa ta, kada yă bar wani abu daga naman yă kwana.
Dont la chair sera mangée le même jour, et il n’en restera rien jusqu’au matin.
16 “‘In hadayarsa cika wa’adin rantsuwa ce ko kuwa ta yardar rai ce, sai a ci hadayar a ranar da ya miƙa ta, amma za a iya cin duk abin da ya rage kashegari.
Si quelqu’un par vœu ou spontanément offre une hostie, elle sera également mangée le même jour, et si quelque chose en reste pour le lendemain, il sera permis d’en manger;
17 Duk naman hadayar da ya rage har kwana uku, dole a ƙone shi.
Mais tout ce que le troisième jour en trouvera, le feu le consumera.
18 Idan aka ci naman hadayarsa ta salama a rana ta uku, ba za a karɓi wanda ya ba da hadayar har ya sami albarkar hadayar ba, naman zai zama abin ƙyama, duk wanda ya ci kuwa ya yi laifi.
Si quelqu’un mange le troisième jour de la chair de la victime des sacrifices pacifiques, l’oblation deviendra nulle, et elle ne sera pas utile à celui qui l’aura offerte; bien plus, quiconque se sera souillé par un tel aliment, sera coupable de prévarication.
19 “‘Ba za a ci naman da ya taɓa wani abu marar tsarki ba; dole a ƙone shi. Game da sauran nama, kowa da yake mai tsarki zai iya ci.
La chair qui aura touché quelque chose d’impur, ne sera point mangée, mais elle sera brûlée au feu; celui qui sera pur mangera de la victime des sacrifices pacifiques.
20 Amma in wani wanda ba shi da tsarki ya ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
L’homme souillé qui mangera de la chair de l’hostie des sacrifices pacifiques, laquelle aura été offerte au Seigneur, périra du milieu de ses peuples.
21 Idan wani mutum ya taɓa abu marar tsarki, ko mutum ne, ko dabba ce, ko wani abu na banƙyama, ya kuma ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.’”
Et celui qui aura touché quelque chose d’impur d’un homme, ou d’une bête, ou bien de toute chose qui peut souiller, et qui mangera de la chair de cette sorte, périra du milieu de ses peuples.
22 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
23 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Kada ku ci wani kitsen shanu, ko na tumaki, ko kuwa na awaki.
Dis aux enfants d’Israël: Vous ne mangerez point de la graisse de brebis, de bœuf et de chèvre.
24 Za a iya yin wani amfani da kitsen dabbar da ta mutu mushe, ko kitsen dabbar da namun jeji su yayyaga, amma kada a kuskura a ci.
Quant à la graisse d’un animal crevé, et de celui qui a été pris par une bête sauvage, vous l’emploierez à divers usages.
25 Duk wanda ya ci kitsen dabbar da aka miƙa ta wuta ga Ubangiji, za a fid da shi daga mutanensa.
Si quelqu’un mange de la graisse qui doit être consumée par le feu comme une oblation au Seigneur, il périra du milieu de son peuple.
26 Kuma duk inda kuke zama, ba za ku ci jinin wani tsuntsu ko na dabba ba.
Vous ne prendrez pas non plus pour nourriture du sang d’aucun animal, tant des oiseaux que des troupeaux.
27 Duk wanda ya ci jini, za a fid da mutumin daga mutanensa.’”
Tout homme qui aura mangé du sang, périra du milieu de ses peuples.
28 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
29 “Faɗa wa Isra’ilawa, ‘Duk wanda ya kawo hadaya ta salama ga Ubangiji, sai ya kawo hadayarsa ga Ubangiji daga cikin hadayu na salama.
Parle aux enfants d’Israël, disant: Que celui qui offre la victime des sacrifices pacifiques au Seigneur, lui offre aussi en même temps son sacrifice, c’est-à-dire, ses libations.
30 Da hannuwansa zai kawo hadayar da za a ƙona ga Ubangiji; zai kawo kitsen tare da ƙirjin, yă kuma kaɗa ƙirjin a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
Il tiendra dans ses mains la graisse de l’hostie et la poitrine; et lorsqu’en les offrant l’une et l’autre au Seigneur, il les aura consacrées, il les remettra au prêtre,
31 Firist zai ƙone kitsen a bisa bagade, amma ƙirjin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza.
Qui brûlera la graisse sur l’autel; mais la poitrine sera pour Aaron et pour ses fils.
32 Za ku ba da cinya ta dama ta hadaya don zumuncinku ga firist a matsayin baiko.
L’épaule droite des hosties des sacrifices pacifiques deviendra les prémices du prêtre.
33 Ɗan Haruna da ya miƙa jini da kitsen hadaya ta salama, zai ɗauki cinyar tă zama rabonsa.
Celui des fils d’Aaron qui aura offert le sang et la graisse, celui-là même aura aussi l’épaule droite pour sa portion.
34 Daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa, na ɗauki ƙirjin da aka kaɗa da kuma cinyar da aka miƙa, na ba da su ga Haruna firist da kuma’ya’yansa maza a matsayin rabonsu na kullum daga Isra’ilawa.’”
Car la poitrine de l’élévation et l’épaule de la séparation, je les ai prises aux enfants d’Israël sur leurs hosties pacifiques, et je les ai données à Aaron, le prêtre, et à ses fils, par une loi perpétuelle pour tout le peuple d’Israël.
35 Wannan shi ne sashen hadayar da aka ba wa Haruna da’ya’yansa maza, hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta, tun ranar da aka gabatar da su don su yi wa Ubangiji hidima a matsayin firist.
C’est là l’onction d’Aaron et de ses fils dans les cérémonies du Seigneur, au jour que Moïse les présenta pour exercer les fonctions du sacerdoce;
36 A ranar da aka keɓe su, Ubangiji ya umarta cewa Isra’ilawa su ba da wannan a gare su a matsayin rabonsu na kullum, a dukan tsararraki masu zuwa.
Et c’est ce que le Seigneur a commandé de donner aux enfants d’Israël, comme culte perpétuel dans leurs générations.
37 Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, hadaya don zunubi, hadaya don laifi, hadaya ta naɗi da kuma hadaya ta salama,
Telle est la loi de l’holocauste et du sacrifice pour le péché et pour le délit, et pour la consécration et les victimes des sacrifices pacifiques;
38 waɗanda Ubangiji ya ba wa Musa a Dutsen Sinai, a Hamadar Sinai, a ranar da ya umarci Isra’ilawa su kawo hadayunsu ga Ubangiji.
Loi que le Seigneur donna à Moïse sur la montagne de Sinaï, quand il commanda aux enfants d’Israël d’offrir leurs oblations au Seigneur dans le désert de Sinaï,